x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 3 - NAMIJIN GASKE Book 1

  • 6001 words
  • 8376 words
  • Out of 8376 words

Category: Adventure Stories

Views 56

02 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
tsaya atsaye toh sai a wannan lokaci ne sarki hinzur yafara ganin jiri a sakamakon jininsa dake zuba,
Nan suka afka ma junansu, wannan karon salon fadan ya canja don cikin dakiku kadan suka hada ma junansu jini da majina,
,
Sarki hinzur ya gaji likis amma saboda tsabar juriya da naci hade da cin rai
Tabbas badun sarki hinzur ya kasance NAMIJIN GASKE ba toh da tuni waziri humaiz ya gama da shi.
Koda suka ga tsagwaron karfin su yazo daya sai kowa yaja baya ya tsaya, nan sukai cirko cirko suna kallon juna,
Cikin matukar fushi sarki hinzur yace"shin yakai dan uwana kayi sani daka zo ka sanar dani cewa kana son mulkina toh tuni na baka, amma tun da ka biyo ta wannan hanyar ne lallai ina tabbatar maka sai na hallaka ka ayau dinnan"
.
Koda waziri humaiz yaji haka sai ya bushe da mahaukaciyar dariya sai da yayi mai isarsa sannan ya dubi sarki hinzur yace mai
"Ni ba dan'uwanka bane kada ka sake ka sake kirana da dan'uwanka'kayi sani tun muna kanana mahaifinmu yake nuna matukar kauna agareka,
Kulawar dayake baka sam ni baya bani, sannan maimakon ni danake Babba na gaji karagar mulkinsa amma sai ya nadaka a matsayin sarki alhalin kaine a kasa dani, tun daga wannan lokaci na fara kulla tarko ina ta kaima ka hare hare amma kana ketarewa, toh yau gashi ka fada a cikin babban tarkona wadda ina tabbatarma ayau dinnan zan halaka, ka sannan inbi matarka ita ma na hallakata"
Koda gama fadin hakan sai sarki hinzur ya kauma waziri humaiz wata naushi adaidai makogaro da nufin ya fasa mai makogoro cikin zafin nama humaiz ya goce sannan ya fidda wata yar karamar wuka a kugunsa cikin shammace ya soka ma sarki hinzur wukan a cikinsa, nan take sarki hinzur ya kwala kara wacce ta amsa a gaba daya ilahirin dajin
Nan take sarki hinzur ya fadi matacce
.
Koda waziri humaiz yaga ya samu nasarar kashe sarki hinzur sai ya nausa cikin daji nemana, nikuma alokacin ina saman wata bishiya na rakube sai kuka nake tayi
.
Yadda agaban idanuwana aka kashe mani masoyi,
.
Bayan tafiyarshine na sauko daga kan wannan bishiyar sannan na nausa daji
.
Alokacin ina dauke da cikin ka wata takwas haka na kariso wannan waje a matukar galabaice.
Na hada sanduna,itacuna na sana'anta wannan dan karamin bukkar haka na cigaba da rayuwa acikin wannan jejin har sa'ar dana haifeka
.
Babu abinda nake ci face yayan itatuwa ,da kuma tsuntsaye sune abincina a haka na raineka ka girma."
.
Koda hamasiya tazo nan a labarinta sai taa dubi muhaisin tace mai"toh dana kaji labarin mahaifinka sarki hinzur bin humas na birnin tehran wanda ayanzu ya zama tarihi"
Koda hamasiya ta kawo nan azancenta sai taga fuskar muhaisin ta jike sharkaf da hawaye nan ya mike tsaye sannan ya rungume mahaifiyarsa yana mai fashewa da matsanancin kuka na bakin ciki.
.

Marubuci:- Shuraih Usman
Hakkin mallaka (m) Shuraih Usman
Company:- Shuraih 99%
(c) shuraih Usman 2017
Typing:- shuraih 99%
Namijin gaske 1
Part 1F
(c) Shuraih Usman
@shuraih 99%
NAMIJIN GASKE
Littafina daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Tel. 08133209890
Part F
.
Doka, banyarda wani yayi copy ko ya sarrafa
wannan labari ta
ko wace hanya batare da izni na ba. Dafatan
za'a kiyaye
Copyright
Shuraih Usman
.
Acan birnin tehran kuwa tun lokacin da sarki hinzur ya mutu, sai aka rada waziri humaiz, a matsayin sarki.
.
Nan fa waziri humaiz ya dawo izuwa sarki humaiz,
Nan ya fiddo da asalin siffarsa ta mulkin zalunci,
Mutanen birnin tehran sun koka sosai akan wannan mulki nasa,
Ya kara yawan haraji, bisa na da, kuma bai dauke wa kowa ba, yaro,jinjiri,babba,tsoho, dole su biya,
Laifi kadan talaka zaiyi yanzu zaisa ayanke masa hukuncin kisa
Su ko attajirai na matukar jin dadin mulkin nasa ,
Rabon da a shimfida irin wannan mulkin zaluncin tun zamanin wani gawurtacce kuma sadaukin Azzalumin sarki mai suna Lu'umanu
(A duba kundin tsatsuba)
.
Wata rana sarki humaiz na barci sai yayi mafarkin wai ga sarki hinzur ya dawo izuwa birnin tehran
Yana zuwa ya nufi gidan sarauta
Da zuwansa gidan ya shiga dakaru suka taso masa amma koda sukayi arba da tsohon sarkinsu
Sai suka zubda makamansu,
Nan sarki hinzur ya dakumo wuyan sarki Humaiz,
Bayan ya hada masa jini da majina ya luguigita shi,
Sai ya sanya masa igiya a kafa sannan ya daure igiyar a jikin doki, nan ya hau kan dokin sannan ya zabureshi,
Wannan dokin yai ta tsala gudu, bai tsaya ako inaba sai da ya kariso tsakiyan gari,
Koda mutane sukai arba da sarki hinzur sai suka kamu da matukar farinciki ,
Nan take sarki hinzur ya dubi jama'an garin yace da su"Ya ku al'umman birnin tehran shin kuna son wannan sarki naku kuna jin dadin mulkinsa ,koko a'a na kashe shi"
.
Gaba daya jama'an garin sai cewa suke akashe shi, la'ananne,azzalumi,akashe shi kawai
Nan take sarki hinzur ya sauko daga kan dokin daya ke kai sannan ya amshi takobi a hannun wani badakare, ya daga sama da nufin ya fille ma sarki humaiz kai.
Humaiz na bada hakuri amma ina
Nan take sarki hinzur ya sauke mai takobin....
.
A daidai wannan lokaci ne sarki humaiz ya farka a firgice, wata kyakkyawar mace dake kwance agefensa ta mike , cikin kissa tace
"Ya masoyina shin meke damunka ,da har ka farka haka a firgice"
.
Murmushi yayi yace"Wani mugun mafarki nayi "
Yana gama fadin hakan sai ya sauko bisa kan luntsumemiyar katifan da suke kwance akai,
.
Cikin kankanin lokaci ya sanya kayansa, sannan yayi tafi da hannu,
Gama tafinsa keda wuya sai ga wasu dakaru su biyu sun shigo cikin turakar, dakarun suka russuna a gabansa nan ya umarcesu dasu tafi su kira masa boka kamsusulajani,
Nan suka fice.
.
Cikin kankanin lokaci sai ga boka kamsusulajani ya bayyana acikin turakar ,
Yace "ya shugabana shin me nene dalilin daya sanya kace ayi kirana,"
Sarki humaiz yace" yakai boka kamsusulajani kayi sani yau nayi mugun mafarki wanda ya tsorata ni ainun,dalilin kiranka kuwa so nake ka fassara mani wannan mafarki tawa,
.
Take ya kwashe labarin abinda yagani acikin mafarkinsa ya sanar da shi,
Koda boka kamsusulajani yaji haka sai yace ya shugabana, ina bukatan lokaci don nayi bincike bisa halwar tsafina "
Sarki humaiz yace" na baka daga yau zuwa gobe da safe lallai ina son jin fassarar wannan mafarki,"
Koda gama fadin haka sai boka kamsusulajani ya bace bat.
Washe gari a fada ana fadanci ayayin da kowa ya lura da hankalin sarki humaiz ya dugunzuma ainun,sabanin da dazakaga sai annashwa yake yana keta dariya .
Kwatsam sai gani akayi boka kamsusulajani ya bayyana tsulum acikin fadan,
Wasu fadawa har sun tattara rigunansu da niyyar su ruga amma koda suka ga boka kamsusulajani ne sai hankalinsu ya kwanta
.
Nan ya kwashi gaisuwa a wajen sarki
Srki humaiz ya sallami kowa a fadan fada ta rage su su biyu,
Sarki humaiz yace "gareka boka kamsusulajani shin me ka ganpo abinciken dakayi,"
Nan take boka kamsusulajani yafara bayani kamar haka" hakika mafarkinka sai ya tabbata..."
Sarki humaiz ya daka masa tsawa yace"ashe kai wani sakarai ne ban sani ba tayaya mutumin dana kasheshi da hannuna zai dawo ya kasheni, ko ka taba ganin anmutu an dawo ne"
Boka yai murmushi yace "eh ba'ataba mutuwa an dawo ba , amma kasani alokacin daka kashe sarki hinzur ai baka kashe matarsa hamasiya ba,babban kuskuren daka aikata kenan,
Kayisani koda hamasiya ta tsira daga hannunku, tana dauke da ciki wata takwas, kuma ta haife wannan da nata yanzu haka ya girma ya zama gawurtaccen jarumi, kuma gagarabadau, lallai ina sanar da kai cewa yana nan zuwa birnin ka nan da yan wasu lokuta kuma ya kasheka sannan ya amshe mulkin mulkin mahaifinsa .
Koda sarki humaiz yaji haka sai hankalinsa ya dugunzuma ainun ,nan ya dubi boka kamsusulajani yace dashi"toh shin yanzu ina mafita,
.
Boka kamsusuljani yace" mafita dayace "
Cikin kaguwa sarki humaiz yace "yakai dirkan birnin tehran gaggauta sanar dani mafitar da ka samo mana"
.
Boka yace "bakomai bane wannan mafita face ka mallaki Wata KAMBUN TSAFI wacce aka killace ta a tsibirin bahar jallus"
.
Boka kamsusulajani ya dubi sarki Humaiz bin Humas yafara bashi labari kamar haka
.
Kimanin Shekaru aru aru da suka shude A Cikin wannan birnin Na Tehran anyi wani gawurtaccen Azzalumin sarki mai suna LU'UMANU na birnin Tehran a duba KUNDIN TSATSUBA
.
Shi wannan sarki mai suna Lu'umanu yana da wata kambu na tsafi wacce take daure a hannun hagunsa,
Da wannan kambune yayi amfani inda yai ta shimfida mulkin zalunci ,
Har lokacin da wani ma'abocin bakon Addini ya hallakashi
.
Yanzu kambun tsafin na ajiye a tsakiyar tsibirin bahar jallus,
Muddin ka mallaki wannan kambu toh duk duniya babu wani jarumin da bazaka taka ba,
Sai ka zama guguwar Annoba mai shafe birane,
Akwai wasu Manya manyan sarakunan aljanu na duniya baki daya guda goma sha bakwai da ke ma wannan kambu bauta,
Muddin ka mallaki wannan kambun toh duk zasu da wo karkashin ikonka,
.
Ita wannan kambu tana tattare da alkaluman sihirin tsafi guda dubu
Kasani muddin ka mallaki wannan kambu toh tamkar ka mallaki wayan can sihirin tsafin ne,
,
A baya jarumai, sadaukai, da Mazan kwarai, duk sun rasa rayukansu bisa mallakar wannan kambu ta tsafi,
.
Kayisani yakai wannan sarki
Kafin ka isa tsibirin bahar jallus kuwa sai ka bita cikin wasu mugayen dazuka guda biyu,
.
Dajin farko ana kiransa da suna Burkum
Babu komai acikin wannan daji face dandazon yan fashi wayanda adadinsu yafi milyan
Su wayannan yanfashi sun kasance mugayene sam basu da imani ko kadan don ko bera sukai arba da ita toh take suke gutsutstsure namanta su rabata ga junansu yadda kowa sai ya samu
.
Komai suka samu raba daidai suke da ita yadda kowa zai samu duk kankantashi kuwa,
.
Atarihin wannan daji babu wani mahaluki walau mutum ko aljan wanda ya taba ratsawa ta cikin wannan daji a raye,
Kai muddin mutum ya shiga wannan daji toh tamkar ya shiga lahira ne don kuwa baza a sake jin duriyarsa ba
.
,
Daji na gaba kuwa ana kiransa Da suna Darul marid babu komai acikin wannan daji face wasu irin zabga zabgan maridai wayanda adadinsu yakai dubu
.
Su wayannan maridai kaifi ko tsini baya tasiri ajikinsu face zagwaron karfin damtse, don sun kasance suna masu baiwa jikinsu horo ta hanyar shan wani tsumi wanda muddin suka sha toh ko kwana zakayi kana saransu ,
Ba za su san kanayi ba
.
A tarihin duniya baki daya
ba'ataba samun wanda ya ratsa ta cikin wayannan dazuka guda biyu sannan ya fito a raye ba walau mutum ko aljan,
.
Shi kuwa tsibirin bahar jallus, duk yafisu masifa da bala'I
Don kuwa wasu irin Aljanu ne a wajen
Su wayannan aljanun suna da katon kai kaman randa sannan sai sililin kafafuwa wanda ke barazanar karyewa a ko wani lokaci,
,
Aljanun gaba daya jikkunansu launin ja ne,
Da sun hadu da mutum ko aljan nan take zasu zuke jinin jikinsa, ta hanyar taba sassan jikinsa
.
Su wayannan aljanu suke tsaron wannan Kambu ta tsafi
.
Lallai tafiya neman wannan kambun tsafi bakaramin masifa da bala'I bane
Don kuwa NAMIJIN GASKE ne kadai zai iya tunkarar wayannan masifu batare da yaji tsoro ko shakka acikin zuciyarsa ba
."
Koda boka kamsusuljani yazo nan azancensa sai yaga sarki humaiz ya bushe da dariya al'amarin daya bashi mamaki kenan
Sarki humaiz ya dubi boka kamsusuljani cikin yarda da kai yace
"Lallai ko zan rasa rayuwata sai na mallaki wannan kambun tsafin kuma ina sanar dakai cewa ka shirya don kuwa da kai za'ayi wannan tafiyan
.
SHIN SARKI HUMAIZ ZAI SAMU NASARAR MALLAKAR KAMBUN TSAFI KUWA
.
WANI IRIN MASIFU DA BALA'IEU ZAI HADA DASU
.
SHIN BOKA KAMSUSULLAJANI ZAI AMINTA YAYI WANNAN TAFIYA MAI MUGUN HADARIN KUWA
.
INA LABARIN JARUMI MUHAISIN DA MAHAiFIYARSA
.
SHIN ZAI SHIRYA YAZO BIRNIN TEHRAN DAUKAN FANSA
.
WANI KARAN BATTA ZA'AI TSAKANINSA DA SARKI, HUMAIZ,
.
Domin jin wayannan amsoshin sai ku tsumaye ni a littafi na biyu
.
NAMIJIN GASKE
Littafina daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Tel. 08133209890
.
Doka, banyarda wani yayi copy ko ya sarrafa
wannan labari ta
ko wace hanya batare da izni na ba. Dafatan
za'a kiyaye
Copyright
Shuraih Usman
.
SHEKARAR RUBUTAWA:- 2017
Addreshi:- tshon/kasuwa gidan malam Usman ,nasarawa state Keffi
.
Akwatin waya:- 0908626148,08133209890
.
Kagaggen labari daga shuraih Usman
SADAUKARWANE GA
M.malam Usman
M.hajiya Maryam
Mujahid hamza(mijin biza) best friend forever
Sis.Zainab Usman
Bro.abdulaziz Usman
Sis.Amina Usman
BAN MANTA DA KUBA
Dahiru Usman Diffusion(D.U.D)
Anas aliyu katuka (bin malik)
Suleiman ishaq(Big army)
Abdullahi Isa (B.O.C)
Dafatan kuna cikin koshin lafiya
Alhamdulillah


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels
End Ads