x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 10 - KASAITA 2

  • 27001 words
  • 28261 words
  • Out of 28261 words

Category: Love Stories

Views 83

02 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
mini ba,na ko lafiya ko kuwa ya yi bacci? Hakan ya sa na juya nima na cigaba da addu'o'in ƙwanciya baccina, na yi ƙwanciyata, jin ya ce, "Alhamdulillah." A bayyane yasa na ce ashe idonsa biyu. Madadin na ji ya yi magana sai kawai na ji ya ɗan cizar mini bayana na ɗan firgita kaɗan saboda a bazatan da cizon ya zo min tare da faɗar.

"Kai Yarima!"

Kafin in ƙarasa ya kuma cije leɓatun kunnena, daidai wajensa ɗan kunne, kafin na yi magana ya kurɗa ya ciji wuyana, kumatuna, na yi saurin juyowa na fuskance shi, sai kawai na ji ya cije laɓɓana.

"Kai...." Yasa tafin hannu ya rufe bakina.

"Don't talk." Numfashina na ji ya yi sama wanda ya ɗauki mintuna uku kenan bai dawo mini ba, ba wani abu ya janyo mini haka ba shi ne salon yanda Yarima ke tsotsar ƴan yatsun hannayena.

Shin Yarima ne kuwa? Tambayar da zuciyata ta yi mini kenan,a daidai lokacin da numfashina ya dawo dai-dai kunya ta kama ni da na ji ya amsa mini da "Yasmin ni ne."

A nan take na tabbatar wa kaina maganar da ke cikin zuciyata ce ta fito fili. Idanuwana kuwa na ƙara runtsewa,runtsewar da ta kai ni har wayewar gari ban ƙara buɗa su ba.

Ji na cikin ruwan ɗumi yasa na san mafarki nake,a cikin mafarkin na dinga cewa, "Yarima mafarki nake na shiga ruwa."

A kunnena na ji ya ce "Buɗe idanuwanki ba mafarki ba ne ba."

Na firgita sai na ji ni rungume a ƙirjin Yariman a cikin ruwa, na waiga na kalle shi ƙwance cikin ruwan kumfa sai ƙamshi kawai ke tashi, na juyo na kalli kaina nima cikin ruwan kumfa.

Na sa hannu na dinga laluba jikina, na ji zargin da nake ya tabbata na rashin kayan jikina, na juyo na ƙara kallonsa sosai sai na ga ya lumshe mini ido na juya a sanyaye na ƙwantar da kaina jikin gefen bahon wankan, sai na ji hawaye, saboda tunanin gane ni ba kaya.

"Why! Why!! Why!!! Yarima? Me yasa ba ka tashe ni ba? Me yasa ka kalle mini jiki?"

Ya ƙwanta bayana, "Yasmin,don kina matata kin manta mun amince da junanmu."

Ya sumbaci bayan wuyana, "kada ki yi da na sani ko ki ji haushin abin da na yi,me yasa ba ki da yarda Yasmin? Nifa na amince da ke ce matata, ke me yasa ki ke kokwanto ne har yanzu?"

Ya yi saurin dawowa gabana jin ina fitar da ƴar jaririyar kukan ƙissa, wanda Aunty ta ce mini ana yi, ya dago kumatuna ya tallabe da hannuwansa masu kumfa.

"Ba ki son abin da na yi miki? Na ɗaga kaina.

"To shi kenan ki yi haƙuri tsaya na baki haƙuri sosai."

Sai na ga ya ɗebo kumfa yasa a saman kansa ya ɗiga a goshi, hanci a kunnuwa, sannan ya riƙe kunnuwa ya gwale idanuwa,dama abu (Tubarakallah) inji Malam bahaushe. Sannan ya ce, "Sorry." Dole ne ma na yi dariya, na yi murmushi kuwa sai ya yi saurin rungume ni.

Ya ɗago kaina ya goge hawayen fuskata. "Kin yi haƙuri?" Na ɗaga kaina.

"Ban yarda ba, sai kin ce eheee."

Yanda ya tale baki ya ce eh, dole ta sa ka dariya, na sa dariya na daki ƙirjinsa da dukkan hannayena, ya girgiza kansa alamar jin daɗi sai ya rungume ni tare da faɗar "I love You too." Nima na amsa masa da "I love You too much." Amma a zuciyata,na koma na ƙara lafewa a ƙirjinsa.

**** **** ****

Satinmu huɗu a Greece,amma wurare ɗai-ɗai ne ban sani ba, balle ma da muka shirya sosai da shi. Ƙasar London,Rum(Italy) da kuma Turkey,duk su ma satinmu bibbiyu, wanda idan na haɗa su waje ɗaya mun ƙwashe watanmu biyu da sati biyu.

Yau kuwa ranar Asabar ce, wacce ta yi daidai da ita ce ranar da muka iso Nijeriya, sai da ma Yarima ya tashe ni daga bacci ya sanar da ni an zo Nijeriya, wanda tun da muka shiga jirgi ya janyo ni ya ƙwantar a ƙirjinsa, ɗan wasannin shafa mini baya ya kama yi, wannan ne ma yasa har bacci ya ɗauke ni ba tare da na sani ba.

Maƙale nake a kafaɗar Yarima har muka iso bakin ƙofar fitowa daga jirgi cikin ɗan ƙaramin lokaci na yi saurin janye jikina daga gare shi, saboda hango mutanenmu da na yi sun zo taryarmu. Dogarawa kenan. Ya janyo ni jikinsa.

"Me ye haka,mun iso Nijeriya za ki fara gasa ni, wallahi sai mu koma."

"Kalli gabanka." Na faɗa a lokacin da muke sauka matattakalar benen jirgin.

Waziri ne da sauran manyan fada a tsaye suna jiran saukowarmu, ban da dogarawa waɗanda sun kai ashirin, motoci kuwa sun cika filin jirgin Jos International Airport,da gani ka san na taryar mu ne. Cikin sakan ɗaya na ga Yarima har ya rikiɗe ya koma Yarima na da dana sani, da na juyo na kalleshi ta wutsiyar idanuwana ni kaina sai na ji tsoronsa ya sauko min.

Alhamdulillah!

Mu haɗu a littafi na uku. Daga Mai ƙaunarku.

Aunty Maryam Kabir Mashi.
















An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels
End Ads