x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 6 - MY LADY BOSS

  • 15001 words
  • 18000 words
  • Out of 20773 words

Category: Romance Story +18

Views 89

01 Sep 2025
Start ads
After Image Ads
Nurse Yusrah tana jan tsaki , tana cigaba da aikin ta don ganin ta tsaida jinin. Hannu Bilkisu takai tana amsan Almaka shin tana caka shi a raunin goshin ta da shima yake jini....wani irin rintse ido duka sukayi ,kamin tace" rana ta farko dana nema abu ya kuɓce mun , ina xan same wa'annan yaran? Dole na gansu naji su waye su? Taya suka samu kuɗin nan..... Cewan Bilkisu tana caccakar kanta da almakashin , jini ke da zuba cewan Yusrah cikin tsoro da tausayawa don ta fahimci a maye Bilkisu ke maganan.


Wai me kkce waye iyaye na? To babu ! Amma ke zaki iya zama iyaye na inkin damu da gani na a haka , shegun likita baku iya komai ba sai saka fararen kaya na banza da wulaƙamci , duk wacce bata zo inda nake ba sai......keeee waye sunan ki?


Yusrah tayi maganan cikin fusata . Cikin Muryar ta da ya fashe tace " Bilkisuuuuuu .


Yusrah ne ta amshe da cewa" jubiki fah Kaman ba mace ba ,waye zai taho inda kike a haka? Waye mahaukaci? Dole suyi baya , kince baki da iyaye , Ni na zama iyayenki , to naji duk da kasancewar kin girmemun indai zaki daina abun da kikeyi na wannan shan barasar a matsayin ki na mace , to ki zo gidan mu ki zauna dani , idan kuma kina da iyaye ina roƙon ki ki koma gare su......Sauran numfashin Bilkisu yasa Yusrah fahimtar bacci ne ya ɗauke ta saka makon allurar da sukayi mata.


Sauran likitocin ne aka hau kallon kallo ,na shin da gaske Yusrah zata ɗauki wannan bugaggiyar takai gidan su ,ita da ke cida kanta ?".

Ku ɗauko gado a sata , ku Kaita room 24 . Suka tsinkayi Muryar Yusrah ya katse su ,wanda cikin sauri suka fara cika umarnin ta....


****


Kallon mai hayan Safna tayi kamin tace " Ka taimaka mana dai ashekara dubu ɗari....mlm sabo ne yace " A'a indai yayi maku ɗari da hamsin to , saboda gidan nan fa duka ku zaku zauna ciki ku kaɗai ai hakan yayi ashekara.


Himm to bdmwa Laurat ku shiga mana da kayan ku mu fara gyarar gidan , ga kuɗin mlm sabo mun gode cewan Sumayya tana bashi kuɗin a dunƙule...washe baki sabo yayi yana godiya ".


Safna ki zauna keda Umma mu bari da Laurat mu shiga kasuwan gari n nan mu haɗo mana kayan abinci ,kana na dawo mu nemi gidan aiki , don Ni dai aikatau zanyi ban san kan garin ba tukunna .mlm sabo zanyi ma magana ya nema mun gidan aiki sai mun dawo.


A dawo lafiya Safna tayi masu tana shigewa ɗaki da Umma".


****


Gidan malam Ilu babu masaka tsinke saboda jama'a cike harda masu lapo dasuka zo zasu sai da gidan tare da tafiya da Sumayya....Ganin ɗaki babu kowa har kayan su wannan yasa su fahimtar Sumayya ta gudu....Ɗakin Lauratu a ka duba ganin ƙofa a buɗe ko ta ɓoye cike ne , nan da shiga aka ga ɗan Asabe tsirara ƙwance a sume haihuwar uwa n shi...Salati su Rita da Mmn mujahida suka sa suna fitowa da gudu maza na shiga ɗakin don ganin halin da Ɗan Asabe ke ciki rai a hannun Allah warwassss.....

Mama Atine ce ta shigo zaf zaf itace uwar lapo tana cewa " gafa kuɗi tun jiya Sumayya ta aikomun da dubu ɗari da hamsin sharrrr....ɗari da Hamsin???? Matan gidan suka haɗa baki cike da mmki ,kamin suce to ina Sumayya na ?.



To ai wannan ban sani ba ,ku za'a tambaya Sumayya nidai nawa kuɗi kuma ta kawo mun tayi maganan tana masu lapo kuɗin su....suna amsa suka juya.



Ɗan Asabe aka ɗauko tarai-tarai kaman gawa ana fita dashi , mlm Ilu na watsa do muchiyan da aka buga masa tsakar gidan , dariya wasu suka gimtse ,wasu kuma na jajanta masa.


*****


Kwana huɗu a Zaria kuɗin Sumayya ya ƙare a cefane kuɗin moto dana kama haya...wannan yasa safiyar talata ta miƙe tana sa hijabi don fitowa neman aikin gida shara girki ko wanke wanke . Mlm sabo ne yayi mata rakiya zuwa wani gida kana yace kunga gidan idan zaki shiga a akwai wani inji da sai ya lacceki tassssss sAbosa tsaban dukiyar da Allah ya basu. Mai gidan yayi gomna yanxu haka ministar ne ,ki shiga da addu'a Allah yasa ki samu , to suna da yara? Ta tambaye shi kai tsaye... Eh kaman ɗan su ɗaya a duniya shima baya ƙasan nake tunani.


To Mlm sabo na gode. Sumayya tayi maganan tana nufar tamfatsetsen gidan kaman hotel saboda girma da tsaruwa ....Sai da masu tsaron gidan suka gama mata tambaya da lacce sannan suka nuna mata hanyar sasan matan gidan... A farfajiyar gidan ne tana can tana tafiya tana mmkin wannan wani irin daula ce da dukiya aka zuba a gidan nan kawai taji tayi kiciɓus da mutum , waya na faɗi ƙasa nan take ya tarwatse.....



Oh God! Matsalar ƴaƴan talakawa kenan duk idan suka zo wuri a Sara ce , taji wata murya cike da masifa ta ɗirar mata. Saurin kai hannun ta ƙasa Sumayya tayi tana cewa " Kiyi hƙr ta ɗago ta na miƙa mawa BINAFA wayar ta, wanda hankaɗe Sumayya tayi tana nufan moton ta tana shigewa , don kun san ta dawo Gidan Hjy Juwairiyya da zama.....

topa! ƙaƙaƙaƙaƙa.......koya abun zata kasance ,shin mahaifiyar Sir Khamal zata ɗauki Sumayya ko ko? Ya kuma zata kasance tsakanin Sumayya da Khamal?



_Free page na dab da ƙarewa ki hanxarta wajen biyan kuɗin littafin LADY BOSS...._ _Littafin na kuɗi ne normal group ₦300 vip group ₦500 spc ₦1000 zaki iya turo da katin MTN ta wannan number 08081202932 ko ki tura ta wannan account details...6037312299 Mohammed A'isha keystone bank Idan Vtu trnsfer ne kiyi ta wannan number 09061466409 zaku na iya fara payment ɗin cox free page ba da yawa xanyi ba..._

'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call *08066268951*




_Aunty Aisha Mmn teddy🧸_
[9/16, 7:45 AM] Aunty Aisha Mmn Teddy🧸: *🕊️MY LADY BOSS🕊️*
_(Romantic and comedian)_



Free page
.......9


Marubuciyar:
(1)Bafullatnn ruga
(2)Ƴar aikina
(3)Walijaam
(4)Ƴar waye
(5)Gidan kwarata
(6)Gidan zaurawa
(7)Ƙwaryar sama
(8)Bintoto
(9)Ƴar maula
(10)Habibi da'iman
(11)Dijama ƴar fulani
(12)kawaliya
(13)Ƙwartn manya
(14)Zuma da maɗaci
(15)Taɓarah
(16) Siyasata
(17)My Lady Boss

*****
_Idan kin San kan ki baxai ɗau abun dake ciki ba,bazaki iya jura ba ,don Allah kar ki karanta ki dawo mun da zancen kutumelesi...ban san wani kitimurmura labarin Romantic ne👌haka kema idan kin san zaki saya ne don ki fitar mun na yafe ki adana kuɗin ki, kar ki fitar mun adawo mun da zancen gntlw.....masoya na billions naji saƙon nin ku gareni ina gdy Allah yabar🫶_

_*Free page zai ƙare a page 10...ku hanxarta wajen biyan kuɗin littafin LADY BOSS domun jin daɗin ku na cigaba da karanta wannan labari , kin shirya biya?? Na shirya! To yanda tsarin biyan ya kasance... Regular payment ₦300 vip payment₦500 special payment ₦1000...zaku iya turo da kuɗin ku ta wannan asusun bankin 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank...ko kuma ki tura katin MTN naki ta wannan number 08081202932...Idan Vtu trnsfer ne ki tura ta wannan MTN number 09061466409 sai ki tura da shaidar biyan ku duka ta wannan WhatsApp number 08081202932 asha karatu lafiya...*_

_SADAUKARWA GA MUTAN ZAZZAU gami da godiya ga masoyana billions ko trillions ne gdy duk😍😂_

***
"Girgiza kai kurum Sumayya tayi a zuciyar ta tana cewa " To Sumayya ya kika iya? Dole kiyi haƙuri ki jure mawa duk wani tijara da cin mutunci , idan bakiyi haƙuri ba ya zakiyi ? Zaki bar Umman ki da yunwa ne ,kece kaɗai gare ta kece mai nemo mata dole . Yarinya wa kike nema ? Nan inda kike nufa ba hanyar Part ɗin Hajiya bane , Part ɗin Boss ne". Juyowa Sumayya tayi tana kallon wacce take mata maganan Muryar na ba cikakkiyar bahaushiya ba. Ohk to Don Allah zaki iya kaini Sasan Hajiyan gidan?". Eh ba damuwa taho muje! A sanyaya Sumayya ke bin Oruma tana tafe tana kallon ikon Allah komai na gidan abun burgewa ne , ga kyau da tsari , wata ƙofa ne ta buɗe tana ɗaga labulen mai laushin gaske , dark Blue Oruma tana kutsa kanta ciki tare da Sallama ,nan Sumayya itama ta shigo tana bin ta a baya... Kaman yanda Ta zube Gaban Hajiya Juwairiyya tana yin ƙasa da kanta kaman baiwa a gaban gjiyar ta yasa Sumayya cewa " Barka da Rana Hajiya?'.

Ɗagowa tayi tana kallon Sumayya , wanda taji gaban ta ya faɗi daranmmm , sai ta kauda kanta tana kallon Oruma kana ta motsa bakin ta da kyar cike da izza tana cewa " Oruma ina aikin dana saki? Kin ɗebo jiki kin dawo, kin san Gobe ne dawowar Su Fahad da Nurƙalby na ko?". Cikin rawar murya Jidda Oruma tace " Eh Hajiya na sani, na rakota ne na nuna mata nan Part ɗin ki. Shiru Hajiya Juwairiyya tayi kana tace " Ok you are free to Go".

Miƙewa Oruma tayi tana fichewa cikin sauri tare da nufar inda hjy Juwairiyya ta umarci taje. Kusan mintuna biyu da fitar Jidda Oruma Hajiya Juwairiyya ta ɗari da idanun ta ,tana kallon Sumayya wanda anan ma Ita take kallo haɗa ido sukayi nan take taji wani Abu yayi circulating blood ɗin ta game da Sumayya ,fara magana tayi cikin Muryar mai ɗauke kamala tana cewa " Ammm kaman na san ki?".


Kallon ta Sumayya tayi kana ta ɗan girgiza kanta alamun a'a ...ɗan caɓa baki Hjy Juwairiyya tayi kana ta miƙa hannun zuwa glasscup ɗin dake gaban ta tana kaiwa bakin ta ...bayan tasha ruwan ne ta aje tana cewa " Lyk i know this face in somewhere else". So mah lady any thing you want from me?". Aƙwai abun da kike buƙata?".

A hankali Sumayya ta fara cewa " Eh Hajiya nazo ne ki taimaka ki ɗauke Ni aiki gidan ki". Aiki?? Kaman yaya kenan? No no it's too late ,yanxu na daina ɗaukar ma'aikata Cox basu da amana , saboda ba ko wacce ma'akaciya ce Son ke buƙata ba , may b yace baki masa ba, Kuma ina da ma'aikata da yawa wanda bana buƙatar ko wacce ƴar aiki yanxu.


Wani irin ƙwalla ne ya ciko idon Sumayya cikin sauri tace " ki taimekeni Hajiya , kona sati biyu ne ko ɗaya nayi maki aiki ki biyani ,Ni baƙuwa ce ban san kowa anan ba , kima Allah ki taimaka idan ya dawo yace baya buƙata na sai na tafi.....ta ƙare maganan hawaye na sauko mata sharrrr..... Ganin haka yasa Hajiya Juwairiyya cewa " Ina ne gidan mahaifin ki?".


Wani irin bugawa ƙirjin Sumayya yayi ,a hankali tace ' Abba na y rasu, daga Lagos muke ,bamu da kowa anan , dagani sai Umma na , kwatanta mata gidan da suke haya Sumayya tayi ,wanda nan Take Hajiya Juwairiyya ta gane gidan Hayan mlm sabo ne.


Shiru Hajiya Juwairiyya tayi tsawon lokaci kana ta buɗe murya da ɗan ƙarfi tana kirar Hajara ! Hajara!! Cikin sauri wacce aka kira Hajara ta fito tana zubewa gaban ta da cewa " Na'am Hajiya Gani .


Ga sabuwar ma'aikaciya nan na ɗauka , ki nuna mata bedroom ɗin Son ta gyara . Tare da gabatar mata da duk aikin gidan da tsare tsare". Anan zaki rinƙa kwana ko can gida zaki na rinƙa komawa?". A'a gida zan rinƙa komawa da safe na rinƙa zuwa".


To naji amma yau ki koma gobe idan kin zo bazaki koma ba sai jibi, saboda dawowar babban mutum Alh DR Abdullah yana hanya Khamal kuma zai taho yau!.


Wani irin dammm ƙirjin Sumayya ya buga a zuciyar ta tana cewa " Wani Khamal ɗin , ohk na gode Hajiya Allah ya saka da alheri. Yowa kuje ,shine Amsan da Hjy Juwairiyya ta basu Hajara na gaba Sumayya na bin ta a baya'.


***


Tsayawa tayi tana kallon Hoton shi ,wanda take jin zazzafan So da ƙaunar shi a zuciyar ta , a hankali takai hannun ta tana sauke farin galashin idon ta , kana ta shafa hoton ɗan nata tana cewa " I love You my lyf. Allah yaƙara karemun kai yayiwa Rayuwar ka Albarka. Hajiya Sarah ke maganan tana murmusawa kaman wanda Ɗan nata Fahad ke gaban ta. Shigowa Ma'aikaciya na ta tayi na hannun daman ta ,tana ƙarasowa gaban ta , wanda a zuciyar ta cewa take " Wuuuu Ranan da aka wayi gari Fahad ya mutu ko wani Abu ya faru dashi ƙila Hjy Sarah zaucewa zatayi ko itama ta mutu ta bishi...kullum yana aikin kallon hoton shi , sai kace mara abinyi ? Don Allah yabaka ɗa ɗaya tilo ai bai kamata ki ɗauki son duniya ki ɗaura masa ba ,gashi yaron ma ba ji yakeyi ba , aikin sa kenan lalata ƴaƴan jama'a kuma kin sani amma kike take sani.


Barka da hutawa hjy Sarah, ga ƴan matan can an kawo maki a ƙasa". Juyowa tayi a hankali hannun ta ɗauke da wani cup da Fahad ne yayi zanen kansa , kissing ɗin cup ɗin tayi tana cewa " I love You mah Son , Ina sonka so Mai yawa yaro na ....

Tana maganan tana murmushi , kana tace ur Dad is own his way to come back ,zai dawo abroad ya kamata ka dawo gida Nigeria ohk? . Tana maganan kaman wanda aka ce mata ga Fahad a gaban ta. Ɗan tsaki Dije taja a zuciyar ta ,wanda kamin ta farga taji masifan Hajiya Sarah tana cewa " Ke sau nawa zan faɗa maki Idan kin ganni tare da Yaro na ko Hoton shi kar ki rinƙa mun ko wanni magana sai na gama abin da nake yi? Wannan ai shashanci ne ! .


Kiyi hƙr Hajiya". Mtswww tsaki taja a hankali tana juyawa tare da nufan Down stairs don ganin kyawawan ƴammatan da ta kawo mawa ɗan nata , a cewan ta Fahad baxai taɓa zama a Nigeria ba mata ba , wannan dalilin yasata sawa a nemo mata kyawawan ƴammata ta xaɓa nashi , bata damu da lalatan da yakeyi da su ba. Ita bata damu daga nan ya ga wata yace zai Aura ba ,burin ta kenan a rayuwa , taga ta ɗauki jikoki yaran Fahad da hannun ta.


Wani irin rantsatstsen material ta saka a jikin ta , mai launin jah da baƙi yana walwali fatar jikin ta a goge yake , abun ka ga farar mace , fuskar ta kuwa yasha makeup na zamani bakace ita ta haifo yaro saurayi ɗan shekara 30+ kaman Fahad ba.


Zama tayi akan royals ɗin falon masu masifan tsada tana bin ƴammatan dake ta aikin karkaɗa kaman wanda aka ce masu itace Fahad ɗin . Sunyi wani irin sexy shiga mai fidda tsaraici wai adole wannan shine wayewa....

***

Tun subahin fari Sumayya tana kimtsa wa kamin gari yayi haske ta nufo gidan su Sir Khamal wato gidan hjy Juwairiyya...yana yin yanda taji gidan shiru ya tabbatar mata da dawowan gogan ,don taji labarin halinshi da yanda kowa ke shiga taitayin shi idan ya dawo ...sai dai ta matsu ita kanta ta ganshi taga waye shi da yake sa kowa na gidan tsorata?". Sasan Hajiya Juwairiyya ta nufa kaman yanda ya kasance itace mai gabatar masu da abinci don karin kumallo....ba ta tadda kowa a falon ba , sai Tsirarun ƴan aiki biyu mata...gaishe su tayi tana nufar kitchen don da'alama hjy Juwairiyya bata fito ba....

***


Dirning area ta nufa tana shirya mawa Fahad breakfast Kaman yanda Hajiya Sarah ta ɗauke ta akai kuma ta umarce ta , don dama haka takeyi duk kyaun budurwa idan ta shiga gidan a matsayin ƴar aikin Fahad take ɗaukar ta , idan tayi masa ya ƙwaƙule ta ,idan batayi masa ba aranan da suka fara haɗuwa yayi mata cin mutunci daga nan Hjy Sarah ta korata.


Wannan karon Nuwaira ce ta zaɓa a matsayin mai dafa masa abinci tare da kulawa da ɓangaren sa...riga da wando tasa wandon matsatstse iya gwiwa ,sai rigar mai kaman roba yana kama jikin ta , sai ƙamshi take a dole ga karuwa...


Bayan ta kammala komai ne ta nufi bedroom ɗin Fahad da yaraba dare tana aikin zane zanen sa , tun da yayi sallar subahi ya koma barci bai tashi ba har shigowan Nuwaira.... A hankali take tafiya tana wani irin girgiza kana ta nufo ƙayataccen gadon shi... Sir Fahad ur breakfast is ready". Tayi maganan tana wani matse murya a dole taga kyakkyawa.


A hankali ya buɗe lumsassun idon shi yana ware su bisa fuskar ta , ko ba'a faɗa masa ba yasan new cook ɗin shi ce . Ƙasa kauda idon sa yayi daga kallon ta ,don Fahad mutum ne mai shegen Son mata. Hannun shi ya miƙa mata ,aiko cikin sauri ta amshe tana shirin hayowa gadon nasa ,don kallon sa kawai tayi taji pant ɗin ta yafara kwarara... U stand there Kar ki hau mun bed? Me xaki mun? Yayi maganan cikin dixgi da yarfi wanda wannan ya kasance a jinin sa yake. Shiru Nuwaira tayi kana taji cikin Muryar sa da ya tafi da hankalin ta yana cewa " Massage".


Hannun ta takai a hankali tana fara masa tausa kaman yanda yace , tana yin masa wani irin tausa mai tada feelings a sakanni.


Idon ta gaba ɗaya na akan budaɗɗiyar ƙirjin sa da Suma yayi masa rumfa ruffff kwance suke lamɓas luf-luf. Jin hannun ta yayi akan ƙirjin sa tana shafawa tare da sauke wani irin numfashi ,tana shafa suman tare da cewa " Ohhh plsss Plz.....fahimtar mai take nufi yasa shi fixgota yana cikin bargon shi da ita yana hayewa kanta....jin abubuwan daɗin nasa tayi a cibiyoyin ta ,wannan yasata saurin kai hannun ta wurin tana shafa su tare da murxa masa , lumshe idon sa yayi yana kai harshen sa saitin kunnen ta yana wani irin lashen ta har zuwa ƙirjin ta kana ya yaye rigar
End Ads