Yarima har ƙarfe ɗaya na dare,wai dole sai na tayashi hira,a irin zaman da muke yi ne a falo talabijin na ta aikin yin hidimominta, wanda hasken da ke fitowa ta jikinta shi ne kawai hasken falon saman da muke zaune.
Cikin mintuna biyar hankalinmu ya koma ga wani fim da suke yi wanda yaro da yarinyar fim ɗin suke zaune suna hirarsu, kamar dai mu sai naga yaron ya miƙe ya iso inda take zaune ya tsugunna daga nan ya yi mata wata magana wacce ta ƙunshi aure.
"Za ki aure ni, Please." Sai na ga yarinyar ta ɗaga kanta tare da riƙe hannunsa ta tashi tsaye da sauri. Abin ka ga marasa kunya sai suka kama tsotsan bakin juna, ta wutsiyar ido na ga Yarima ya ƙura mini ido.
Ɗan minti ɗayan nan da na yi ina kallon Yarima ta wutsiyar ido, sai kawai na ji takun kiɗan talabijin ɗin ya canja kallon farko ban ƙara maimaitawa ba, na miƙe jikina na rawa ko sallama babu na sauko da saurina, sai gidana. Ina isa gadona na faɗa sai kuka. Anwar na dinga kira da ƙarfi, saboda shi ne mutumin da yake ƙwance a zuciyata.
Ko da wasa ban yi zaton Yarima zai biyo bayana ba, asali ma ban ji ya shigo ɗakina ba, sai dai jin an zauna gefen gadona na ji anyi, na ɗago da sauri,dama fitilar gefen gadona ƙwaya ɗaya ita ke kunne,ido muka haɗa da shi.
"Wa ye Anwar Yasmin? Ina ƙoƙarin in ga na mallaki zuciyarki da gangar jikinki gaba ki ɗaya, ashe duk ban sani ba da wanda zuciyarki ke ƙauna, na yi da na sani a yanzun da nine na fara sakar miki jikina, saboda samun ƙwanciyar hankalin junanmu."
Ya miƙe tsaye yasa hannuwansa a aljihun wandonshi, wanda dama T.shirt ce a jikinsa, tsayuwar da ya yi zata kai ta mintuna taƙwas, sannan ya juya ya tafi. Tabbas ban ji daɗi ba, ban kuma so a ce yajini ina ambaton sunan masoyina ba.
_To masu karatu sai mun hadu a littafi na biyu, wanda tare suka fito._
_Taku har kullum: Maryam Kabir Mashi_
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng