An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels [7/12, 2:32 PM] Mom Islam: *NAKASA JUREWA* 🪻🪻🪻 Bismillahir rahmanir Rahim, Nagode wa Allah da ya bani rai da lafiya har na kawo muku wannan labari mai suna a sama, idan har kinga ko kaga yayi dai-dai da rayuwar ka/ki, arashi ne, banyi wannan labarin da inci zarafin kowa ba. Free Book Page 1_2 Cikin tashin hankali Ma'aruf ya fito daga side ɗin momy hannunsa riƙe da key car idanunsa sun kaɗa sunyi jajir, cewa yake "Saudart kin cuceni kin lalata mana zumunci kin tozartani a..." karaf a kunnen Anty Jamila, sam baiyi tunanin maganar zuci ta fito fili ba, a hankali ya ɗago kai ya kalli ƙwayar idanunta, sai kuma ya sunkuyar da kansa, dama yasan a wannan karon ma bazata yarda da abinda zai ce ba, wani irin kallo take binsa dashi kai kace taga mugun abu, daga ƙarshe tai ƙwafa tabar gurin, har tayi nisa sosai bai ƙara ko taku ɗaya ba, saima jingina kansa da yayi da jikin bango yana mai-maita innalillahi wa inna ilahir raji'un zuciyarsa kamar zata fashe. A hankali ya janye ƙafafunsa yai side ɗin Hajiya mama, yasan ita kam zata duba damuwarsa, Da sallama a bakinsa ya shiga, sai dai beji daɗin ganinta a yanayin da ya ganta ba, Jiki na karkarwa ya ƙarisa inda take, yayiwa kansa mazauni a saman Capet, kasancewar ita tana saman kujera 2sitter. Ya rasa da wace kalma zeyi amfani domin ta gane nufinsa. "Ma'aruf" Hajiya mama ta kira sunansa fuska babu walwala murya a dakile, Sai da gabansa ya bada rass kafin, yaja gauron numfashi, sannan yace "na'am Hajiya" "Wace tsiyar ka sake aikatawa ƴar mutane?" Murya na rawa yace "Hajiya cewa nayi kawai taje gidansu, saboda daren jiya ko runtsawa banyi ba" "Eh lallai biri yayi kama da mutum, wato gulmace-gulmacen da ake yi a kanka yana nema ya tabbata kenan?" "Kiyi hakuri Hajiya wlhi zanyi miki bayani ɗaya-bayan...." "Dalla can rufemin baki, duk ka susuce kana neman ka mayar da kanka magaukacin ƙarfi da yaji, nidai a iya sanina ban haifi mahaukaci ba, kuma kaf danginmu babu mahaukaci" Tana rufe baki, Anty Jamila ta karɓe da cewa "hmm ai yanzu abinda ya dace kawai ya rubuta mata takardarta shine abu mafi sauki, haka kawai abu yaƙici yaki cinyewa" Sam ya rasa dalilin da yasa basa yarda da maganarsa, sai dai suyi amfani da maganar Saudart, wannan karon ma maganarta ce tayi tasiri a zuciyarsu, "Jamila.." "Na'am Hajiya mama" "Shin kina ganin yaron nan yanada gaskiya kokuma dai sauden ce baya so a cikin rayuwarsa, anyi wannan rigimar karo na uku kenan?" Sai da Anty Jamila ta numfasa kafin tace "nifa na ganewa idanuna, har dukanta yake yi da bulala, bayan nan ya tattakata harda furucin zai sallameta sannan..." "Ya isheni haka" Hajiya mama ta faɗa rai a ɓace. Ya gaza sake furta komai, sbda sun mayar dashi maƙaryaci, har yanzu kansa a sunkuyar yana jiran hukuncin da zasu yanke. "Ma'aruf.." Ya amsa da "na'am Hajiya" Jiki a sanyaye. "Inaso kaje gidansu Saudart yau ɗin nan ka dawo da ita ɗakinta, wannan umarni ne kaji na gaya maka..!! Dum!!! Dumm!! Ƙirjinsa ya buga, yanzu ne ma ya gane tabbas a wannan karon ma Saudart ta sake yin galaba a kansa amma zeyi maganinta, dawowarta shi zai bashi damar horata, "Banji kace komai ba?" Hajiya mama tayi maganar a taƙaice. "Insha Allah zan je amma sai gobe" "Inaa!!, Wallahi ban amince ba, ina Abuja ina Keffi, yau ɗin nan nakeso kaje Keffi" Babu inda ya iya dole hakan yabi umarninta, sosai yakejin zuciyarsa babu daɗi, ya miƙe zai fita, Anty Jamila tace "ayi maka rakiya ne kokuma kai kaɗai zakaje?" Murya a daƙile yace "ni kaɗai zani" Ya miƙe fuuu ya fice. Kai tsaye gidansa ya nufa, gidan nasa yana kusa da na iyayensa, zamu iya cewa katanga ce ta raba, a hankali yai hannunsa jikin get ɗin milk color ya ƙwanƙwsa, Idi mai gadi dake ta rusa gyangyadi ya miƙe a firgice yana cewa "innalillahi ƙila ma me buga ƙofar nan ya jima yana bugawa" ya ajiye rediyon dake hannunsa yake bude ƙaramar ƙofar dake jikin get ɗin. "Ahh Alhaji kaine ?" "Eh matsa" Ganin fuskar ubangidan nasa babu walwalah yasa shi yin tsit da bakinsa har Ma'aruf ɗin ya ɓacewa ganinsa. Koda ya buɗe ƙofa kai tsaye bedroom ɗinta ya wuce, tafkeken frame na hotonta ya tsaya yana ƙarewa kallo, lokaci ɗaya ya runtse idanunsa tare da cije kyakkyawan pink lip ɗinsa, tura hannunsa yayi cikin sumar kansa, a fili ya furta kayun ɗan maciji, "wallahi tallahi na tsaneki na tsani komai naki mtsw" ya fice a bedroom ɗin nata tare da bugo ƙofa, Ita ɗin ba ƙaramar bace komai nata tsaf-tsaf, kasancewarta mace mai tsafta, sbda haka nema ta hana a ɗauko mata ƴar aiki, amma wannan lefukan da ya kamata dashi ya goge duk wata kyakkyawar mu'amala da yayi da ita, sam zuciyarsa ta gaza yi mata uzuri, tunda abinda abinda ya gani ba shine na farkon ganinsa ba, ya shiga bedroom ɗinsa ya zauna saman gado zuciyarsa cike da saƙe-saƙe, hannunsa ya tura cikin aljihun wandonsa ya ciro wayarsa duba time, "ƙarfe hudu" ya faɗa a fili, ma miƙewa yayi ya rage kayan jikinsa ka na a ya shiga toilet, saida ya tara ruwa a bahon wanka, kafin ya shiga ciki ya daɗe sanyin ruwan na ratsa fatar jikinsa, kasancewar akwai zafi sosai a gari, idanunsa a lumshe yake hasaso irin zaman da zasu cigaba da yi a wannan karon saboda wallahi tallahi yakai maƙura bazai iya ba" Daga ƙarshe yai wanka ya fito ɗaure da farin towel, ya rasa me zeyi sai juye-juye yakeyi, kiran wayar Anty Jamila ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi, har wayar ta gama ruri bai ɗaga ba, sai ma shiryawa da ya farayi, sai da ya shirya tsaf ya fito kamar sabon ango, ya Subhanallah "Ma'aruf ya haɗu iya haɗuwa, fari ne amma ba sosai ba, yanada tsayi da ƙiba, tsayin nasa sai ya ɓoye ƙibar tasa, yanada dogon hanci, da ƴan madai-daitan idanu, idan ka kalli pink lips ɗinsa wow, sai ya birgeka, kai kace na wata macen, hatta fatar jikinsa abin kallo ce, sbda sheƙi da sulɓin da take yi, shiɗin fa ya haɗu, bakinsa yana zagaye da gashi ba wani mai yawa ba, sumar kansa koda yaushe cikin gyara take. Matsawa yayi gaban mirror ya kalli kansa a midubi, ya haɗe hannunsa guri ɗaya tare da ambaton alhmdulilah, kana ya ɗibi mukullin mota da wayoyinsa da duk abinda yasan ze buƙata ya fice. Duk wanda ya kalli fuskarsa yasan baya cikin walwalah, har ya isa parking space, ɗaya daga cikin jerin motocin ya shiga wacce already a wanke take sai sheƙi take, black color, Koda ya tada motar, ya danna horn sosai har sai da Idi mai gadi ya fito a guje ya buɗe masa, ya figi mota sai Keffi, Tabbas in banda biyayya babu abinda zai sashi ya tafi Keffi, Yana tafe yana saƙe-saƙe har Allah yayi isowarsa, a bakin wani danƙareren gida ya tsaya da motarsa, yana danna horn. Gidane na gani na faɗa, kafin ka shiga cikin gidan zaka fara hasaso irin tsantsar kyawun gida, tsarki ya tabbata ga Allah, abinda na faɗa kenan yayinda na kutsa kaina ciki, babban gida ne wanda ya haɗa da garden da gurin lilo da sauran kayan more rayuwa, "Anty Saudart ga wancan ɗan na cin can wallahi karki koma ko yazo, kawai ki bari goben mu wuce India tare, tunda an gama shirye-shiryen tafiyarmu" Ƙala batace ba, ta ci gaba da danne-danne a watarta sam ta nuna bata ma san da maganar da Anam ɗin keyi ba, "Assalamu alaikum" Sallamarsa gami da tattausar muryarsa ta ratsa kwanyarta, ko ɗagowa batayi ba, sai dai ya samu albarkacin amsa sallama, shima ɗin ya iya ji da kai, ko ta kanta bai bi ba, ya nemi guri ya zauna a saman one sitter, "Ina wuni yah Ma'aruf" "Lafiya lau Anam ina momy fa?" Anam ta gaishesa fuska a sake kai kace ba itace ta gama ce masa Sarkin naci ba, Yanayin inda ya amsa yasa Saudart ɗago idanunta karaf, suka sarƙe a na juna, fuska ba walwala yaci gaba da kallonta, zuciyarsa nayi masa ƙuna, A maimakon yaji shigowar momy, sai yajie Muryar Dady yana cewa "ashe yaron nawa ya iso" Gabansa ya bada dumm, sam ya rasa dalili, duk girman lefin da Saudart tayi masa bai hanasa ganin girman Dad ba, sosai yakejin nauyinsa har cikin zuciyarsa, koda Dady ɗin ya zauna Ma'aruf sauka ƙasa yayi saman Capet ya sadda kansa kasa kafin yace "Dady ina wuni" "Lafiya lau yarona wlhi nayi farinciki da ganinka, ai nayita neman number Alhaji bukar bata tafiya amman dai lafiya ko?" "Eh lafiya Dady, kasan bai cika zama a Nigeria ba yanzu yana Saudiyya aikin asibiti" "Ayya kasan najima rabon da mu haɗu, amma dai kazo ɗaukar matarka ne ku tafi ko?" Jimm yayi bai ce komai ba. Kasancewar Dady mutum ne mai tawakkali da hangen nesa yace "Ma'aruf kayi haƙuri da duk wani abu da ya faru dan Allah, duk da dai naso jin me ya haɗaku momynta tacemin wai faɗanku ne a tsakaninku, dan Allah kayi haƙuri ku zauna lafiya, a iya zaman da muka yi da Saudart batada abokin faɗa ko tashin hankali.." "Ina never wallahi..!! na rantse da rabissamawati wal ardi babu inda ƴata zataje, haba Alhaji sai kace wata mara galihu?, koda ka fara bincike dalilin da yasa ban baka labarin abinda ya faru ba, saboda baka ƙasar ne, taɓɓ bazata koma yaci gaba da zargin taba" Ta ƙare maganar tana janyo Saudart jikinta, kuka take yi sosai kamar ranta zai fita, shi ko Ma'aruf, addu'arsa bata wuce Allah yasa Dady yaki amincewa da komawar Saudart ɗin, "Haba mom Saudart me yasa kike faɗin haka bayan an wuce wannan gurin?" Dady yai maganar ransa a ɓace. "Ni kawai kayi masa gargaɗin kar irin haka ta sake faruwa, idan ko har hakan ta faru to shida Saudart har abada". Inda tai maganar momyn cike da ƙwarin gwaiwa, sanar ta nuna ko a jikinta. Murmushinsu na manya Dady yayi gami da cewa "Ma'aruf ɗauki matarka ku wuce, zamu yi magana a waya" Jin haka yasa Saudart miƙewa ta wuce ɗakinta da gudu tana kuka. "Anty Saudart kiyi shiru, a tunanina karatun da kika yi ya isa ki koyar da Ma'aruf shiɗin ba komai bane" Shiru tayi batace da Anam komai ba, Anam ta sake cewa "shiɗin wa, dan ubansa, ki rikirkitashi wallahi" Sai yanzu ta amsa mata da cewa "rikitawa fa kikace" "Eh man, nifa anty Saudart na fara zargin Yah Ma'aruf ko dai, shine ma abin zargin?" Saudart tace wa Anam "zargi name fa?" "Bin mata" Cewar Anam, "Hamm Anam Allah ne kaɗai yasan gaibu, wallahi ko sau ɗaya Anam ban taɓa zargin Ma'aruf ba, amma ya ɗauki laifin duniya ya ɗora shi a kaina, menayi masa??!!" Takai ƙarshen maganar tana sake fashewa da kuka, Shigowar momy ne yasa ta miƙe da sauri ta rungume momyn tana cewa "shikenan bani da gata momy, nace masa bana yin facebook yace ba haka ba, wallahi duk wasu social nayi". "Saudart ki kwantar da hankali, idan yanacin ƙasa ya kiyayi ta shuri, anzo ƙarshe, tashi ki shirya ku tafi" Sam ta kasa haɗa kayan ta, sai Anam ce take ta ƙoƙarin haɗa mata kayan, koda Anam ɗin ta gama ta fito da kayan parlo time ɗin Ma'aruf ya fita shida Dady, dole takai mota, sam momy ta kasa yiwa ɗiyar tata rakiya ita kaɗai ta fito, ta shiga mota, lokacin Ma'aruf yana gidan gaba, itama nan ta shiga, Anam tayi musu sallama suka wuce. Kasancewar already me gadi ya buɗe get na gidan, ya figi motar kamar ze tashi sama...! #Cin amana #Zalunci #Badda kama #Rayuwar gidan yarin #Hassada #Zazzafar soyayya #Nadama Idan har naga anyi sharing insha Allah zaku dinga samun update any time. Ga number WhatsApp please ga duk meson shiga channel ɗina 08141799224 Page 3-4 Ganin shiru yayi yawa, ta buɗe hand bag ɗinta ta ciro wayarta ta fara game, sosai take jin daɗin game ɗin sbda har wani murmishi takeyi, Tayi nisa sosai, dan batajin ko ƙarar tafiyar da suke yi a motar, ta ɗan kalli gurin zaman Ma'aruf taga babu shi babu alamarsa, juyawa tayi ta kalli inda suke kafin tace "hmm ashe mun iso ne, yafi ƙarfin yace min munzo" Sai kuma ta fara tunani ya akayi sun iso bata sani ba?" Kawar da tunanin nata tayi ta hanyar bude murfin ma motar ta wuce ciki. Koda ta shiga parlon bakinta ɗauke da sallama tsit babu motsin kowa, to ina ruwanta ma, kamata yayi ta wuce bedroom ɗin ta kawai, duk wannan tunanin tayi shi ne a lokaci ɗaya, Sam zaman gidan ya isheta, tunda tazo gidan Ma'aruf wata uku tayi da farinciki, meyasa bata da gata ne?" Tunanin wace shawara ya kamata ta yanke ta farayi. Ta daɗe tana tufka da warwara daga ƙarshe dai ta wuce kitchen lokacin ana shirin kirin sallahar magriba, Kasancewar duk wani abu da zata buƙata akwai shi a kitchen ɗin yasa ta dafa indomie jollof, parlo tazo ta zauna sbda ta tabbatarwa kanta akwai mutum a gidan ko ya fita" Har aka kira sallah aka shiga bataji motsin kowa ba, ta miƙe ta koma ɗakinta, bayan takai plet ɗin kitchen. Toilet ta shiga ta ɗauro alwala, ta shimfiɗa sallahya ta kabbara sallah, tana kan sallayar tana rokon Ubangiji, har aka kira sallahar isha'i, sai da tayi kafin ta kwanta. Rurin neman agajin da wayarta keyi ne yasa ta ciro wayar a hand bag ɗinta, "momy" ta faɗa a fili tana murmishi. "Hello momy kuna nan lafiya mun iso gida lafiya" "Saudart ki sanar dani idan akwai abinda ya shige miki duhu" "Lahh momy babu komai wallahi" Daga nan sukayi sallama ta ajiye wayar. Lumshe idanunta tayi, lokaci ɗaya rigimar da suke yi da Ma'aruf ta dawo mata sabo fil, tunani ta farayi, anya Ma'aruf bashi da taɓin ƙwaƙwalwa kuwa?" Yo inba taɓin ƙwaƙwalwa ba yace wai itace take posting ɓatattun hotuna a social, da yaushe ma ta fara? ita da ba wani shige shige takeyi a madia ba, to inko haka ne akwai lauje cikin naɗi, yace hotonta ne a profile ɗin da yake zargin itace, waye yake neman ruguza mata farinciki, Inko haka ne, zatasan inda zatayi domin ta ganewa idonta waye yake aikata wannan abin yake fakewa da ita, sbda a kwatancen da yakeyi kamar su ɗaya da wacce yake gani. Kyakkyawa ce ta bugawa a jarida, sbda kyawunta ya ishi duk wani mai tunani misali, fara ce tass ga dogon hanci, gashinta baƙi ne siɗik har gadon baya, tanada zara zaran gashin ido, ga dogon hanci, bugu da ƙari doguwa ce bata da jiki ga diri kai kace kwalbar lemu lolx, a takaice kamar ita tayi kanta don kyawu, Saudart kenan, nasan zakuce me yasa Ma'aruf yake wulaƙantata? muje zuwa yanzu wasan ya fara. Har dare yayi sosai bataji alamar shigowarsa ba, har bacci yayi awon gaba da ita, A cikin barcin nata ne tayi wani irin mafarki, wata budurwa take gani idanunta a rufe tanayi mata dariya hannunta rike da wuƙa suna kokawa, Kiraye-kirayen sallahar asbha da ake yi ne yasa ta farka daga wannan mafarki, da sauri ta dinga mai maita innalillahi wa inna ilahir raji'un, ga wani dukan uku-uku da ƙirjinta yakeyi, a hankali takai hannunta ta mutsike idanunta tare da zuro ƙafafun ƙasa ta wuce toilet, Alwala tayi tai raka'atanil fijir, kafin ta kabbara sallah. Bayan ta idar da sallah ta daɗe tana kwararo adu'oi na Allah ya tona asirin koma waye, domin kuwa abin ya shige mata duhu, a iya rayuwarta bata da wani saurayi bata da ƙawa wace ta wuce mahaifiyarta, ba fita takeyi ba, ko zuwa makaranta ne kawai yake fitar da ita daga gida, sam iyayen nata basa bari ta leƙa ko ƙofar gida. Daga ƙarshe ta jingina kanta a jikin bango sbda barci ya ƙauracewa idanunta, Tana sanye da hijab har ƙasa ta fito parlo ta zauna, remote ta ɗauka sannan ta kunna TV ta nemi guri ta zauna a 3sitter ji tayi kallon ma babu wani daɗi ta kashe TV tare da ɗaukar ɗan ƙaramin pillow ta rungume a ƙirjinta, tayi nisa a tunani batayi aune ba taji an watsa mata ruwan sanyi, da sauri ta mike tsaye jikinta na karkarwa bakinta na ɓari tace "yah..ma..ma" ragowar maganar ta sarƙe mata a maƙoshi, kallon ƙasa kan tayis tayi taga gudajin ƙanƙara, sosai jikinta ke rawa ga wani azababben sanyi da takeji, sbda ruwan da ya zuba mata ba ɗan kadan bane, "Ƙin ɗauka zaki dawo kici gaba da rayuwa kamar da ne? tambayarki nakeyi?" "Jikinta na cigaba da karkarwa tace "ka...ka...ka...." Cikin daka tsawa yace, "Shot up your mouth idiot" Waro dara daran idanunta tayi, tare da janye jikinta daga gurin tunda ko tayi masa magana ba saurararta zeyi ba, "dawo nace..!!" Da baya da baya ta, dinga takowa har zuwa inda yake, batace masa ƙala ba itadai tana tsaye. "Ungo cire wannan munafukin hijabin naki ki sanya waɗannan kayan yanzu a gabana" "Yah Ma'aruf bazan iya ba, sunyi nuna tsaraici da yawa" Ta faɗa tana dafe hannayenta a ƙirji sbda har yanzu sanyi takeji, "Munafuka ni zaki gayawa sunyi tsaraici, ba cikin dare kike ficewa a gidan nan kike zuwa yawon nuna tsaraici ba?!!, Waro dara daran idanunta tayi kafin tace "wallahi tallahi bayan mahaifiyata da ta raineni tun ina ƙarama babu wanda ya taɓa ganin tsaraici na, sai..." "Sai kuma me? wallahi tallahi idan kika bari na sake magana sai na zaneki munafuka kawai" Yai maganar yana zaro belt ɗin wandonsa. "Sai kai" "Kutumar uba" Ya faɗa yayin da ya fara lafta mata belt ɗin wandonsa, Ihu take na neman agaji, anyi rashin sa'a babu wanda yaji bare yasan tanayi, sai da ya tabbatar da ta daku, ta kusa fita a haiyyacinta kafin ya ƙyaleta, ya shiga toilet na bedroom ɗinsa yai wanka bayan ya fito ya gyara jikinsa ya ciro ƙananan kaya blue jeans da t-shirt light blue mai gajeren hannu wace ta daɗa fito da ainihin kyawunsa, sai da ya gyare sumar kansa kafin ya feshe jikinsa da turaruka masu sanyin ƙamshi kana ya fito parlo. Inda ya barta anan ya sameta tanata rusa kuka, tsaki yaja "mtsw" kafin ya fice. Da rarrafe ta ƙarisa ɗaki sbda sam komai ya sauya mata, tashi ɗaya jikinta yayi tsami sosai, Babbar damuwarta idan har tace zata gayawa momy sai sun sami matsala da Dady inba sa'a ba ma yai sanadiyar igiyar aurenta, ta girgiza kai tana faɗin "Noo, zan yanke shawara da kaina" A take ta yanke shawarar inasha Allah idan gari ya waye zata gudu Kano gurin dangin Dady, dan bazataje dangin momy ba. A ranar dai tasha bakar azaba, gashi tanaji tana gani akayi ta nocking ƙofar parlon takasa miƙewa taje ta buɗe haka ta mayar da kanta ta kwanta. Babu abinda ta sa a bakinta, dan ko yunwar ma bataji, sai ma barcin wahala da ya ɗauketa, kamar koda yaushe yauma mafarkin matarnan tayi, a firgice ta tashi, dudu du ma barcin ba wani mai yawa tayi ba, Ta duba agogo ƙarfe 12:pm 10 miss call ta gani a wayar tata tai saurin duba wanda yayi mata, innalillahi ta ambata tare da waro idanu, Hajiya mama Anty Jamila ta faɗa a fili, gashi wayarta babu ko sisi, kuma batada ko biyar a account, "To shikenan sai inta kai musu ƙorafi?, ai gara nima wannan karon in nemawa kaina ƴanci" Ta faɗa tana rarrafawa ta buɗe drowa gurin kayan ta, sai yanzu ma ta tuna ai akwatin kayanta yana mota, wasu ta ɗiba kamar kala goma kana ta sanya cikin jaka ta zuge jakar, cije lip ɗin tayi tare da sake fashewa da kuka, "shikenan bani da gata babu me sona na *KASA JUREWA* wayo Allah na, tawa ƙaddarar kenan" ta faɗa yayinda ta sake fashewa da marayan kuka. Tunani ta farayi, "bata da kuɗi ta ya za'ayi ma tafiyar tayiwu?" Number Anam ta yiwa mtn beep, kana ta mayar da wayar ta ajiye. Har aka kira sallahar azhar bataji jikinta ya sake ba, daƙyar ta miƙe tana tafe tana dafa bango ta shiga toilet ta haɗa ruwa mai zafi ta shiga ciki a bathroom kana tayi wanka daga ƙarshe, sosai taji daɗin jikinta, ta fito ɗaure da towel, tofa, yanzu ne ta fara dawowa haiyyacinta sbda yunwar dake ƙwaƙularta, cikin ƙwarin gwaiwa ta wuce kitchen, murɗa handle ɗin ƙofar da zatayi taji a kulle da key, jingina tayi da jikin bango tare da sauke ajiyar zuciya mai nauyi, Sosai da takejin yunwa, i zuwa lokacin sallahar la'asar yunwa ta fara galabaitar da ita, dan a zaune tayi sallah, tunaninta shine da yaushe Ma'aruf ya shigo gidan bataji alamunsa ba, ko lokacin da tayi barci?", Ta tambayi kanta. har aka kira sallahar magriba tayi tana zaune aka kira isha'i, ta rasa me keyi mata daɗi gashi har yanzu Anam bata kira ba, Data ta kunna kasancewar tana da, ta duba Anam ɗin ko tana online, cikin sa'a ta samu Anam ɗin a online, tai saurin yin mata sallama, Anam ta amsa tare da cewa "Anty Saudart kin koma gida lafiya?" Rubuta mata, "lpy Lou har Kun tafi ne? na nayita yi miki mtn beep baki biyo kiran ba" Eh wallahi ai na sauya simcard, ya dai mutumin naki?" "Hm Anam nidai wata alfarma nake nema a gurinki, banaso kowa ya sani Please ya zamo sirri daga ni se ke, Saudart ta faɗa tana sheshekar kuka, a voice. "Ina jinki Anty Saudart duk maganar da muke yi dake ta sirri ai ban taɓa faɗawa kowa ba" "Shikenan" Saudart ta faɗa, yayinda take sauke ajiyar zuciya. "Please Anam ki turomin da 50k yanzu gobe zanyi tafiya zanbar gidannan saboda wallahi ina cikin matsanancin hali" "Ba sai kin haɗani da Allah ba Anty Saudart barin turo miki, a wane bank?" "First bank ai kinada" "Eh barin tura miki" Ko 30mints ba'ayi ba sai ga alert na 70k Kasancewar any months Dady yana tura mata da kuɗi, ada yana turawa Saudart, daga baya yace mijinta ai shima mai hali ne, yana iya yi mata abinda yafi haka" Hamdala tayi sai ma taji yunwar da takeji ya ragu, tunani ta farayi to wa zata aika ya siyo mata abinci?" Yanzu ba kamar ɗazu ba ta ɗanji daɗin jikinta, ta fito parlo sanye da ƙaton hijabi, ta murɗa handle na ƙofar taji a kulle, a fili ta furta "kodai Ma'aruf yana son kasheni ne?" Tun jiya da yabar gidansu bai koma ba, sannan ya juya sim ɗinsa dan karsu kirashi, yana zaune a office sanye shadda mai ruwan ƙasa, tayi masa kyau sosai, idanunsa na nanne cikin baƙin gilashi, sai juyi yake a kan kujera, Idanunsa a lumshe suke, duk da tulin file ɗin dake gabansa bai hanashi jin fargaba ko wani abu ba, nocking akayi yanaji yayi burus becewa me ƙwanƙwasawar ya shigo ba, sai da akayi sau uku kafin yace "Yes come in" Tunda ya buɗe ƙofa ya hango mutumin nasa yasan yau yanajin rashin mutunci, sbda ba lallai su kwashe ta daɗi ba...! More comment more typing 08141799224 WhatsApp only Share fisabilillah inci arziƙin Manzon 👏 Mom Islam ce.... [7/12, 2:33 PM] Mom Islam: *NAKASA JUREWA* 🪻🪻🪻 Mom Islam Domin samun more pages kuyi following ɗina a Arewabook danna blue link👇 https://arewabooks.com/u/momislam11 Ga wanda basa Arewabook ga link na Wattpad hilis ayi following ɗina 👇 https://www.wattpad.com/user/Momislam2021?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends Page 5-6 "Kai abokina kana cin duniya fa, kaga inda ka sake yin fresh kayi kyau, gaskiya amaryarmu ta iya kula da miji Masha Allah, ai da naso ma in..." Muhammad ya faɗa yana dafa kafar Ma'aruf. "Kai dalla kauce ka bani guri, uban me ya kawo ka office ɗina?" "Nazo inji ya aka kashe boss ne a daren jiya" "Mtsw tashi ka fitar min wallahi zan ci ubanka" Dariya Muhammad yakeyi son ransa, dan ya lura abokin nasa yau a up yake, Ganin baya son wasan ya nemi guri ya zauna har yanzu fuskar Ma'aruf ɗin a murtuke take, yace "abokina Hajiya ce ta aikoni wai idan ka tashi a office tana nemanka", "Naji" Ma'aruf ya faɗa a taƙaice. Koda Muhammad ya gama zamansa ya miƙe tare da yi masa sallama, bai samu albarkacin amsa wa ba ya fice, tunda ya isar da saƙon da mahaifiyarsa ta bashi. Wani ƙululun bakin ciki yaji ya turnuƙe shi, kasancewar shiɗin ɗan duniya ne ya basar tare da duba time 5:20pm ya rufe takardun da ya buɗe dan yau be taɓuka komai ba, ya rasa nutsuwarsa, kai tsaye hanyar gidansu ya nufa, sai da ya biya gurin mai siyarda banƙararriyar kaza ya siyo guda huɗu, na Hajiya ɗaya na Anty Jamila ɗaya, sai nashi ɗaya ɗayar kuma 🤔ina tunanin na Saudart ne uhm. Horn yayi aka buɗe masa get, ya kutsa hancin motarsa ciki a parking space ya ajiye motar tare da fito da ledojin, kana ya shiga ciki, Da sallama ya shiga babban parlon nasu tare da ƙwalawa Hajiya kira saboda bata parlo, babu kowa sai ƙarar TV, Daga bedroom ɗinta ta jiyo muryarsa, da sauri ta fito tana washe haƙora, tana cewa "ɗan albarka, inata cigiyarka, naso in shigo gidan naku sai nayi baƙi" "Hajiya ai dama inada niyar shigowa, sai ga Muhammad ya biyoni har office" Ma'aruf ya faɗa yana ajiye wa Hajiya mama leda biyu, Cikin farinciki ta ɗauko ledar tana cewa "amma dai Saudart na nan lafiya ko?" "Eh Hajiya, tace ma a gaishe ki, da zamu shigo tare, sai kuma na shigo kafin in shiga gida" A wannan karon hankalin Hajiya mama ya kwanta sosai, dan a iya tunaninta Ma'aruf ya sauka kama inda zuciyarta ta labarta mata, Nan sukaci gaba da fira kamar babu wata damuwar da ta gifta a tsakaninsu, Anan gidan hajiyar yai magriba yai isha'i, a takaice ma anan yaci abincin dare. Ƙarfe 9:pm ya miƙe yana danna wayarsa, "Hajiya banga Anty Jamila ba ina ta shiga ne?" "Ai ba kwanan gidannan ba yau kam, taje ƙauye" "Ƙauye??" Ya maimaita, "eh mana, nasan kai baka son zumunci shiyasa kake ƙyamatarsu, duk ɗan halak baya ƙin asalinsa, komai daren daɗewa dole kaje ka dubosu" Kawar da kai yayi, tare da cewa "Hajiya sai da safe" "Allah ya bamu alheri" Hajiya ta faɗa, ta yago jinyar kaza, tare da binsa da murmishi. "Allah ya tsallakar dani wannan case ɗin" Ma'aruf ya faɗa time ɗin da yake ƙoƙarin shiga mota. Kai tsaye ya wuce gidansa, Bayan an buɗe masa get yayi parking motarsa, Ya fito da ledojin tare da jakar aikinsa kana ya wuce ciki, A parlo ya sameta tana zaune saman Capet hannunta rike da gorar hollandia yoghurt, gefe kuma tsire ne ta baje tana ci, Sosai yayi mamakin, ya akayi ta samu arzikin cin waɗannan kayayyakin, koda yake bai kamata yayiwa kansa wannan tambayar ba, "Amma waye ya siyo mata?" Shine tambayar da yake yiwa kansa, Niko nace horo da yunwa? A zahiri taji shigowarsa, sbda ko sallama beyi ba, a matsayinsa na cikakken musulmi, ƙin ɗago kanta tayi bare ta nuna masa tasan da shigowarsa, dogon tsaki yaja "mtswww" tare da take mata ƙafa, har sai da ta ƙwalara ƴar ƙara, cikin jin tsananin azaba tace "sai Allah ya sakamin" Har ya wuce ya dawo da baya, kana ya bige mata baki ya wuce. Hannu ta ɗora a saman lips ɗinta cikin jin zafi ta runtse idanunta. ***** ƘAUYEN ƊAN ƁAURE Tuntsurewa tayi da dariya lokacin da take gwaguyar goruba, kafin ta kalli ƙawarta Gudidi tace "yasin raken Iliya kamar an zambaɗa madara da suga, wai kinhya kinji kuwa?" "A'a Talatu ɗan hammin mana" "Alƙur'an se kinyi min alƙawari" Talatu ta faɗa tana ƙwalalo idanu. Talatu ta sake cewa "kasuwa yau bana son Inna ta sani, idan na hammiki rakena kina faɗa wa Inna ga inda naje, wallahi tallahi sai nayi ƙulikulin kubura dake" Talatu ta ƙarashe maganar tana murguɗa baki, "Zaro ido waje Gudidi tayi, kafin ta haɗiyi wani miyau maƙwat, kana tace "yo ni hauka nakeyi Talatu? wallahi ko haurawa ta katanga kikayi bakina ƙanin ƙafata, amma dai hammin raken sbda miyau ɗina ya tsinke" Talatu ta washe haƙora gami da cewa "ahe dai kina sona" Gudidi tace "sosai ma" Kafin ta gutsiro mata raken sai da ta gama wanke shi da miyau kafin ta miƙa mata, Gudidi na ƙarɓa ta ruga da gudu tana cewa "wallahi sena faɗa me warin baki kawai, da hakori kamar na kaza" Sosai Talatu ta tunzura domin tabi Gudidi da uban gudu, cewa takeyi "tsohuwar munafuka zoki biyani raken da na baki, yau ko zaki hige cikin Ramma sai na ƙwaƙuloki" Karaf sai a kunnen Ramma, mahaifiyar Gudidi, "ke Talatu uwa naji kamar zagina kikeyi?" Ramma tai maganar tana yiwa Talatu daƙuwa, Murguɗa mata baki Talatu tayi kafin tace "ki gayawa Gudidi ta biyani rakena" "Dalla can tafi kiba mutane guri, lokacin da kika bata raken kin nuna min?" Talatu ta wani murtuke fuska tare da riƙe ƙugu tace "kunci bahi, daga ke har ƴar taki" Ta faɗa tana ficewa daga gidan. Tunda Gudidi ta tabbatar da Talatu ta shigo gidansu take ta leƙe ta windo ga wata uwar zufa dake ta tsatsa tsafo mata, "Ramma wallahi kibi Talatu a hankali ko kin mance wacece ita?" Ramma ta wani mulmulo uwar ashar ta yiwa Gudidi gami da cewa "idan na sake ganinki tare da wannan yarinyar wallahi sai na lahira ya fiki jin daɗi" "Toh" kawai Gudidi tace tana cino baki. Tunda Talatu ta fice daga gidansu ta wuce can gonar baban Gudidi, mijin Ramma kenan, Daga nesa ta hango shi, ya haɗa zufa sosai yasha aiki, sai da tayi nazarin kalaman da zata gaya masa, kafin ta ƙarasa gurinsa, har ƙasa ta durƙusa tace "ina kwana baba" lafiya lau ƴar albarka ya Innar taki?" "Tana lafiya lau baba" Gudidi ta faɗa tana sunkuyar da kai. "Baba dama nazo in sanar dakai wani abu, amma kayi haƙuri baba" Talatu ta faɗa tana wasa da sanda wace ta tsinta a inda take tsugune, "Ina jinki ƴata gayamin koma menene, domin na yaba da hankalinki" Talatu tace "baba dama kullum idan zamuje kai niƙan tuwo injin me Kano, kullum sai Gudidi ta tafi da leda ta rage gari, da na tambayeta sai tace wai Ramma ce tace mata ta dinga yin haka, tunda wai kana barinsu da yunwa sai kaje can waje kaci abincinka me rai da lafiya" Koda takai ƙarshen maganar ta miƙe tsaye tare da cewa "amma dan Allah karka ce nice na faɗa maka, saboda gudidi ma taso gaya maka Ramma ta kamata tayi mata duka" Jikin baba na rawa yace "yarinya Nagode, badan kinzo kin gayamin ba wlhi babu inda za'ayi in sani, ungo wannan kyasha alewa" Ta durƙusa ta karɓi kuɗin tanayi masa godiya. Har tayi nisa da hanyar gonar, bata duba ko nawa ya bata ba, sai da ta kusa da ƙofar zuwa gidansu kafin ta duba kuɗin, nera Hamsin ce, Sosai tayi murna, tana ta taka rawa, tana cewa "idan rabonka ya rantse, kai kai kai idan rabonka ya rantse, ɗin ɗirin ɗin" Ta ƙulle hamsin ɗin a hannun zani kana ta shige gidansu da gudu. A tsakar gida ta samu Inna ta raba dambu, kasancewar shi suka girka, "wayo daɗi kaheni wuya barni" Talatu ta faɗa tana cigaba da taka rawa, Kasancewar tsakar gidan nasu yanada tsaki, ita kuma Talatu tana can nesa, Inna tace "Talatu ina kikaje nasa a dubomin ke kizo ki ɗauki allo ki wuce islamiyya ba'a ganki ba" Tofa. Daga can inda take ta buga tsalle ta faɗi tik a ƙasa, ko gezau tunda dama ta riga ta saba, kurma ihu tayi tana cewa "wayyo na mutu na lalace wayyo na balaga ayimin aure wayyo Inna bata sona" Inna na zuba yaji bata san lokacin da taketa zubawa a ƙasa ba, dan a iya tunaninta a abinci take zubawa, Mamaki suruntun Talatu ya bata ko da yake ma, ai ba yau ne farau ba, inda sabo ma ai yaci ace ta saba, Da gudu ta bita tana cewa "wallahi sai kinje makaranta, idan kika zauna a gida me zaki tsinana banda yawo a gari?" A zauren gidan ta laɓe tanajin maganar da Inna takeyi, tana murguɗa baki. Tana ganin Inna ta gama rabon damu ta wuce ɗauki, ta siɗaɗo a hankali taje ta ɗauki nata, ta nemi guri ta raɓe ta fara ci, duk wanda ya shigo ya ganta ze ce marai niya ce. Ashe har tafiyar da takeyi a hankali da zuwanta ɗaukar abinci duk Inna ta gani, sai da ta bari tayi nisa sosai kafin ta leƙo, hannunta rike da bulalar inji ta riƙeta gam, tare da haɗe mata hannaye, cikin kururuwa take cewa "Inna kiwa Allah da ma'aikinsa ki yi hakuri Inna ki duba darajar Musa me jaki da tantabaru, Inna ki duba darajar Hama me tuyar ƙosai, kasaƙe Inna tayi tana jinta, abin ya matuƙar bata mamaki, sai haɗata da sana'ar iyayenta da basa raye take yi, "Na duba darajarsu, amma ki tahi ki wuce makarantar Allo" "Inna nifa malamin ne sai ya dinga ɗagamin gira, ɗan iska ne yasin" Talatu ta faɗa tana buga ƙafa. "La hula wala ƙuwwata illa billah ni Zainabu naga abinda ya isheni" Inna ta faɗa tana riƙe haɓa, "To tashi in rakaki yanzu" Babu inda ya iya dole ta tashi ta ɗauko hijabinta, sbda basa wani rayuwa da hijabi, idan aika yayi nisa haka suke tafiya, koda yaushe rayuwarsu ta sanya riga da ban zani da ban ne. Suna isowa makarantar, Talatu ta zame hannunta a na Inna, a hankali tace "Inna duk maganar da na gaya miki akan malaminnan ƙarya ne wallahi, dan Allah ki koma tun daga nan karki kaini gurin hi, gardawa zesa su ɗagani ya zaneni. "To naji, amma tsan tsaya anan har sai naga higarki" Inna ta faɗa tana yi mata nuni da yatsa, "Wace ni Inna zan higa fa dan Allah ki koma kar malam yace "nayi taurin kai ne kikai min raki ya" Sam bata son a daki Talatu, hakan yasa ta juya tana murmishi. A gindin bishiyar mangoro suke yin karatu, inda suke shimfiɗa tampol a gurin, maza na can gefe mata ma suna gefe, Kusa da gudidi taje ta zauna, cikin ƙasa da murya tace "idan kere na yawo zabo na yawo wata rana za'a gamu, wa na kama?" Gudidi tayi wulli wulli da idanu, cikin marairaice murya gudidi tace "dan Allah dan Annabi Talatu kiyi haƙuri bazan sake ba, daga yau zan dinga ce miki abinnan da ƴan binni suke gayawa yayunsu, Antu yake ko meye ma? "In kinso kice gwaggo babu abinda yai tsalle ya wankan mari, kizo kawai mu cire raini, ta cukuikuyo mata wuyan hijabi, ƙara Gudidi ta tsanda wanda yaja hankalin malam dake biyawa ɗaya daga cikin ɗaliban karatu, da sauri ya tashi tsaye da zafgegiyar dorina yace...! Page 7-8 "Wai ke wace irin sheɗaniyar yarinya ce?, a islamiyya ma bazaki rabu da wannan yarinyar da kika sa a gaba ba? kullum sai an rabaku faɗa kenan" Haba ai tunda Gudidi taji malam yana yiwa Talatu gargaɗi, ta saki baki ta fara bashi labarin rashin jin Talatu, a take a gun ya tsula mata bulala har uku, sam batayi kuka ba, sai dai tayi ƙwafa, irin "zamu haɗu ɗinnan" •••••••• SINGAPORE Bulan Island Wani haɗaɗɗen gida na hango wanda komai nasa da remote yake amfani, hatta get ɗin ya haɗu ya gama haɗuwa, kutsa kaina nayi ciki yayinda nake ta ƙoƙarin kwaso muku jawabi, ƙarewa farfajiyar gidan kallo nayi, wanda yai matuƙar ƙayatar dani, "Masha Allah" na faɗa a cikin zuciyata, gidane na gani na faɗa, gidane wanda idan ka shige shi zaka rantse waɗannan mamallakansa basu da labarin talauci a duniya, sosai yanayin tsarin shuke-shuken zai birge me karatu, hmm yo gini ne na turawa, Wata matashiyar budurwa ce ta fito daga wata ƙofa, wacce na tabbatar da ta danna wasu lambobi ne yasa ƙofar buɗewa, a ƙalla budurwar zatayi 23yrs cikin shiga ta nuna tsaraici, daga ganinta kasan babu musulunci a tare da ita, riga ce a jikinta ƴar yaloluwa milk color, ko Cibiyar ta bata rufe ba, sai ɗan mini skirt ɗin dake jikinta pink color iya cinya, kayan sun matseta sosai, ƙafarta kuwa takalmi ne mai bala'in tsini, duk igiyoyi ne a jikinsa, hannunta riƙe da handbag, gashin kanta har gadon baya, fara ce tass kunsan dai fari irin na turawa, ita ɗin baturiya ce.. Batsha kenan yarinyar mai ji da kyau. Ci gaba da tafiya tayi, inda ta iso parking space securities suna take mata baya, ɗaya daga cikin scuritin shine drivernta, bayan ta shiga back side shikuma ya shiga mazaunin driver, "Madam ina zamuje?" Yai maganar cike da girmamawa, Am sorry to say da yare suke maganar, mukuma zamu ci gaba da yarenmu na Hausa, lolx. "Kaini Ariana hotel" Okay scuritin ya faɗa cike da girmamawa, Tunda suka iso Hotel ɗin na gama tsinkewa, saboda kai da kaga kyau da tsarin gini kamar ba da bulo akayi ginin ba, ga wasu flawoyi da walwali da gurin yakeyi, bayan an buɗe musu get ya kutsa motar ciki, a inda ake parking ya ajiye motar kana ya fito ya buɗe mata ƙofa, takai kamar 10mins bata fito ba, can sai gashi ta zuro kyawawan ƙafafunta wanda suka sha adon jan farce mai kwalliya, buɗe hand bag ɗinta tayi kana ta ciro wayarta ƙirar 💕 ta kara a kunnenta, "Hello Vijay ka gayamin number" Daga can ɓangaren wanda ta kira da Vijay ɗin yace "144" ta katse kiran tana yiwa scuritin alama da ya tafi, girgiza kai yayi kana ya shiga mota ya wuce. A hankali take takawa kai kace tana tsoron taka ƙasa, har ta isa cikin Hotel ɗin, my fans Ina baku labari wani sassanyar sanyi naji ya ratsa kowacce gaɓɓa ta jikina, tunda nikam ba saba zuwa nayi ba, amma anam zan barta, Bayan tayi musu bayani, ba tare da ɓata lokaci ba kai tsaye ta wuce room ɗin, yana zaune saman bed ta sameshi daga shi sai boxer ƙirjinsa a cike da gashi, Yana ganinta ya miƙe tare da hugging ɗinta ya manna mata kiss a kumatu yana cewa "i miss You pretty" Wani farr da idanu tayi masa wanda ya daɗa sace zuciyarsa, ya wani rungume ta ya sinsinar wuyanta, my pretty wane irin turare kike using kowane time sai inajin shauƙi idan muna tare" rufe masa baki tayi da nata, kana ta kashe masa one eye tace "uhhh muyi selfie mana, two days bamu haɗu ba" Kamar koda yaushe idan sun haɗu sai sunyi hoto, yau ma hakan ta kasance, tana rungume a ƙirjinsa shikuma babu riga ga shi ƙirjin nasa duk gashi yayi masa luff, ta wani kwantar da kanta a saman ƙirjinsa, sunyi kyau sosai, kamar koda yaushe idan sukayi hoton suna ɗorawa a media, haka yau ma ta kasance, duk wasu kafafe da suke yi sai da suka ɗora shi. ABUJA NIGERIA "Saudart!! Saudart!! Saudart!!" firgit ta tashi daga barcin da takeyi, jiki na karkarwa sbda wannan kiran da yakeyi mata cikin ƙaraji yakeyi, "Na am" tace, murya a sanyaye, tana takowa har inda yake, "Saboda yawon dare da kike zuwa ne yasa baki tashi da wuri ko?" "Yaya ban fahimci abinda kake cewa ba?" Sai da Ma'aruf ya ƙare mata kallo up and down kafin yace "oky kinaso in baki labarin fitarki ta jiya ne?" "Jiya kuma zuwa ina?" "Zuwa gidan ubanki" Ma'aruf ya faɗa ransa a ɓace, "are you nonsense?, me kike nema a duniya, Saudart na tsaneki na tsaneki har abada bazan sake sonki ba wallahi ki ficemin a gida, ya sanya hannu cikin aljihun wandonsa ya ciro bandir na ƴan dubu-dubu, guda biyu ya watsa mata tana durƙushe a gurin tana rusa kuka, hannunta na karkarwa da wayarsa a hannunta, ya fizge tare da shureta da ƙafafuwansa, har ya fara tafiya, sai kuma ya dawo da baya, ba tare da ya juyo ba, cikin kakkausar murya yace "zan shiga wanka, idan har na fito da ga wanka baki bar min gida ba sai kinyi nadama" Ya ƙare maganar yana cigaba da tafiya. Rushewa tayi da kuka mai tsuma zuciya, a fili ta dinga maimaita innalillahi wa inna ilahir raji'un, zafafan hawaye ne suke ta zarya a kumatunta, Jiki babu ƙwari ta miƙe, a fili ta sake furta "na gaji da wulaƙanci da cin mutunci, cikin ƙarawa kanta ƙwarin gwaiwa tace "ko me za'ayi yau sai ya sakeni, idan ya sakeni shikenan, Dady bazai sake matsamin akan komawa gidansa ba" Tayi maganar tana share hawaye, Yaushe rabonta da ta shiga sashen sa, har ta manta, Cike da ƙwarin gwaiwa ta ci gaba da tafiya har ta iso ƙofar ɗakinsa, inda kasan ƙwai ya fashe mata a ciki haka tayi, ƙirjinta sai dukan uku-uku yakeyi, da sauri ta sake ƙoƙarin kawar da tsoro, ta yi nocking da ƙarfi, sam beyi tunanin ita ba ce, sbda tunda waɗannan abubuwan suke faruwa ko inda yake bata zuwa, buɗe ƙofa yayi fuska a tamke, daga shi sai gajeren wando da farar singileti ya waro ido, sai kuma yaci magani yace "wa ya baki izinin zuwa bakin ƙofa ta?" "Babu wanda ya bani izini tunda ba gidan ubana bane" Sosai yayi mamakin zafafan kalaman da Saudart ta gaya masa, Ya ɗaga hannu zai kai mata mari ta riƙe hannun cikin ƙarfin hali tace "a wannan karon na kasa jure wulaƙanci da tozarcinka, haba Ma'aruf, ko a bola ka tsintoni ai na ci darajar ɗan adam, bare a gidan iyayena ka auroni, ko dan kaga iyayena basu goyamin baya ba? to ka sani wallahi tallahi yau sai ka sakeni nagaji na gaji, NA KASA JUREWA wulaƙancinka, ta ƙarisa maganar hawaye na sake wanke mata fuska....! Please kuyi manege. Mom Islam ce Ayi following ɗina fisabilillah *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻        Mom Islam Page 9-10 Cikin isa da jiji da kai ya furzar da isa mai huci kana yace "me kike nufi?,  ba dan an takura min ba me zan ci dake?, kinga ni sauƙi ma kika nema min kije na sakeki saki uku" Kafar a kunnen Hajiya mama dake ta kwaɗa sallama tun daga parlo bataji motsin kowa ba, a take a gurin ta faɗi sumammiya, cikin azama Saudart ta taho da gudu zata taimaka mata, yai saurin dakatar da ita gami da cewa "idan har kika taɓa ta wallahi sai na illata ki" Ko da jin haka ta miƙe zuciyarta fess dan har ta fara jin tausayin Hajiya, tunda ya gaya mata magana tayi ta kanta, cikin farinciki da samun ƙwarin gwaiwa ta harhaɗa komai nata, kuɗin da Anam ta turo mata ta sake dubawa, a fili ta tace "hmm wallahi bazan sanarwa kowa maganar sakin nan ba, amma fa dole in nemo sheda kodan kar Dady yace min ƙarya nakeyi. Biro da takarda ta ɗauka zuciyarta fess ta wuce ɗakinsa, a bakin ƙofa ta sameshi yana yayyafawa, Hajiya ruwan sanyi, tace "yaya nazo ka rubuta min shedar saki" Babu musu ya karɓa saboda har ga Allah ta zame masa tamkar gobara, duk da tashin hankalin da yake ciki na suman Hajiya be hanashi rubuta mata saki ba, ya miƙa mata tare da cewa "kafin inje asibiti in dawo kar in sameki anan" "Ai bazaka sameni ba, yanzu kam meye haɗinka dani, Allah yabi bayan me gaskiya" ta faɗa tana wucewa abin ta, Ko saurar ta beyi ba ya kin kimi Hajiya zuwa parking space yana ƙwalawa Idi mai gadi kira, da gudu Idi ya taho yana cewa "lafiya kuwa alhjaji?" "Dalla can buɗe min get, lafiya ne zan dinga yi maka wannan kiran?" Jikin Idi na rawa yai azamar zuwa buɗe masa get sbda yasan halin uban gidan nasa. A guje ya fice daga gidan kamar wanda zai tashi sama, cikin ransa ya dinga mai-maita innalillahi wa inna ilahir raji'un, har suka iso (Mai tama District Hospital) Emergency room aka wuce da ita, inda aka bata taimakon gaggawa, Duk wanda ya kalli fuskar Ma'aruf ko ba'a gaya masa ba yasan yana cikin matsanancin tashin hankali, adu'arsa bata wuce Allah yasa babu abinda ya sami hajiyarsa ba, idan kuma ta kamu da wani ciwon ta sanadinsa fa?" Gaskiya bazai yafewa kansa ba. Duk wani likita me shige da fice a ɗakin da aka kwantar da Hajiya, sai ya bishi yana cewa "likita dan Allah ya farfaɗo? likita tana magana?, Inda kasan zautacce haka ya koma, wayarta dake hannunsa ya kalla, a sanadin faɗuwarta, duk ta farfashe, ya kawar da kallon wayar da yake sakamakon rurin da wayar ta farayi, Sunan Anty Jamila ya gani yana yawo a fuskar wayar, sosai gabansa ya bada rass, lokaci ɗaya zufa ya fara karyo masa, be san amsar da ze bata ba, ƙarfin hali yayi ya ɗaga a ɗarare yace "As...asalamu a.." "A'a Ma'aruf yakuke ina Hajiyar?" Shiru yayi bai bata amsa ba, jin shirun yayi yawa, ta katse kiran ta sake kira, dolensa ya ɗaga, duk girman kansa da jan ajinsa baya yiwa mutum biyu, idan ka cire mahaifinsa da ya rasu, wato Hajiyarsa da Anty Jamila ƙanwarta kenan. "Kayi magana mana, wai meke faruwa ne Ma'aruf?" "Hajiya na hospital" Kalmar da ya iya gaya mata kenan ya katse kiran. Sosai hankalinta in yayi dubu ya tashi, ta fara harhaɗa kaya, ƘAUYE Ko da aka tashi daga islamiyya kowa ya watse amma Talatu bata matsa ko nan da can ba, sbda tun kafin a tashe su malamin ya fita, anyi masa kiran gaggawa,  ɗaya daga cikin manyan ɗaliban ne ya yi musu addu'a kowa ya watse, har lungu Talatu taja wuyan hijabin Gudidi, mutane biyu ne a biye dasu,  ɗaya sahura ce ƙawar Gudidi, ɗayar kuma Lantana sunanta ƙawar Talatu, Rawa suke tiƙa sunayi musu waƙa suna cewa ... "🎺A casu mata a casu, ku casu ba me rabaku araba ace anyi cuta, a zamanin nan na yanzu" Sosai suke tiƙar rawa, kan kace me har Talatu tayiwa Gudidi lilis, babu mataimaki sai Allah, duk su biyun ƙawayen nasu basu isa suja da ƙarfin Talatu ba, sosai ta haɗawa Gudidi jini da majina, kafin faɗan ya ƙare, Gudidi na tafiya tana ɗingishi, tace "Hegiya maiyya jaka me ƙarfin Allatsine me kai kamar na duwatsun murhu" Talatu ta biyota da gudu, itama gudun takeyi tana ɗingishi har ta ƙarisa gidansu, Tana shiga ta samu Tabaiyye da malam sai uban musayar yawu suke yi, ita kuma ta shigo tana kuka babu wanda ya saurareta, Wucewa tayi ɗakin Tabaiyyen ta kwanta a ƙasa ko zataji sassaucin mutsikar da tasha gurin Talatu. Malam ya gyara zaman babbar rigarsa kana yace "Wallahi wannan hine gargaɗi na ƙarhe idan kika sake ragemin hatsi  kowa ze kama gabansa" Cikin masifa Tabaiyye tace "yo in kama gaban nawa mana, ka gayamin me na tsinana tunda na aureka, kaf kiwon da iyayena suka haɗoni dashi sun ƙare, me kake dashi da zan ɗin ga ɗiba? ta gyara ɗaurin zaninta taci gaba da cewa "ko yanzu na fita a gidanka zan samu saurayi sabo fil gada gau me jini a jika" Tun da ya ji ta faɗi haka, ya wuce ƙofar ɗakinsa kana ya ɗauki buta ya kuskure bakinsa, har ya nufi hanyar zaure ya juyo  yace "Tabaiyye kiji ta tsoron Allah karki ragemin masara" "Da tsoronka nakeji mtsw" Tai maganar tana yatsina masa fuska. Hankali kwance Talatu ke tafiya har ta iso gida, tunowa da babbar baƙuwar da Inna ta gaya mata zasuyi ne yasa ta washe haƙora, a fili tace "na rantse da Allah ina son ganin ƴan binne" da gudu ta shige tana cewa "Inna dan Allah ki biyoni ban ɗaki da buta tsuuuuu (Gudawa) nakeyi" Sam bata ma ga Anty Jamila dake zaune saman tabarma ba, cikin ɗaga murya Inna tace "Talatu zanci mutuncin ki", tana ƙare maganar ta miƙe takai mata buta, "Yauwa Innata idan nai aure zanyi kewarki" Ko ƙala Inna batace mata ba ta dawo gurin Anty Jamila. Murmishi Anty Jamila tayi kafin tace "wallahi A'isha tana birgini" Inna tace "taɓɓ bakisan waye A'isha bane" "Haba Inna ai Kowane yaro da ƙuruciyarsa" "Hakane kam" Inna ta faɗa tana dariya. Bayan ta fito daga banɗaki ta ware idanunta, fess ta ɗora su kan Anty Jamila, washe jajayen haƙoranta tayi kafin ta taho da sauri tace "ahe kin ƙaraso Inna Jumai?" "Na ƙaraso A'isha, amma sau nawa zan ce miki bana son ki dinga ce min jummai?" "To kiyi hakuri yasin mancewa nakeyi, amma dai kinzo kiyi mana wata da watanni ne ko?" Anty Jamila tai dariya kana tace "a'a yanzu ma daga Madobi nake gobe insha Allah zan koma Abuja" Zaro idanu Talatu tayi sai kuma ta matso kusa da Anty Jamila tace "dan Allah ina Hajiyar nan da take zuwa tana raba mana hinkafa?" Anty Jamila tace "Hajiya tana gida, sbda rashin lafiyarta ne ma zan koma gobe" "Ahe bata da lafiya?" Talatu ta faɗa tana ƙara tattaro nutsuwarta, kai kace dagaske, Ita ko Anty Jamila duk tambayar Talatu tayi mata sai ta bata amsa. Koda Inna tazo ta samesu sunata hira, abin yai mata daɗi, Tace "Jamila kuna zantawa ne da ƴar taki?" Anty Jamila tai murmishi. Jollof ɗin dawa da wake Inna ta kawo wa Anty Jamila, ayko taci sosai ba laifi dan kaɗan ta rage tasha ruwa, Wayar Anty Jamila ta fara ringing, Ganin sunan Ma'aruf yana yawo a kan screen ɗin wayar yasa tai saurin ɗagawa, tare da cewa "my Son ya akayi?" "Anty Jamila Hajiya fa bata magana kwata-kwata" Cikin firgici Anty Jamila ta fara mai-maita "innalillahi wa inna ilahir raji'un" Kana tace "son kayi haƙuri yanzu dare ya fara tunda ana shirin kiran sallahar magriba, insha Allah gobe ƙarfe huɗu zan taho, Allah ya bata lafiya" Sosai hankalin Anty Jamila ya tashi, sanda a iya saninta Hajiya ba ta taɓa irin wannan ciwon ba. Nan ta labartawa Inna abin da ke faruwa, Inna tace "itama zata bi Anty Jamila su tafi tare" Talatu tace "taɓɓ wallahi he anje dani kawai ki tafi har binni ki barni hu'um" "Ba fa wani abin daɗi ne ze kaini can ba, rashin lafiya ne, kuma befi in ɗauki kaya kala ɗaya ba" Da ƙyar da lallashi dan sai da Anty Jamila tayi mata alkawarin zata turo me mota ya kawo ta Abuja sannan ta amince, A daren Inna ta haɗa mata kayanta a bako sbda kafin su wuce zata kai ta gidan mahaifiyar babanta. Bayan sallahar isha'i, suka wuce gidan Kaka, da sallama Inna ta shiga kafin tace "zauna mana ai dai kya gaihe ta" "Ina wuni" Talatu ta faɗa tana turo baki, "lafiya lau ƙawata na ganki da jakar kaya?" Inna tace "wallahi na kawo ta ne zamu wuce Habuja gobe saboda Hajiya Habiba babu lafiya" "Ash sha, Allah ya bata lafiya, zaki daɗe ne?" "A'a kwana ɗaya zanyi" Inna taba kaka amsa, kaka tace "to ki ja mata kunne banda rahin kunya, dan ba kowa bane ze ɗauka" Sosai Inna tayiwa Talatu faɗa kana tayi musu sallama, bayan ta miƙa wa Talatu ɗari biyu taba wa kaka ɗari uku, Kaka ta washe haƙora tana cewa "Allah ya tsare, "maiyyar kuɗi" Talatu ta faɗa tana hararar kaka" "Nayi ɗin naga uwarki ce ta bani ko?" Koda taji barci kaka ta hanata hawa gado wai kar tayi mata fitsarin kwance, sai da Talatu ta bari kaka tayi barci kana ta lallaɓa ta kwanta can gefenta, Kaka dai tasan ta hana Talatu hawa gado, gashi fitila ta mutu, tunda su basa ganin wutar lantarki, cikin ihu da kururuwa take cewa "ke Talatu tahi ki gani kwarto" Tunda Talatu taji kaka ta faɗi haka, ayko ta kunce zanin kaka ta cukuai kuyeshi, ta janyo hannun kaka kiiiii ta janyo ta ƙasa, ta haye gadon daga can inda take ta sauya murya tace "ke ƴar tsohuwa jiya naji kina adu'ar Allah ya baki miji hine nazo mu shirya" Haba kaka ta sake rikicewa, bakinta na rawa tace "nifa tsohuwa ce haba kai kuwa baka ga jikina duk a tamushe ba, na roƙeka nidai ban ce haka ba" "Zo nan" Talatu ta faɗa cikin daka tsawa, ganin kaka ta rikice sosai yasa ta koma kan gadon ta kwanta tunda tasan bazata taba komawa ta kwanta acan ba. Ƙarfe huɗu na asbha Anty Jamila ta farka, dan ba wani barci me nauyi tayi ba, ko wanka batai ba, ta shirya cikin leshi Black anyi masa ado da zare golden color me adon duwatsu farare, mai kawai ta mutsika, tayi tunanin Inna tana barci sai taga itama har ta gama shiri, kasancewar basu da wani kaya me nauyi suka fita neman me mashin, sbda masu mashina ba kasafai suke yawo ba, kasancewar ƙauye ne sosai, idan kaga mashin sai na masu zuwa gona, can maƙotansu Inna taje ta roki alfarma, tai sa'a yaron gidan na nan, ya fito da mashin ɗinsa suka hau zuwa tasha, Sai da suka ƙarfe shida kafin motar ta cika, sannan suka fara tafiya...! Ayi haƙuri jiya baku ga posting ba, wallahi kuna raina kunsan weekend mutum ba shi da wani hutu sosai. Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻        Mom Islam Page11-12 Kai tsaye asibitin suka wuce, koda suka iso ba'a basu damar shiga ba, dole suka nemi gurin zama suka zubawa sarautar Allah idanu, Tunani Anty Jamila ta farayi, to me ya faru da Hajiya har abin ya kaita ga haka, duk da ansan cuta da mutuwa duk na Allah ne, amma jikinta yana bata akwai wani abu da ya faru, Kallo ɗaya tayiwa Ma'aruf ta kawar da kai, kafin tace "wai meke faruwa ne ban gane ba?" "Na me fa anty?" Anty Jamila tace "my son kafin faruwar ciwon Hajiya babu abinda ya faru" Shiru yayi kamar me tunanin wani abu, hakan ya bata damar gano zargin da takeyi akan faruwar ciwon hajiyar, "ina magana baka ce min komai ba?" "Um..am..da...dama" Katse shi tayi rai a ɓace tace "ka yimin bayani inda zan fahimta" "Dama mun rabu..." Ma'aruf ya fara magana yana sarƙewa, cikin tsoron magar da ya fara yi tace "kun rabu da wa?, Saudart?" "Eh, Anty amma dan Allah ki fahimceni, wallahi har yanzu ba ta dena posting hotunan banza ba" Sosai jikin Anty Jamila yayi sanyi ta tabbatar wannan maganar ce ta jawo  ciwon na hajiya, gashi abu yayi tsamari tunda ba'a bari a ganta, "can anjima likita ya fito daga room ɗin da aka shigar da Hajiya, "yauwa kune ƴan uwan matar da aka kawo jiya ko?" "Eh mune" Anty Jamila tai saurin amsawa, "Ina son ganinki a office" daga faɗar haka likita ya wuce. Kafin yakai ga shiga office ɗin nasa har ta ƙaraso, kusan a tare suka shiga. Nuni yayi mata da gurin zama, bayan ta zauna ya zauna shima, kana ya ajiye fil ɗin dake hannunsa,  cire farin gilashin dake manne a idanunsa yayi kana yace "ƴar uwarku tana buƙatar kulawa sosai, a iya binciken da muka yi, mun gano tana daf da kamuwa da ciwon zuciya, ya kamata kuyi ƙoƙarin ganin kun bi matakan da zamu gaya muku", Hankalin Anty Jamila a tashe tace "likita ina jinka" "A rage yawan ɓata mata rai, sannan a yawaita sa ta farinciki dan Allah" "Insha Allah" ta ce tana share ƙwallar da ta kwaranyo mata, Daga nan ya basu wata takarda yace taje ta siyo magani a pharmacy, godiya tayi masa kana tace "yanzu zamu iya ganinta? "Eh" yace mata "amma banda hayaniya" kai tsaye ta wuce  zuwa siyo magani. Tare da Ma'aruf suka je pharmacy ɗin, bayan sun dawo suka ɗunguma dukkansu zuwa room ɗin Hajiyar har da Inna, Alhmdllh ta tashi, Norse suka samu a ciki tana ɓarewa Hajiya ayaba, gefe kuma ga ragowar kayan marmarin da Ma'aruf ya siyo, Koda suka haɗa ido da Ma'aruf juyar da fuskarta tayi, sai kuma tace "Allah sarki Inna wallahi kuna rai na" Inna ta gaishe ta, bayan ta amsa tayi mata ya jiki, Anty Jamila ma tayi mata ya jiki, amsawa tayi, kana tace "Ma'aruf ne ya gaya miki bani da lafiya ko?" Murmishin yaƙe tayi, tana gyaɗa kai da sauri" Mayar da kanta tayi ta kwanta, har yanzu tana jin ɗaci a cikin zuciyarta.           ************** Duk wani kaya da tasan nata ne, sai da ta kwashe shi, abinda tasan ba nata ba ko kallonsa batayi, takai ƙarfe 1:pm tana tattara kayan, daga bisani ta fito harabar gidan tana ƙwalawa driver kira, da sauri ya taho yana cewa "Hajiya Barka dai" "Yauwa Barka, dama inaso ka ɗauko car key  kashigo ciki, zaka taimaka min in fito da kaya" "Toh" Yace mata, tana komawa ciki Idi mai gadi ya kalli driver kafin yace "idan an baka naka kason dan Allah ka tuna dani" Suka kwashe da dariya. Bakinsa ɗauke da sallama driver ya shiga ciki, koda Saudart taji muryarsa ta ce masa ya shigo, bayan ya shiga ya taimaka mata suka fito da kayayyakin, shi kansa yawan kayan ya bashi mamaki "anya ko lafiya?" Ya tambayi kansa. Kai tsaye mota suka kai kayan, kasancewa akwai Toyota Coaster, ta kwashe har kayan gadon nata. Abin mamaki da ya ishi su driver da mai gadi, amma basu da bakin magana sbda gargaɗin me gidan ne, Kai tsaye Keffi suka nufa, suna cikin tafiya wayarta tayi ruri, sunan Anty Jamila ta gani yana yawo a kan screen ɗin wayarta, zaro ido tayi a fili tace "ai na tambayeki aka ce min kinje anguwa, gaskiya bazan amsa wayarki ba, kokuma ai yanzu an free barin ɗauka" Ta danna kore tare da karawa a kunnenta, "Assalamu alaikum anty ina yini kinje lafiya" Saudart ta gaishe ta cike da ladabi, "Naje lafiya Saudart, yanzu kina ina ne?" Kai tsaye ta bata amsa "Ina Keffi anty" "Keffi kuma?" Saudart ta bata amsa da "eh" Wani ƙululun baƙinciki ne ya tokarewa anty Jamila a  maƙoshi, "Amma me yasa zaki yanke hukunci ba tare da kin shawarce mu ba?" Dariya ma abin ya ba Saudart, tai ƙoƙarin dai daita nutsuwarta kafin tace "anty ai saki uku yai min" Dumm...dumm..dumm, Ƙirjin anty Jamila ya bada, zufa ya fara keto mata, lokaci ɗaya numfashinta ya fara barazanar ɗauke wa, Inna dake la'akare da yanayin da ta shiga tace "Jamila wani abun ne ya faru?" "Hmm Inna, wai Ma'aruf ne ya saki Saudart, abin haushi ma har saki uku" Waro idanu Inna tayi kafin tace "wannan ai ganganci ne, shi beyi shawara da kowa ba kenan?" Duk wannan maganar da suke yi a harabar asibitin suke yi, gudun kar hankalin Hajiya ya sake tashi. Sai yanzu Antu Jamila ta daɗa gano sanadiyyar rashin lafiyar Hajiya. "Alhmdllh" Saudart ta ambata lokacin da drivernta yai horn a bakin get na gidansu, sai da me gadi ya buɗe ƙaramar ƙofa ya leƙo kafin ya buɗe get ɗin yana ɗagawa Saudart hannu, Itama hannun ta ɗaga masa har suka wuce parking space. A hankali ta buɗe murfin mota ta fito zuciyarta fess kamar anyi mata bushara da gidan aljanna, drivern ya fara firfito da kaya yana ajiye wa, sai da ya kammala kafin ta ce "ka zauna gurin me gadi barin sa a kawo maka abinci" "To yace mata yana washe haƙora" Sallama yayiwa me gadi bayan ya amsa, suka fara hira kai kace tun dama can sun san juna, Can anjima sai ga ƙatuwar foodflaks, da sauri me gadi ya karɓa yana cewa ƴar aikin "Nagode sosai" ta wuce tana amsa masa. Me gadi ya shimfiɗa musu tabarma suka baje abincin a plate suka fara ci, jollof ɗin taliya da wake, yaji kifi sosai, Nan suka fara ci hannu baka hannu ƙwarya, bayan sun kammala ci sukayi hamdala aka ci gaba da fira, Saudart ta aiko ƴar aiki da kuɗi, koda tazo cewa tayi "sannunku driver anty ce ta aiko ni" "To to gani" Ya miƙe tare da sanya takalminsa ya bita, "Gashi wai kasha mai" Jiki na rawa ya karɓa yanata yi mata godiya, daga nan yayiwa driver sallama ya wuce, Yana tafe hanya yace "taɓɓ motar da take shaƙe da fetur shine zata wani ce insa mai, wallahi nabar sawa. Yai maganar yana ci gaba da driving. Bayan shigarta gida, ta samu momy na kitchen ita da ƴar aiki, lokacin sun kammala abincin rana kenan, tunda momy ta ganta jikinta ya bata babu lafiya, sbda ganin yanayin jikinta da fuskarta duk tabon duka wani gurin yayi ja wani gurin fari, da kallon tausayi tabi ɗiyar tata, cikin sanyin murya tace "Saudart jeki huta ina zuwa. Kai tsaye ɗakinta ta wuce, komai yana nan fess kamar tana gidan, tunda dama su biyu suke zama a ɗakin ita da Anam, koda yaushe a tsaftace yake, kasancewar da suna nan da basa nan ƴan aiki suna gyara ko ina, Bayan su momy sun kammala hidimar abinci, ta wuce ɗakin Saudart, a zaune ta sameta tana shan yoghurt, wanda ta ɗauko yanzu a fridge, "Saudart ya sake yin tsiyar tasa kenan?" Momy ta jefawa Saudart tambaya, "Hmm momy kenan, ni wallahi azaba ta isheni, wai har yanzu zargina yakeyi bayan ni ban ma san wacce yake zargi ba, yace kullum sai tayi posting hotunan banza, ɗazu ma ya nuna min, kamar mu ɗaya momy" Bubbuga bayanta momy tayi kana tace "Saudart ki kwantar da hankalinki, inaga zamanki da wannan mara mutuncin yaron yazo ƙarshe" Saudart tai murmishi takaici, kafin tace "momy yau na nemi saki a gurin Ma'aruf kuma Allah ya taimakeni" Tafi momy tayi, wanda yai nuni da tana cikin tsantsar farinciki, ta rungume ɗiyar tata kana tace "na gode miki, kinga yanzu ko dadynki ya dawo kinada sheda, tunda dama goyon baya ya samu shiyasa ya dinga ci miki mutunci, in banda shinɗin me kuɗin gaske bane wallahi da tuni na shiga na fita, amma babu wani abu da kika yayibo mana?" Saudart ta yamutsa fuska kana tace "momy iya kaya na ne sai furniture ɗin da driver ya ɗauko suna can ɗakin baƙi" "Mtsw, kedai anyi wa wuya wallahi, ki rasa abinda zaki kwaso duk girman gidannan?" Momy ya sawa ko ina key fa" "In ya sawa ko ina key bazaki ɗauko ko wani abun ba, wanda zaki tunguna masa haushi?" Momy tai maganar tana yin tagumi, Su ma gidan nasu tubarkalla sbda gidane na gani na faɗa, amma ta sawa kanta done abin duniya. Kwanan momy uku a asibiti sannan aka sallameta, Inna kam batayi tunanin haka jikin yayi tsamari ba, shiyasa ta zauna, dan kaya kala ɗaya ta taho dashi, daga ƙarshe dai ta koma sa kayan Hajiya mama, A ranar da aka sallamesu, suka wuce gida, bayan sun karɓo magunguna da sauran abubuwan buƙata. Jiki yayi sauƙi alhmdulilah sai dai ƙarfin jiki, koda suka iso gida an gyareshi tsaf, kasancewar sunada ƴan aiki sunkai su uku duka mata, biyu ƴan mata ɗaya dattijuwa. A falo suka zauna, aka kawowa Hajiya pillow ta sanya a saman 3sitter ta kwanta. "Inna muyi wanka se muci abinci ko?" Antu Jamila ta yiwa Inna magana. "Toh" Inna tace tana tashi ta wuce ɗakin Antu Jamila, tunda dama gidan ba baƙonta bane, Kai tsaye ta wuce toilet tai wanka, kasancewar duk wasu na'ura da ake amfani dasu tun zuwanta na farko aka nuna mata yanzu kam bata wani tambaya, tunda a ƙalla tayi zuwa biyar har da wannan. Bayan ta fito a wanka ta samu Anty Jamila ta ajiye mata kaya riga da zani na atamfa, da sabon skirt. Bayan ta shafa mai ta sanya kayan, kana ta fito parlo, "sannu ta yiwa Hajiya kana ta nemi guri ta zauna" "Yauwa Hajiya ta amsa tana ce mata, kin baro mutuniya ta acan kenan?" Inna tayi murmishi kafin tace "ai kam tana can gurin kaka" Hajiya tace "ina son ki dinga tafiya da ita fur kinƙi" Ai bata taɓa zuwa Habuja ba ko wani gari ban taɓa zuwa da ita ba, kinsan ta akwai rawar kai" Inna tai maganar tana kallon ƙaton TV wanda ya kusan ɗauke bango guda, Har gabanta aka ajiye mata abinci a kuloli biyu, ta farkon ta buɗe, faten dankalin turawa ne a ciki, sai soyayyen naman kaza a sama, hannu tasa kafin taci tai bismillah, ba wani me yawa taci ba ta mayar da murfin ta rufe, Hajiya mama ta ƙwalawa yarinyar da ta kawo abincin kira, da sauri tazo, Hajiya mata tace "ki damawa Inna kunun tamba idan akwai" "Akwai Hajiya ai jiya muka je kasuwa tare da Alhaji" Kawar da kai Hajiya tayi, kafin ta ƙirƙiro murmishi tayiwa Inna, Wow Masha Allah, anty Jamila tayi kyau sosai, doguwar riga ta sanya A baya coffee brown ta gaban rigar anyi mata adon light pink tasha stone, tayi rolling ɗankwalin a kanta, Cike da nuna kulawa tace "Hajiya ya ƙarfin jikin?" "Yayi sauƙi jamila, ina Ma'aruf?" "Ai tunda aka sallameki bai biyomu ba" "To babu damuwa" Hajiya ta faɗa a takaice. Tea anty Jamila ta haɗa tazo ta zauna tana kallon TV tana sha, can anjima aka zubowa Inna kunun tamba wanda ya ji kayan ƙamshi ga fanke a gefe, Hajiya ma tace "idan da ragowa a kawo mata" Koda aka kawo mata harda fanken tasha kunun sosai kuma taci fanken, daga nan kuma hira ta ɓarke a tsakaninsu, har aka kira sallahar azhar ba'a sake ɗora wani abinci ba, na safen suka ci. Kasancewar ba a motar Ma'aruf ɗin suka dawo ba, shi kam ya wuce nasa gu, Zaune yake a restaurant yayi uban tagumi, sam ya rasa abinda yake damunsa, sannan ya rasa abinda ma yake tunani, daga ƙarshe yace " yanzu da wane ido zan kalli Hajiya?" Sai kuma yace "to me na aikata da nake jin shayin haɗa ido da ita?" Koda aka kawo masa list na abinci ya zaɓa ɗaga musu hannu yayi, cikin nemawa kansa ƙakwarin gwaiwa yabar gurin, kai tsaye motarsa ya shiga ya wuce gidansa, sai da yai wanka kana ya fito cikin shiga ta alfarma, yau kam sarautar ce ta motsa, sbda kayan sarakai ne a jikinsa, sumar kansa tasha gyara Masha Allah gaskiya Ma'aruf kyakkyawa ne, ya fito sai ƙamshi yakeyi. Kafin yai nocking na a get ɗin gidan Hajiya sai da ya ɗau tsawon mintoci daga ƙarshe yai nocking me gadi ya buɗe masa, in kaga yadda yake taku kai kace basaraken ne, sai dai fadawa ne babu a tare dashi, kai tsaye ya wuce sashen Hajiya, da sallama ya ƙarisa badan yaji Muryar Hajiyar ta amsa masa ba, muryoyin mutum biyu yaji, na anty Jamila da na Inna, Bayan ya gaishe su, ya durƙusa ya gaishe da Hajiya mama, cikin fushi ta amsa, ya koma ya zauna, wayarsa ya ciro ya ɗan fara danne danne, yana jiran sakamako, "Ma'aruf..!" Hajiya ta kira sunansa murya a dakile, "Na'am Hajiya?" Ya amsa yana kallon ta, ka kyauta basan me zance maka ba, amma bazan ci gaba da sa maka ido baka da mata ba, tunda har ka zaɓi ɓata min rai akan abinda hasashen sa kakeyi, ko yanka ka za'ayi bazaka tan tantance gaskiya ba, ka nemo mata nan da sati biyu, "Hajiya mat..." Ta katse shi da cewa "wannan umarni ne bawai shawararka nake nema ba" Daga Inna har anty Jamila babu wanda yace ƙala, sbda dama tun kafin zuwansa, Hajiya ta yi musu magana akan idan tana magana dashi karsu sa mata baki...! More comment more typing.. Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻        Mom Islam Page 13-14 Ta inda Hajiya ta shiga ba tanan take fita ba, sai da tayi masa tass kafin tace "ka tashi kabani guri"   Jiki babu ƙwari ya miƙe, sam bega lefin faɗan da Hajiyar tayi masa ba, tunda ya rabu da Saudart, dama ita ce ta zame masa ƙarfen ƙafa.., ƘAUYE Inna kam barci ra bi da ra bi tayi, kasancewar tashin hankalin da ta shiga a daren jiya, abin da bata so shine ya faru, wato makara ta makara har gari yayi haske sosai, da sauri ta tashi ta waiga inda Talatu take kwance, sbda a iya tunaninta talatu ta kwana a inda ta barta jiya. Cikin sauri ta fito tsakar gida tana ƙarewa ko ina kallo, "lahaula wala ƙuwwata illa billah" Inna ta ambata tana tafa hannu, sbda ganin ɓarnar da Talatu tayi mata, cikin ɗaga murya ta ƙwala mata kira "Talatu..." Ta amsa da ƙarfi kana ta rugo a guje tana cewa "kaka meye?" "Mele dan gidanku, ina ƙulin ƙosai na?" "Yana waje har na gama suya jiran masu siya kawai nakeyi" Talatu ta bata amsa tana washe haƙora, "Talatu kin cuceni" Inna ta faɗa tana zabga uban tagumi, Talatu tace "kaka kike zaure ki duba idan banyi dai-dai ba seki sake toyawa" Kaka ta ma rasa me zatace mata, kai tsaye ta wuce zauren ta barta a gurin, kafin takai ga duba ƙosan da talatu soya talatu tai wuf ta cika hannu ta jefa a baki, da sauri ta furzar tana kakarin amai, Kaka ta durƙusa a gaban ƙosai tana ƙare masa kallo, kafin takai hannunta ta ɗauki guda ɗaya ta ɗan gutsira, da sauri ta furzar tare da salati, Kaka na ji kamar ansa kubewa, "uwarki ce tasa ko ni ce na saka?" Kaka ta mulmula mata zagi, Talatu tai tsuru da idanu kafin kaka ta yanke hukunci talatu ta ƙwalawa al'majiran da suke kusa dasu kira, tace "suzo ana sadaka" Kafin kaka tayi wata magana ƙosai ya ƙare, suma masu karɓar sadakar Basu san meye ba, suna dai kallonsa kamar ƙosai, jiki babu ƙwari kaka ta tattara kasko suya ta koma ciki, sai zuwa ake ana cewa a bada ƙosai, kaka tana cewa "babu" Talatu ta shigo tana rawa tace "albihirinki kaka" Kaka tai banza da ita, Talatu tace "yo tunda bazaki amsa ba, dama zan ce miki kowa ya samu, Kaka ta tashi kamar me zuwa ɗakin girki ta ɗauko bulala, ta dinga shinfifaɗawa Talatu, ihu take iya ƙarfinta amma kaka taƙi dena dukanta, tun talatu na ganin abin kamar wasa har takai ga, ta riƙe bulalar hannun kaka, tana kuka ta riƙe kwankwaso kana tace "alƙur'an sai ayi kare jini biri jini, ki sake dukana ki gani idan ban karya ƙashinki naba karnuka ba" kaka ta zaro ido tare da ƙoƙarin fincikar bulalar, ta ga ina bazata iya ba, ranta a ɓace tace "Talatu ki saki wannan tsumagiyar kokuma in ɗauko wace zata sa jikinki lauhi, banda rahin  kunya da tarbiyya ki dubeni ki dinga gayamin wannan maganar bayan kin yimin asara kuɗi ba nawa ba kuɗin bahi ne fa" Talatu tace "daga abin arziƙi ya koma na tsiya, wallahi kaka ki rabu dani kar in sake yamushe miki fatar jikinki" Tunda kaka ta ji haka, ta sakar mata tare da cewa "shegiya addababbiya me ƙarshen Giwa" "Eh naji ko me ƙashin meye ai ni jikarki ce kuma in haka ne ma ƙashin mu iri ɗaya ne" Talatu na gama rufe baki, Hansai me siyarda wake da mangyaɗa tayi sallama, kallon ta Talatu ta tsaya yi, a iya zamanta a ƙauyen bata san ta ba, doguwa ce sosai ga ƙiba da ɗuwaiwaka bugu da ƙari kana ganinta sai kace irin samudawan nanne, "Kaka tace "maraba da Hansai, yau kece a gidan namu?" "Eh nice, ba zama ne ya kawoni ba, dama nazo karbar kuɗin wake ne wallahi kaka kin saɓa alƙawari, yau mako ɗaya da kenan" Hansai tai maganar cike da masifa, Kaka tace "dan Allah kiyi hakuri asara nayi yau" Hansai tace "na rantse da Allah bazan matsa ko nan da can ba he an bani kuɗin wake da mai" Talatu ta matso kusa da Hansai kafin tace "kina ta wani yiwa mutane rantsuwa ba se akwai bane za'a baki? kokuma za'a baki babu ne?" "Kan uba, kaka wannan wacece ?" Hansai ta jefawa kaka tambaya, "Jikata ce" Kaka ta bata amsa. Hansai ta nuna Talatu da yatsa tace "wallahi ki kiyayeni in ba haka ba, zan takaki" Kaka tace "a gaba na?" "To bakya ganin rahin kunyar da take yimini?" Idan ku ka ga Talatu a gaban Hansai, abin sai ya bawa me karatu dariya, ƴar ɗugul amma bakinta yaƙi mutuwa, "Kiyi abinda zakiyi ke kin daɗe bakiyi ba, ga fili ga me doki, da kaka zakiyi faɗan ko dani ki zaɓa a ciki?, tai saurin ɗauko gawayi ta zana a ƙasa tana cewa "idan kin isa ki tsallake wannan layin" Hansai ta riƙe baki, a fili tace "tunda nake a duniya ban taɓa cin karo da fitsararriyar yarinya irinki ba, amma yanzu nan zan koya miki hankali" Hansai ta matsa zata cafko talatu, Talatu ta fizge bulalar dake hannun kaka da ta zama kamar gunki, kan kace me ta zafgawa Hansai a ɗuwawu, a zabure tai waje da gudu tana tsinewa Talatu, hamdala kaka tayi, da fitar Hansai  a gidan, tace "ƴar albarka Nagode miki" "Kika godewa wa?" Kaka tace "ke mana Talatu tawa.." "Mtsw ki jira haɗuwata dake wallahi sai na rama dukan da kikai min" Kaka ta zaro idanu tare da tafa hannu, cikin mamaki tace "yanzu idan aka ce ki dukeni zaki iya dukana?" "Fess ma kuwa harda kwantar dake in ɗame miki fatarin sikel ɗinki in tsula miki" Cikin sauri kaka ta koma ɗakinta, sbda ta tsorata da lamarin Talatu, Dama ba tun yanzu ake kawo mata ƙorafin Talatu ba, wasu suce kodai bata da hankali ne, kowa da abinda yake cewa. To my lovely fans, yanzu zamu tsunduma cikin labarin, FARKON LABARI. Keffi Gidane ɗan madau-daici, wanda ya kasance mu haɗu a parlo, alhmdulilah Alhaji Aliyu ɗan kasuwa ne, duk da cewar be ɗaukaka sosai ba, amma yana da rufin asiri, matarsa ɗaya Zainab, suna zaman lafiya tun auren saurayi da budurwa, takai kusan shekaru 3yrs Allah be bata aihuwa ba, kwatsam Allah ya bata rabo, wanda ya kasance suna ta murna da, kaf danginsu sai da suka kira suka sanarwa, sosai Alhaji Aliyu yake bawa Zainab kulawa ta musamman, baya fatan a wayi gari Zainab ta nemi wani abu a duniya bata samu ba, ga shi ya ɗorawa kansa son Duniya, kwanci tashi cikin zainab yakai 3months, taje scanning akayi mata albishir da tagwaye duka mata, bakinta sam yaƙi rufuwa tsabar murna da farinciki, koda ta dawo gida ta nunawa Alhaji Aliyu takardar scanning ɗin, sai ma ya fi ta murna. Dama yana tura takardar neman aiki a kafafen sada zumunta, Allah besa ya samu ba, koda yaushe burinsa ya siyi motoci sannan yayi gida na alfarma, hakan be samu ba saboda hidimar yau da kullum, Yau ma kamar kullum yana tsaye a bakin titi yana ta re mota, wata danƙareriyar mota tai parking a gabansa, ƙirar Lexus, burinsa be wuce yaga waye mamallakin motar ba, a hankali ya rage tsayin gilashin motar, tare da washe haƙora yace "Alhaji Aliyu manya, ashe kana duniyar nan" Alhaji Aliyu ya zaro ido tare da cewa "Innalillahi Muktar kai ne a wannan mahaukaciyar motar?" Wanda Alhaji Aliyu ya kira da Muktar yace "haba mutumina dan wannan motar ai ba komai bace, saboda inada waɗanda suka fisu tsada a gida, insha Allah zanyi maka alkairi abokina" Jikin Alhaji Aliyu yana rawa ya shiga mota, suka ci gaba da fira, firar duniya kawai suke yi. Muktar yayiwa Alhaji Aliyu kwatancen gidansa, A kasuwa ya ajiye shi, kasancewar yana siyarda takalma da handbag. 9:pm Alhaji Aliyu ya dawo daga kasuwa, ya fara bawa Zainab labarin haɗuwarsu da Muktar sbda abokinsa ne tun suna primary, harda kyautar da yace zeyi masa, sosai tayi farinciki, take ce masa kasan wasu abokan alkairi ne, "wasu kuma akasin haka" Already sunyi musayar lamba. Washe gari tun ƙarfe 7:am time ɗin ma yana barci, saboda tun sallahar asbha da ya dawo ya koma ya kwanta, janyo wayarsa yayi dan yaga me kiran nasa, yana ganin number Muktar ya miƙe zaune har yana mutsike idanu, kafin ya amsa kiran, "Hello abokina barka da safiya" Muktar yace "Barka dai, dama nace ya kamata kazo zuwa gobe zan wuce SINGAPORE" "To..to..to gani nan zuwa yanzu ma kuwa insha Allah" Alhaji Aliyu ya ba Muktar amsa, ko wanka beyi ba bare brush haka ya sauya kaya, yayiwa Zainab sallama ya wuce. Be wani sha wahala gurin gano gidan nasa ba, kasancewar ya bashi adreshi da komai, sai da ya gama ƙarewa anguwar kallo kafin hankalinsa ya dawo gurin get ɗin da yake tsaye, ya Subhanallah 🥳 gidan fa abin a kalla ne, dole Alhaji Aliyu ya koma kamar ya fito daga garin su Gudidi, kamar wani me jin tsoro, ya miƙa hannu a hankali kana ya danna ƙararrawa, sai ga me gadi nan ya buɗe masa, "daga ina?" Me gadin ya jefo masa tambaya, "Ni dama abokin me gidan ne, kuma yasan da zuwana" Me gadi yayi murmishi kai da ka gansa ma kasan ba musulmi bane, "mu ai bamu san da zuwanka ba" Alhaji Aliyu ya zaro ido tare da cewa "yanzu dai ba wannan ba, ka taimaka ka buɗemin" Me gadi yace "sai ka bani abin shan sigari" Sosai Alhaji Aliyu ya fara tsoron me gadi kasancewarsa zabgege ga damtse na ƙarfi, jiki na rawa ya tura hannunsa cikin aljihu ya ciro ɗari biyar, "Haba me zanyi da wannan, nasan idan ka shiga gurin me gida sai ka samu abinda ya ninninka shi, dan haka nayi maka sauƙi kawo 5k, Alhaji Aliyu ya waro ido kana yace "da wannan ɓata min lokacin da kake yi ai gara in kirashi" Ya danna number Muktar, ringing ɗaya ya ɗaga kana yace "ka iso ne?" "Eh wallahi, gani a get anƙi barina in shigo" "To idan kuka gama ina jiran ka ni zan fita ta ƙofar baya" Muktar ya faɗa yana katse kiran, "Tofa ga ƙoshi ga kwanan yunwa, ya Allah ka ɗorani a kansa, jiya har ina mafarkin mota wallahi, ace dai yau in koma da galleliyar mota wallahi da na haye wow" Duk wannan zancen a zuci yakeyi, Daga ƙarshe dai yace "kayi haƙuri ga dubu ɗaya dan Allah" "Abinda na gaya maka shi zaka bada ai zaka samu idan ka shiga" Me gadi ya faɗa yana sake tare bakin get, dama kuɗin nasa dubu goma ne, idan ya bada dubu biyar ai ya zaftare kudin, amma haka zeyi shahada ya bayar tunda babu inda ya iya. Daga ƙarshe dai dole ya ƙirgo dubu biyar ya mika masa sannan ya barshi ya shiga. "Aljannar duniya" Alhaji Aliyu ya faɗa yana tafe yana ɗaga kai sama, Ze iya cewa a iya saninsa da kalle-kallensa be taɓa ganin gida irin na Muktar ba, Yama rasa inda ze dosa tunda ko ina ƙofofi ne na gilashi kai kace ƙofofin zinare, Ƙara kiran waya yayi, Muktar ɗin yace ze turo yanzu a ɗauke shi, yayi masa godiya ya tsaya yaci gaba da kalle kalle-kallensa....! Muje zuwa 💥 Kunsan me na fara ji ga me daku fans? Naga kamar labarin beyi muku ba, jikina ya fara sanyi, bana ganin comments sam wallahi bana jin daɗi. Wanda suke son shiga group ɗina ko channel wanda nake posting kumin magana ta WhatsApp kawai Please 08141799224 Mom Islam ce.. *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻        Mom Islam Page 15-16 "Alhaji Aliyu.." juyawa yayi dan yaga me kiransa, security ya hango yana sanye da bakaken kaya kai kace police, kafin yai magana, ya ji ance masa, "Alhaji yace ka shigo ciki" Jiki na rawa ya bi bayansa suka wuce, Tofa anan ne Alhaji Aliyu yayi suman tsaye, "shin wannan gurin anya ba wata duniyar bane?" Tambayar kansa yake yi a cikin zuciyarsa, "Barka da shigowa abokina" Muktar ya katse masa tunani, "Yauwa Barka nayi sa'a" Alhaji Aliyu ya faɗa yana murmishi, Bayan sun gaisa Muktar yace "kamar inda nayi maka alkawarin mota gashi, irin wacce ka ganni a ciki jiya Lexus" Tsabar farinciki be san lokacin da ya zame ƙasa ya riƙe ƙafafun Muktar yana yi masa godiya ba, Muktar yace "babu komai abokina ai ka wuce nan" Daga nan suka ɗan taɓa fira, Muktar yace ze fita gobe yana son barin ƙasar, sallama sukayi yana ta yi masa godiya har parking space Muktar ya rako Alhaji Aliyu, securities suna biye dasu, Boot aka buɗe masa, yaga kayan abinci iri iri, nan ma ya sake kwasar godiya, aka miƙa masa key ya shiga, kai tsaye ya wuce yana ɗaga musu hannu, har yanzu ya kasa tabbatarwa da kansa shine yayi wannan haɗaɗɗiyar motar?" can kuma yace "na yarda da maganar da bahaushe yake cewa idan rabonka ya rantse..." Allah ya temakeshi ya iya driving, Cike da shauki ya ƙarasa gidansa, Zainab da taji horn ɗin mota ta fito da gudu, ganin mijinta ne a ciki yasa ta yin farin ciki marar misaltawa, bayan ya fito a motar taje da sauri ta rungume shi. Daga nan rayuwa ta fara sauya musu, lokaci ɗaya Alhaji Aliyu ya zamo attajiri, kasancewar any months se Muktar ya tura masa kuɗi, After 1 month Friday, bayan an sakko sallahar juma'a, lokacin cikin Zainab yakai 6momths suna zaune a parlo tana zaune saman cinyarsa, cikin shagoɓa tace "Habiby sana'ar da abokin ka yakeyi ta birgeni, sbda kyautata wa mutane da yakeyi" Alhaji Aliyu yace "Kamar kin shiga rai na  kuwa, amma kinsan me?" "A'a" tace tana girgiza masa kai, "Nifa har yanzu ban tambayeshi wace sana'a yakeyi ba" Alhaji Aliyu yai maganar yana shafa mararta da cikin ke kwance se motsi yake. Zainab tace "Gara ka tambayeshi kaga kai ma sai ka dinga taimakawa na ƙasa da kai, Allah se ya daɗa buɗa maka" "Toh bari zan tambayeshi, idan da hali sai in roƙe shi arziki" Yanzu kam ba koda wane lokaci suke haduwa ba, yawanci ma sai a WhatsApp tunda baya zama a Nigeria sosai. Washe gari yana zaune saman two sitter Zainab na kusa dashi tana ɗaura masa agogon hannu, wayarsa ta fara rurin neman agaji, kasancewar wayar tana saman table wanda ya kasance a tsakiyar ɗakin, Zainab ta mike zata ɗauko, ya riƙe mata hannu kafin yace "na hutar dake maman ƴan biyu, Ko da yaga Muktar ne me kiran yai murmishi yana ce mata "abokina ne" Ya ɗaga tare da sallama, daga can ɓangaren Muktar yace "wallahi jiya na dawo idan da hali yau ka zo mu tattauna wata magana" Cikin rawar jiki yace "to abokina insha Allah zan zo da yardar Allah ga mom twins ma tana gaishe ka" Muktar yace "ina amsawa, ka ce mun samu ƴan biyu?" "A'a zadai ku samu" Muktar yace "to Allah ya sauketa lafiya, Alhaji Aliyu ya amsa da amin" Zuwa yamma da misalin ƙarfe 5:pm ya kai masa ziyara, wannan karon be sha wahala gurin ganinsa ba, koda suka zauna sun tattauna akan matsalolin rayuwa, sannan ya yi masa godiyar alkairan da yake yi musu, kana yace masa yaga ana ta ginin masallaci, a takaice dai yana ta yabonsa, daga ƙarshe Alhaji Aliyu yace "nima in da hali a taimaka min da sana'a amma nafi sha'awar irin taka" Muktar yai murmishi kafin yace "abokina samun damar shiga sana'ata ba abu bane me wahala, idan ka amince da ƙa'idoji" Cikin rawa jiki yace "haba wane ƙa,idoji?, Nifa nan da kake gani na, na shirya wallahi" Muktar ya katse shi da cewa "ka shirya ranar sunday, kaga dama saura kwana biyar, zan koma SINGAPORE se muje tare in kai ka gurin me gidana" Koda ranar sunday ta zagayo an gama visa da komai da komai, yayiwa Zainab alƙawarurruka da dama, kafin tafiyarsa. A ranar da zasu wuce tasha kuka kamar me, SINGAPORE A wani danƙareren gida aka yi musu masauki, inda Alhaji Aliyu yai ta cewa "ashe mu muna ƙauye ne, ashe duk ƙyale ƙyalen da yake gidan Muktar bagu ne, wannan masaukin da suke ciki ya mugun tafiya da tunaninsa, sai na natawa yake a zuciyarsa yana cewa "kuɗi sunyi a rayuwa" Kasancewar Muktar ɗin ya fita ganawa da oga yasa Alhaji Aliyu tashi tsaye tare da ɗaga hannayensa biyu yace "ya Ubangiji ka yalwaceni da dukiya me yawa wacce za'a kirani a faɗin duniya da ƙasar waje" Daga ƙarshe ya nemi guri kana ya zauna cike da tarin damuwa. Abin mamaki, idan ka shiga bazaka fita ba har se lokacin da aka sallameka, duba agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa yayi, kana yace "ƙarfe biyar, babu azhar babu la'asar?, Wannan asara tayi yawa" Gama maganar tasa yayi daidai da shigowar Muktar, cikin fara'a yace "abokina ka shigo ciki, tofa, sai yanzu ya fara tunanin yayi babban ganganci fiye da inda beyi zato ba, "to dama kai nake ta jira ka tafi ka barni shiru" Muktar yace ai munata shawarin inda za'a ɗauke ka ne, yanzu dai mu shiga ciki" Kafin ya miƙe tsaye se da ƙirjinsa yace "rass" ya dafe ƙirjin nasa yana maimaita innalillahi wa inna ilahir raji'un, a zuciyarsa, Kai tsaye suka wuce part nan oga, wani abu Muktar ya danna kawai suka yi ƙasa suuu, sai gasu a wani kyakkyawan ɗaki me kyau, ya hakimce akan wata haɗaɗɗiyar kujera wace zamu iya cewa ta zinare ce, mutumin zeyi shekaru 50yrs a duniya, yayi musu nuni da su zauna, da yaren su, tunda oga ya fara magana Alhaji Aliyu kallonsa yakeyi kawai badan ya san me yake cewa ba, sai da ya gama magana Muktar yace "Abokina nasan baka fahimci abinda oga yace ba, dama cewa yayi duk wani bawa ba haka kawai yake samun kuɗi ba, wasu sana'arsu siyar da kayayyakin masarufi wasu kidnaping wasu siyar da kayan shaye-shaye wasu neman mata da sauran su, mu sana'ar mu itace siyan mutane mu shigo dasu addinin mu, saboda musulunci yayi yawa a duniya, gaskiya anata ƙoƙari gurin ganin anyi yaƙi da hakan, daga trillions har abinda ya ninninka shi zai baka idan ka amince..! Kunsan me yasa? kun kashe min jiki babu comments babu shar'hi ko kunfi so ya koma paid book ne? Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻        Mom Islam Page 17-18 Yana matuƙar ƙaunar musulunci a rayuwarsa, lokaci ɗaya kansa ya fara juyawa ya rasa wane irin tunani yakeyi, gaskiya akan son Duniya baze iya ja da addinin musulunci ba, Duk wannan shawarin a zuciyarsa yake yi, yayi nisa da tunani ya tsinkayo maganar Muktar yana ce masa, "abokina duk wata shawara da zakayi ai bakin alƙalami ya bushe, kana tunanin zasu ƙyale ka ne?, ka riga da ka gama sanin sirrin su, hamm kayi haƙuri kawai ka mori duniya son ranka sannan ka mori lokacinka da tarin dukiyar da zaka samu, wanda kaf danginku idan an bibiya babu wanda ya taɓa riƙe dukiya irin ta. Cikin ƙanƙanin lokaci shaiɗan yayi galaba a kansa, sukayi yarjejeniya,  akan ze kawo musu ƴan mata ko jarirai guda uku, Muktar yace "abokina ai baka da matsala tunda bawai zaka kawo su duka lokaci ɗaya bane, shawarar da zan baka, tunda likitoci sun tabbatar muku da ƴan biyu matarka zata haifa, ka bada ɗaya se ku riƙe ɗaya" Sosai tsoro da firgici gami da munmunar nadama mai ɗauke da dana sani suka ɗarsu a zuciyar Alhaji Aliyu, babban tashin hankalin ma "wai wanda ya shiga baya fita" Se yaji kamar zai amince sai wata zuciyar ta dinga nusar dashi, daga ƙarshe dai ya amince da bayar da ɗaya daga cikin ƴan biyun da Zainab zata haifa, kafin nan ya roƙesu alfarma akan a juyar mata da tunani kar ta taɓa jin wata damuwa game da bayar da ƴar Tata, wace bata san  a ina zata rayu ba. Hakan ko akayi, tun kafin yaje mata da labarin bokan su ya gama aiki, Wasu mahaukatan kuɗaɗe aka bashi wanda suka zarce tunanin mai tunani, tashi ɗaya Alhaji Aliyu ya fara birkicewa, tunda a iya tsawon rayuwarsa bai taɓa ganin irin wannan tarin dukiyar ba, Akwai wani tsafi da suke yiwa masu ƙaramar ƙwaƙwalwa, sai da akayi masa kafin ya dawo daidai, Kwanansa biyar suka dawo gida Nigeria, kai tsaye ya wuce gidansa, dan ya kasa riƙo kuɗaɗen suna gidan Muktar wasu ko suna bank, Duk wanda ya kalli fuskar Zainab ze gane tana cikin farinciki saboda dawowar mijinta, sannan ga dukkan alamu anyi nasara duk da ƴar ramar da yayi. Kallon tausayi ya bita dashi, sbda zuciyarsa ta karye sosai, kamar wanda aka cirewa lakka a jiki ya rungume ta suka wuce ciki, "Habiby ya naga kamar baka so dawowa ba, naga mood ɗin ka duk ya sauya" Cike da kewarsa take maganar tana zaune a gefensa, janyota jikinsa yayi kana yace "ba haka bane maman ƴan biyu, sai kuma ya ji lokaci ɗaya ƙunci ya sake mamaye zuciyarsa, sbda ko ɗa guda ɗaya ta haifa dole ya bar musu" "Habiby muje kayi wanka sai kaci abinci" Ta katse masa tunani. Dole ya miƙe sbda kar ta gane halin da yake ciki, bayan yayi wanka yaci abinci, ya fara tunanin ta ya ya ze tare ta da wannan maganar? ya jima yana tattauna maganar da zuciyarsa, har washe gari ya kasa ce mata komai 3:an motar Muktar ta shigo gidan Alhaji Aliyu, already ya san da zuwansa, lokacin kowa na barci ban da Zainab da hankalinta ya fara tashi, Ta window take leƙensu, Wani ƙatoton kwali babba sosai suka kamo Alhaji Aliyu ya shigo dashi parlonsa, bayan sun fito Muktar yace "abokina Zaka ji dadin wannan harkar fa, saboda ka zama sabon shiga shiyasa kake jin babu daɗi, ni nan da kake gani ƙanwata na bayar tun tana da shekaru 9yrs anata cewa ba'asan inda take ba, nayi ƙus da bakina..." Alhji Aliyu ya katse shi da cewa "amma ka zuwa ganinta ko jin labarin ta?" Muktar ya waro idanu kafin yace "abokina abinda nake so ka sani shine, idan har ka riga ka basu abinda suka nema har abada kai da tambayar su wannan abin, za ka sawa zuciyarka baka taɓa sanin wannan abin a duniya ba, sannan kaja bakinka kayi shiru, sannan ka nemi wata muhimmiyar sana'a wacce zata lulluɓe tarin dukiyar da kake da ita" Babu inda ya iya dole ya ɗauki shawarar Muktar tunda ya fishi gogewa akan harkar, duk wani abu da Muktar ya san ze kawo wa alhji Aliyu matsala se da yayi maganinsa. Bayan sun rabu da Muktar sam beyi barci ba a ranar, kasancewar gyare gyare da ya dinga yi, sannan ya shiga jiji app yana ta searching na gidan da ze siya da motoci da duk wasu kayan alatu, gaba ki ɗaya hankalin Zainab ya kasa kwanciya, duba da tunda sukayi aure baya taɓa ɓoye mata komai, abin mamaki yau ya ƙaurace wa ɗakinta, nasa ɗakin kuma yayi masa key, kiran sallahar asbha da akayi ne ya sa shi saurin  ƙarasa gyare-gyaren daga ƙarshe yai alwalah ya wuce masallaci, fitowa tayi kai kace munafuka ta murɗa handle na ƙofar taji a kulle, da sauri ta koma bedroom ɗinta ta jingina da bango tana ta saƙe-saƙe a ranta. Bayan ya dawo sallahar asbha kai tsaye ɗakinta ya wuce, ya sameta ta idar da Sallah tana kan sallahya tana gyangyadi dan bata ji shigowarsa ba, zama yayi a gabanta tare da shafa cikin ta buɗe ido a hankali, bata nuna masa ɓaci ran ta ba tace "ina kwana Habiby" "Lafiya mom ƴan biyu da fatan kin tashi lpy ya yarana" "Lafiya lau" tace ma sa, a takaice, Ya lura ta sauya sosai, amma dole ya sanar mata sbda lokaci yana ƙurewa. Janyota jikinsa yayi, ya cire mata hijab kana ya zuge mata zip ɗin rigar jikinta, lokaci ɗaya halittun ta suka baiyyana, ɗan turo cikin tayi sai kuma ta cuno baki" "Mene ne?" Ya tambaye ta in cold voice, "babu komai uhm Habiby duk ka sauya bana jin daɗin hakan, ko kana son yaran mu suma su fuskanci ɓacin raina? kuma kasan illa ne a gare su" Tana gama rufe baki ya zura harshensa a bakinta, ya fara yi mata wani salo me wuyar fassara, hannunsa ya zagayo dashi ta ƙugunta cikin cold voice yace "komai ya canja ciki har da abinda na fi ƙauna" Ɗan turo masa ƙirjinta tayi kafin tace "uhm dole ka bar wa yara tunda ka girma" "Kafin su zo ai zan ɗan sha koda na one week ne" Zainab ta waro idanu kafin tace "ka mance har ruwa yana fitowa?" Suka sakarwa junansu murmishi me kyau, "AM kinsan me?" "A'a habiby" Zainab ta faɗa tana rangwaɗar masa da kai. Yace "baki tambayeni ya mukayi akan maganar neman aiki ba?" Cikin nutsuwarta tace "Habiby ai kai ne ya kama ta ka bani labari" Sai da yaja dogon numfashi kafin yace "Zainab bazan ɓoye miki komai ba" Ya kwashe kaf inda sukayi ya gaya mata, da sauri ta matsa kusa dashi, tana ja da baya tana daga zaune, "Haba Zainab, a tunani na zakiyi min maganin damuwata? me yasa zaki gujeni?" Abin sai kace wani sihiri, ko da yake ya riga yasa an juyar mata da hankali, lokaci ɗaya ta share hawayen dake kwaranyo mata tace "shi kenan Habiby na amince" Tattaro ƙarfinsa yayi kana ya ɗaga ta sama yana juyi da ita, suna yiwa junansu murmishi...! Idan naga comments gobe nayi muku alkawarin read more 6 insha Allah Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*       🪻🪻🪻       Mom Islm Page 19-20 Sai da ya tabbatar da ya kwantar mata da hankali, kafin yabar bedroom ɗinta, time ɗin ya barta har ta fara barci, Kai tsaye bedroom ɗinsa ya wuce, ya baje a ƙasa tare da zuba wa kwalayen da suke ɗauke da kuɗaɗen idanu tunanin wace irin sana'a ya kamata ya fara, tun kafin a fara yi masa tambayar ƙaƙa uwarka ta haifeka, lokaci ɗaya ya yanke shawarar buɗe katafaren shagon siyarda atamfofi lases da su abaya da duk wasu kaya na mata da maza, Tunda waɗannan kuɗaɗe suka zo masa ya ƙaurace wa kasuwar da yake zuwa, Kwanci tashi asarar mai rai, ranar Litinin ranar da ta kasance musu rana mafi ɗumbin tarihi. Tun dare ta fara naƙuda aka wuce da ita Hospital, cikin hukuncin Allah ta haifo yaranta guda biyu duka mata, kamar su ɗaya sak komai nasu iri ɗaya, badan alama da Norse sukayi musu ba, ƙarya ne ka tantance su, koda aka kai ta ɗakin juyawa cewa takeyi "ina yarana ina yarana?" Dole aka kawo mata su ta rungume su, wasu zafafan hawaye suka kwaranyo mata, nadama mai cike da dana sani ta fara yi, duk da ita ta amsa masa, kama daga danginta har da gin alhji Aliyu, duk wanda yazo ganinta ba'a bari ya shiga, sannan babu wanda ya san me ta haifa, An so sallamo su da yamma, alhji Aliyu yace a bari zuwa gobe da asbha, lokacin ta sake hutawa, amma yanzu idan aka sallameta mutane zasuyits hayaniya, haka ko akayi, ƙarfe 11pm na dare, Muktar yazo ya tafi da ɗaya daga cikin ƴan biyun wato Usaina, idan kuka ga inda ake fita da jariran sai abin ya bawa mai karatu mamaki, ba wai na alhji Aliyu kawai aka ɗauka ba, jarirai da yara wanda aka ɗiba a Nigeria sunkai dubu, koma duk wata hakan yake kasancewa, Bayan hakan ta faru, suka tattara kayan su zuwa gida, dangi kuwa kowa ya kama gabansa tunda sun san faɗan sa  dole suka barsu. Kamar inda ya faɗa da asbha suka wuce gida,  nan fa ya fara kiran ƴan uwansa da ƴan uwanta, tashi ɗaya aka cika gida, Zainab tayi iya bakin ƙoƙarinta gurin ganin ta mance da ɗiyar tata, sai dai wani lokacin zaka same ta tayi shiru, abin da ya bawa ƴan uwa mamaki bai wuce, saniya da suka gani an shigo da ita ba, kowa sai mamaki yakeyi, wasu na cewa "ashe dama alhji Aliyu yana da kuɗi sosai haka?" Hhh ƴan uwa daga masu kwaso kaya bayan suna zasu tafi, haka dai sukayi ta facaka tunda komai a kwai shi enough, Ranar suna raguna biyu ya yanka irin manya manyan nan, ga ragowar naman saniya da aka yanka, sai da yayi wa Zainab da jaririyar ta, kaya na gani na faɗa, ga gift da aka rarraba Masha Allah. Washe garin suna dangi sun gama komai, suka fara hidimar komawa gida, Ko wanne sai da aka bashi kudin mota, Haka rayuwa taci gaba da tafiya musu cikin daula da kwanciyar hankali, tunda dai ko sun nuna damuwa ƴarsu baza ta sake dawowa ba, A halin yanzu Zainab ta kasance mafi soyuwa a cikin dangi sbda tana da kyau ta sosai ga fara'a da sakin fuska, Watan ta bakwai da aihuwa ya siyar da gidan da suke ciki ya siyi wani anan keffi, danƙareren gida mai kyau da tsari, wanda daga bakin get ma kaɗai zaka bawa wasu labari, masu zuwa ziyara ko basa yanke wa sam, Hassana wace suke kira da Saudart lokacin ta fara wayo, ga dariya ga ta kyakkyawa kamar mahaifiyarta zainab.               ************ Girman ɗan mutum babu wuya, wata kyakkyawar budurwa na hango, tana sanye da doguwar riga ta atamfa, mai adon koren ganye da shuɗi, yanayin ɗinkin da zanen dake jikin atamfar ya amshi jikinta doguwar riga ce buba ɗinkin riga da zani, ita kaɗai take zaune gefe kuma takardu ne wanda zaka tabbatar da bitar karatunta takeyi, Saudart Aliyu kenan, kyakkyawar yarinya mai tashe, duk wani ɗalibi da malami yasan waye Alhji Aliyu, hakan yasa ake kaf kaf da Saudart, har tazo matakin ƙarshe na kammala karatu, bata kula samari a cewar Zainab wacce a yanzu Saudart take kira da momy, su zasu zaɓa mata mijin aure, sai mai nera dan ba zasu siyar da akuya ba,  ta dawo tana ci musu danga. Kasancewarta yarinya mai hankali da jin maganar iyaye, yasa bata tsallake maganarsu ba. Koda ta kammala karatu zata tafi bautar ƙasa, ta sha jan kunne sosai. Koda aiki ya fito mata bata wani yi na'am ba haka ta ci gaba da zaman gida, tunda babu abin da ta nema ta rasa, A sanadin kasuwanci Alhji Aliyu ya haɗu da mahaifin Ma'aruf, lokacin ya zo da su Hajiya mama siyan kayan sallah, daga nan suka ƙalla abota mai ƙarfi, har sukayi musayar numbobi, a zahirin gaskiya mahaifin Ma'aruf ya fi Alhji Aliyu kuɗi, nasan zakuyi mamaki... Mahaifin Ma'aruf. Asalinsu noma da kiwo shi ya karɓesu, ta haka suka tara ɗumbin dukiya tun iyaye da kakanni, tun duniya na kwance suke siyan filaye, iyayensa shi kaɗai suka haifa, asalinsu Fulanin jihar Yola ne, duk shekara suna shirya gagarumin taro nasu na Fulani, wanda ilahirin mutanen ƙauyen suke halarta, a wannan shekarar ma mutanen da suka halarci taron bazasu ƙirgu ba, saboda gabaki ɗaya yankin suka tafi, sai dai Allah mai iko babu wanda ya dawo a raye duk sun mutu, sai mahaifin Ma'aruf shine kawai a raye, shima duk ya ji rauni ta ko ina, Bayan ya warke ya ci gaba da tafiyar da kayan iyayensa, kasancewarsa mutum me gaskiya da amana yasa ya samu al'umma masu ƙaunarsa, alhmdulilah yayi boko dai-dai gwargwado kowa na alfahari dashi, ga taimakon talakawa, ko bayan rashin iyayensa be hana shi ci gaba da noma da kiwo ba, Kasancewar lokacin Ma'aruf yana ƙaramin, shi kaɗai suka haifa, mutum ɗaya ne ya rage a danginsu wato Inna, wacce take ƙauyen Kano, aure ne ya kai ta can, Allah yayiwa mijin nata rasuwa amma ya jima sosai tun bayan da ta haifi Talatu, wannan kenan. After 3days Hajiya ta ji sauƙi sosai, se dai har yanzu ta kasa kiran  momyn Saudart saboda takaici, A ranar Inna ta shirya komawa ƙauye, Hajiya mama da Anty Jamila suka ce mata ta turo musu Talatu suna son ganinta, sai da tayi musu alƙawarin idan ta koma zata sata a mota drivern su ya kawota, kaya da yawa Hajiya mama ta haɗa mata, anty Jamila ma ba'a barta a baya ba gurin zaɓo mata hijabai da sikel ɗin ciki. Ƙarfe 9:am Inna ta bar Abuja, suka kama hanya sai Kano.. Sun sha tafiya sosai saboda sunyi awanni kana cikin hukuncin Ubangiji sai gasu a cikin garin Kano, sun sake yin tafiya mai nisa kafin suka Iso ƙauye. Shugowar motarsu ke da wuya, yara da ƴan mata suka cika gurin, kai kace biki akeyi,  can na hango Talatu sai tuture mutane takeyi, tana cewa hegu ƴan ƙauye, tana rattaba motar, Inna ce ta fito tana murmishi, Talatu ta je da gudu ta rungume ta tana cewa " kun higa uku kudai, to Inna aka kawo a mato se kowa ya watse ƴan cusa kai.. Parking ɗin motar yayi a gindin bishiyar dake ƙofar gidan su Talatu kana ya jingina kansa a jikin kujerar motar ya ciro waya yana dannawa, Suna shiga gida, kafin su kai ga shiga ɗaki kaka tayi sallama, suka amsa, a tsakar gida ta zauna tana yiwa Inna Barka da dawowa, ganin anata fitowa da jakar kaya ya sanya ta cewa "ina kuma ja a kai su?" wallahi su Hajiya ne suka ce Talatu taje tayi musu kwana biyu shine na haɗo mata kaya" "Alhmdllh na gode musu, wallahi dama ta isheni taɓɓ duk wanda ya kwashi wannan yarinyar to ya kwasar wa kansa" Kaka ta ƙare maganar tana riƙe haɓa, "Ni ki dena yimin baki, wataran na ga me tare miki faɗa wallahi" Kaka ta raɓe baki, gami da cewa "kafin ki taremin faɗa kin bani wuya" Inna ko ta kansu bata bi ba, sbda idan sun haɗu sana'arsu kenan da kaka da talatu, Talatu ta ruga gidansu Gudidi, a tskar gida ta sameta tana cin rogo da ƙuli, Gudidi na ganinta ta ɗora ƙafafu a saman kwanon tana wulli wulli da idanu, "keee" Talatu ta faɗa a hankali, Yi mata alama da ta taso tayi, ta taso tazo gurinta, lokacin Ramma tana ɗauki tana sallah, "Ki faɗa min menene ko kinzo sake dukana ne?" "Ke dalla can binni zani hine nace bari inzo in gaya miki, al'kur'an idan zaki ki ɗibo kayanki ki watso min ta katanga sai in kwahe mu wuce kinga mun zamo ƴan binni" Cikin sanɗa taje ta miƙa mata kwanon abincin nata, tace ɓoye maci a mato, Talatu ta juye a ɗankwalinta ta cukuikuye guri guda, ɗan zirine mayafie da taci ɗammara dashi ta ɗaura, har gudidi ta gama tattaro kayanta ta watsa su ta baya Ramma bata sani ba, ashe barci ma takeyi, Gudidi ta kalli ƙaramar ƙanwarta wacce bata wuce shekaru biyar ba, tace "ke Atika ki ce wa Ramma na tafi binni ni da Talatu" Yarinyar sam bata ma gane me Gudidin take nufi ba, ta amsa da "toh" suka wuce, Tunda driver ya san tare da Talatu zai koma ko me ta kawo baya yi mata musu, har kayan Gudidi sai da ta saka a boot, Daga ƙarshe suka raba rogon tare, Talatu ta tura gudidi a boot kana ta rufe, dama kafin Gudidin ta shiga,  Talatu tace mata ta daure, idan suka je can kilihi zasu dinga ci" Talatu ta koma gida tana tsalle, Inna tace "dan Allah talatin ki nutsu ban da yawan magana, Kaka tace "ban da mugunta, hannan ban da  idan ayi maka ka rama" "Wallahi duk wanda ya nuna min yatsa he na karyehi kohi waye" Talatu tai maganar tana tsalle. Horn ɗin da driver yayi ne, yasa su fitowa, Inna ta miƙawa talatu wani babban buhu mai ɗauke da daddawa da kuka da su barkono, Har za a saka a boot, Talatu tace "za'a sace a hanya a bata a hannunta, sbda asirinta zai tonu. Koda driver ya tada mota su Inna suna ta ɗaga masa hannu da yaran dake gurin har suka ɓace wa ganinsu, Sunyi nisa sosai dan sun bar garin Kano, zamu iya cewa sunyi ra bi a tafiyar tasu, Talatu tace "me mato dan Allah ka tsaya zanyi fitsari" Gefen hanya ya samu yayi parking ta fito ya miƙa mata gorar faro "yace gashi" karɓa tayi, bayan tayi fitsarin tana dawowa ya fito shima, cewa take "Gudidi zan buɗe ki yanzu ki dawo cikin mato idan kuma kin mutu hikenan maci naman kaza babu ke" driver yace "Kee! Waye Gudidi? kinada hankali kuwa, a jeji muke da zaki dinga kirawo mana wasu mutane wanda sunan ma babu daɗin ji, daga cikin Boot ya ji ance "me mato ka buɗe ni in fito yasin na gaji da zaman kurkuku" Driver ya zaro idanu tare da matsawa a jikin motar, ya tsorata sosai, tunda a iya saninsa mutum ɗaya ya ɗauko, Talatu tace "kiyi hakuri idan mukayi mihi rabine kunya ze zubemu a nan bari in lallaɓa hi" Ta durƙusa har ƙasa tace "kayiwa darajar gyatumarka ka fito min da ƙawata" A tsorace ya buɗe Boot ɗin sai ga Gudidi tasha kuka ta gaji har da majina, Driver yace "ke ai ke kadai aka ce in ɗauko wannan kuma wacece?...! Sharhin ku shi zai bani damar yi muku typing da yawa. Wanda suke karantawa basa magana karku damu zan tafi hutu kunji?. Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻 Page 21-22 Talatu na matsar ƙwalla tace "ƙawata ce" Kai tsaye ya zagaya ya shiga mota bai sake bi ta kansu ba, koda suka shiga mota basu kulle murfin motar ba, driver ya ce "ke rufe murfin motar mana" Talatu tace "da ƙarfi ko a hankali?" Driver yace "idan kika rufe a hankali kika faɗo mutuwa zakiyi" Ai da sauri Talatu ta buga murfin motar gaaaam!!! , A tsorace ya ambaci sunan Allah, suka ci gaba da tafiya, Suna gaf da shiga Abuja dan har sun wuce Keffi, Gudidi tace "me mato ka dakata yasin rogo ya sa ni gudawa" Wani dogon tsaki yaja mtswww, kafin yace "ni fa na gaji da ɓatamin lokacin da kukeyi, mun kusa isa gida sai kuyi acan. Gudidi sai cije baki take alamun kashi ya matseta, suna hawa gargada ta sake kashin tsuuuuu, wanda ya fara cika gurin da ɗoyi, ba driver ba, hatta Talatu toshe hanci tayi, sai kuma ta dinga sake tusa tana cewa "na higa uku ni gudalle Allah ka sa ban ɓata musu mato ba" Talatu tace "Hegiya ance miki ki bari aje can gidan amma kin ƙi, saboda taurin kai irin naki" "Talatu kinsan idan naci rogo cikina yana lalacewa, yanzun ma wani kahin nakeji" Driver yace "wallahi idan kika sake yin kashi zan sauke ku duka" Tsit sukayi babu wanda yayi magana, sbda sunga babu wasa a tattare dashi.    Zaman ta a gidansu ya fi mata kwanciyar hankali a bisa zamanta a gidan Ma'aruf, satin ta ɗaya amma ta fara murmurewa, abin mamaki har yanzu momy ba ta sanarwa da Dady Saudert ta dawo ba, Sai da suka kwashe one month a can kafin Dady ya biyo jirgi ya dawo, ya bar Anam acan kasancewar tana karatu ne, Wacece Anam?, Anam ƙanwar Saudart ce, shakarunta 18yrs a duniya, Dady ya ɗora buri a kanta, sbda ita ce alkawarin su na ƙarshe da oga akan itama ze kai ta can wato ya bar musu,kamar inda ya bada ƴar uwar Saudart. Girke-girke momy ta shirya masa masu rai da lafiya, ita da ƴan aikinta biyu da Saudart suke ta ƙoƙarin girkin, 5:pm driver ya ɗauko Dady daga airport zuwa gidansu, Momy Saudart, duk sun ci kwalliya sunyi kyau sosai suna jiran shigowarsa, sallamar Dady ne ya karaɗe parlon, Saudart ta miƙe da gudu tana oyoyo dady, bubbuga bayanta ya ɗan yi kai kace wata baby kafin ta koma ta zauna tana murna, ya buɗe hannayensa ma me momy ta taho ya rungumeta, suna sakarwa junansu murmishi, Bayan ya zauna aka kawo masa abinci saman table, sbda a ranar da ya dawo baya zuwa dinning cin abinci, farfesun naman rago ne da tuwon shinkafa miyar egusi sai lemon abarba da kankana wanda aka zuba masa peakmilk, sai da Dady ya cika cikinsa kafin ya wuce bedroom ɗinsa, acan ya samu momy tana ƙoƙarin fito masa da kayan da zai sa, ta baya ya rungumeta tare da cewa "Hajiya Zee meye sirrin komai nawa yana sake haɓɓaka" cike da so da ƙauna ta juyo tare da kwantar da kanta a faffaɗan ƙirjinsa, gami da shafo gashin gemunsa wanda ya fara zama fari da baƙi sbda ya fara manyanta, Habiby any time kana sake zamowa kamar saurayi" Cikin shauƙin so ya wani zagaya da hannayensa zuwa wuyanta kafin yakai bakinsa kumatunta ya sakar mata hot kiss, kafin Dady ya shiga wanka an sha love fa. A tare da momy suka shiga wankan sbda wannan umarninsa ne, idan har yana gari tare suke wanka, bayan ya fito yana tsane jiki, momy ma ta fito ɗaure da towel milk color, Habiby yau  zanje anguwa wata ƙawata ta aihu walhi yau 4days ko zuwa banyi ba" Momy na gama rufe baki Dady ya sanya hannunsa a saman lips ɗinta kana yace "shiiii" wannan ranar tawa ce dan haka a bata haƙuri a tura mata da 100k, babu inda momy ta iya dole ta haƙura. Duk wannan maganganun da suke yi a kunnen Saudart, tazo wucewa taji suna magana ita kuma ta tsaya, nikam nace Saudart ki rufawa kanki asiri, jin shiru yasa ta bar gurin ta wuce bedroom ɗinta, fashewa da kuka tayi yayinda ta tuno soyayyar da suka kwasa ita da Ma'aruf, daga ƙarshe ta juye ta koma ƙiyayya mai muni. Lokacin da aka fara kiraye-kirayen sallahar magriba, Dady ya fito sanye da jallabiya, zai wuce ya kalli Saudart kafin yace "daughter yaushe kikazo?" fashewa da kuka tayi kana ta miƙe ta bar gurin da gudu, wucewa yayi masallaci sbda idan ya koma ciki yana iya rasa sallah. Lokacin da su Talatu suka iso Abuja ana kiran sallahar isha'i, saboda tsayuwar da suka dinga sa driver yayi, Tunda suka doso bakin get Gudidi take ƙwalalo idanu ita da talatu, koda aka buɗe get ɗin bayan yayi horn sakin baki sukayi, a parking space ya ajiye motar kana ya zare key ya fito suna gaisawa da mai gadi, Boot ya buɗe kana ya firfito musu da kaya ya wuce dashi side na su Hajiya mama, suma bayansa suka bi . Hajiya mama na ganin driver ta hau washe haƙora ita a dole yarinyarta tazo, duk da ganinsu su biyu be sa ta ɓata ranta ba, sai ma rungumesu da tayi, tace a shigar dasu ciki suyi wanka sai suci abinci, driver yace "Hajiya har da kashi fa a mota, Talatu tace "to me tonon silili anji ai he ka wuce ko?" Hajiya tayi dariya ta shiga ciki. Sai da sukayi wanka suka sauya kaya, wata koɗaɗɗiyar atamfa Talatu tasa, ita kuma gudidi zani daban riga da ban ɗankwali daban haka ta saka, ga wata kwalliya da sukayi iri ɗaya, sun lafka janbaki ja a leɓensu anyi jagira da koren pencil, Koda suka fito ƴan aikin gimtse dariyarsu sukayi, sbda suma dai a gidan aka wayar dasu, a parlo suka zauna yayinda Hajiya ta sanya a kawo musu farfesun naman kaza, da soyayyen dankalin turawa da kunun gyaɗa, sai ruwan gora a gefe, Talatu ta kwaso kulolin duka gabanta, kafin tace "Gudidi bari kiga idan bamu raba shi ba, ƙur'ani zasu ce mana ƴan ƙauye, Talatin ta yago cinyar kaza takai baki, tana cewa "ungo wuya da gurin ɗuwawu kinsan bana cin su" Gudidi tace "kai Talatu me makon ki raba mana tare hine zaki nuna min waraki?" Murguɗa mata baki tayi, yayin da take sake yago naman kana tace "tausaya miki fa nayi hi yasa nace kizo mu tafi, idan ba zaki ci ba to hikenan cinye wannan na kwanon dan ban san meye ba, ga dukkan alamu zai iya tsurar da mutum" Gudidi ta karɓi wuyan kazar da kwankwaso ta koma gefe, dama a saman Capet suke zaune, ta buɗe kular dankalin turawar da aka soya da ƙwai, ashe har da dambun nama a gefe, ko gayawa talatu batayi ba ta dinga ci hannu baka hannu ƙwarya, bata cinye na bakinta take sa wani, sallamar da Ma'aruf yayi ne yasa Talatu da gudidi suka juya a tare....! Idan ana comments in sauya taku idan ba'ayi muci gaba da tafiya a haka, idan na gaji in dena posting Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻      Mom Islam Page 23-24 Sanye yake da blue jeans da t-shirt milk color, fuskarsa tana ɗauke da annuri, hannunsa na riƙe da wayarsa yayinda ya tsunsa suka kasance da tsadaddun zobuna masu kyau, ko da yaga babu kowa a parlo ya tsaya bai ƙarisa ciki ba, ƙare wa su Talatu kallo yakeyi, yayin da suma shi ɗin suke kallo, Talatu ta wani ƙwalalo masa idanunta, Gudidi na suɗe hannu tace "Talatu idanunki sun gano miki abinda na gani kuwa?" A hankali tace "wa Gudidi, zo ki dangwali romo muyi kamar zamu wuce ta gabansa se mu hyafa mai" Kamar inda Talatu ta tsara haka sukayi, kafin zuwan su yana ta, ƙare musu kallo sbda bai taɓa ganin irinsu a gidansu ba, yayi nisa da tunani ya ji sun ruga waje da gudu suna dariya, sai yanzu ma ya gani wa shi suke yiwa dariyar, ashe ɓata masa jiki sukayi, Cikin zafin zuciya ya kalli kulolin da suka ci abincin kafin yace "su waye waɗannan kamar ba mutane ba?" Kai tsaye ya wuce room ɗin Hajiya mama, ya sameta tana shafa mai, kasancewar ta fito daga wanka, "Hajiya su waye a parlo kamar mahaukata?" "Mahaukata fa kace Ma'aruf?" "Yarinyar yayar mahaifinka ce" waro idanu yayi cike da wulaƙanci kafin yace "gaskiya Hajiya suyi gaggawar barin gidannan" Inda yai maganar ta gane Bama shawara yake bata ba, umarni yake bata, "Ma'aruf  ka nutsu kasan me kake yi, yarinyar nan da ka ga tazo zama daram a gidannan babu inda zata je" "Yara dai, Hajiya ki daina cewa yarinya ai su biyu na gani kuma wallahi da su da mahaukata duk tafiyar su ɗaya, Hajiya ki duba rigata ki ga wulaƙancin da sukai min" Yai maganar yana zuba hannayensa cikin aljihu rai a ɓace. Ɗayar ƙawarta ce tare suka zo ɗazu, Beyi abin da ya kawo shi ba ya fice, sbda haushi da takaici, a rayuwarsa ya tsani ƴan ƙauye. Rai a ɓace ya fito daga side na Hajiya yana ƙwalawa anty Jamila kira Hajiya tace ta fita har yanzu bata dawoba" Yanke shawarar ya fice a gidan yayi, ya fito parlo kafin ya buɗe, ƙofa yaji an cakumeshi tana cewa "yasin na kamaki kuma mintsini sittin zanyi  miki" Idanunta a ɗaure take maganar. Ƙare mata kallo yayi up and down, kafin ya fara kiciniyar fincike hannunta a jikinsa, cikin ƙyanƙyami yake ƙwace hannun nata, har ga Allah bata san ba gudidi ta kama ba, ita kuma gudidi tana can corridor tana jiran Talatu ta kira ta, abin ya matukar bashi mamaki wai namiji kamar shi ya kasa cire hannun talatu a jikinsa? meye hakan yake nufi?" wani gigitaccen mari ya zabga mata kafin yace "ba kisan wa kika riƙe ba ko?" Ya ƙara da cewa "wawuya ƙazama me warin awaki" Jin shigar marin tayi har cikin ƙwaƙwalwar ta, lokaci ɗaya taji zafin na shigarta sosai, tai saurin cire ɗankwalin da ta ɗaure idanun nata, buɗe idonta ke da wuya ta ɗora su a na Ma'aruf, hannunta a saman kumatunta tana sosa gurin tace "me nayi maga mugu kawai, na ɗauka ma Gudidi ce ashe Garba ne" Tai maganar tana murguɗa baki, hannunsa yakai bakinta ya ɗanne sai da taji zafi sosai ta ruga da gudu idanunta sun cika da hawaye tace "mugu basamude" Babu hali ya bita sbda sai ta rai nashi haka dai ya fice a gidan zuciyarsa babu daɗi. Kai tsaye gidansa ya wuce, bayan an buɗe masa ya shiga, kai tsaye bedroom ɗinsa ya wuce,  kallon kansa yayi a mirror kafin ya ja dogon tsaki mtswww, sai kuma ya hau ɓaɓɓalle bottoms ɗin rigar, lokaci ɗaya faffaɗan ƙirjinsa ya baiyyana, wanda ke ɗauke da kwantaccen gashi baƙi gunin birgewa, gashin yayi lufff kai kace an tace shi, Har yanzu yana cikin ɓacin rai, ya zauna saman bed ko me yake tunani oho, ya ciro wayarsa ya fara gwada number anty Jamila, ringing ɗaya zuwa uku ta ɗaga, cikin katseta a maganar da takeyi yace " Anty kina da labarin mahaukatan da suka zo gidan Hajiya kuwa?" Anty Jamila ta zaro idanu kafin tace "shine babu wanda ya kirani, Ma'aruf yace "dan girman Allah ko sun zo yin kwana biyu ne ki fitar dasu anty naje rai na a ɓace na dawo gida. Sallama sukayi ya ajiye wayar, sai yanzu hankalinsa ya kwanta a tunaninsa Anty Jamila bata da masaniyar zuwan su Talatu. A gurguje ta koma gida hankali a tashe, tun daga harabar gidan take ƙwalawa drivers da mai gadi da ƴan aiki kira, da gudu suka taho dukkansu suka durƙusa a gabanta, cikin zafin rai da ɗaga murya tace "waye ya bari mahaukata suka shigo gidannan?" A ƙalla ƴan aikin gidan zasu kai goma, kuma ko wanne a wata ana biyansa albashi mai tsoka. Ƴan matan da suke aiki da mai bawa flowers ruwa da mai gadi da ɗan aikan gidan da sauran ma'aikatan suka rantse da Allah basu ma ga mahaukata ba" Anty Jamila ta ɗibi sauri sai cikin gida, tana shiga tun daga parlo take cewa "Hajiya wai gidannan lafiya kuwa?" Lokacin ma sallahar magriba tayi, ta fito parlo ta samu anty Jamila na ta haɗa gumi tace "lafiya Jamila?" "Au Hajiya lafiya fa kike tambaya ta, ni da aka kirani musamman wai mahaukata sun shigo gidannan" Hajiya ta riƙe haɓɓa kafin tace "injiwa?" "Son mana" Anty Jamila tai maganar tana kallon su talatu da suka fito sunata tsotse ƙashi, Hajiya ta nemi guri ta zauna kana tace"Jamila ki fita harkar Ma'aruf wallahi, ƙanwarsa ya gani ita da ƙawarta shine yake kiransu mahaukata, Hajiya tace "ai su biyu suka zo?" Kafin tai wata magana Talatu tace "ai dama kema anan gidan kike?" Anty Jamila ta gyaɗa mata kai. Bayan anyi sallahar isha'i, Hajiya ta nuna musu ɗakin da zasu dinga kwana, babban ɗaki ne, haɗaɗe kai kace ɗakin amarya, ga gado makeke ga katifa mai laushi, wani tangamemen tv ne a manne jikin bango, yayinda remote ya kasance a cikin drowa dake gefe, acan, tsakiyar ɗakin yana malale da grass Capet, yayinda can saman pop ya kasance akwai wasu ado kusa da ƙwanlantarki a taƙaice dai ɗakin yayi kyau over, Koda suka rufe ƙofa, talatu ta fara jin kashi, ta tashi gudidi da ta fara barci tace "ke tahi ki rakani banɗaki alƙur'an kahi nakeji" cikin barci gudidi tace "unn ke komai kahi Allah hi ƙara ai romon da kika hya ne" "Nidai ba wannan ba ki tahi muje in yaso idan muka dawo sai ki ci gaba" Tana maganar tana tsalle, dole gudidi ta tashi suka murɗa handle na ƙofar toilet ɗin suka shiga, "lalala na higa uku wannan aljannar duniyar haka?" Talatu ta faɗa tana ƙarewa toilet ɗin kallo, "kinsan meye gudidi?" Gudidi tace "a'a amma dai yasin sun cucemu ga guri me sanyi da ni'ima sun wani sa mu cikin ɗumi, " "Ke har na ji kahin ya koma, yanzu dai zo mu kinkimo katifa mu kawota nan" Talatu ta nunawa Gudidi toilet, Yasin bazamu iya ba, kafin mu kinkimo ina jin ƙihi, yauwa ka kofi, ta ɗauko wani cup wanda yake ajiye a can sama dan har da abin ajiye shi, kai idan ka ga cup ɗin kamar ka cinye amma wanka akeyi dashi, babu wani datti a jikinsa sai sheƙi yake, Gudidi ta fara dube duben inda zata samu ruwa, "lahh ga rijiya kuma ga dukkan alamu ruwanta ze yi sanyi sosai" Gudidi ta faɗa tana buɗe p-toilet, dumbulo ruwan tayi kafin ta kurɓa cikin jin daɗin sanyi da ya ratsa ta tace "ahhhh" Talatu ta karɓe cup ɗin tare da ɗibowa itama tasha, har tana wani lumshe idanu, sai kuma ta sake ɗibowa, kowaccensu ta sha ya kai cup biyar biyar, daga nan suka fito bedroom sukayi ta kiciniyar ɗauko katifa tafi ƙarfin su, dole suka hakura suka kwanta, "wayo daɗi Talatu ƴan binni suna morewa wannan katifar kamar lallausan burodin hyagon Lado" Gudidi tai maganar tana bubbuga ƙafafunta, da haka har barci ya ɗauke su. Acan ɓangaren Hajiya suna zaune da Anty Jamila, Hajiya tace "Jamila ina son zumuncin mu yaci gaba da ɗorawa da yaɗuwa ta hanyar haɗa auren Ma'aruf da A'isha" Anty Jamila ta ja gauron numfashi kafin tace "Hajiya wato Hajiya wani hanzari ba gudu ba" Hajiya mama tace "ina jinki" Anty Jamila tace "da farko dai a mayar da ƙawar A'isha daga nan sai mu fara tunanin abubuwan da ya dace muyi mata" "Hakane gaskiya banyi tunanin hakan ba sai yanzu, kinga idan ta ga ita kaɗai ce zata fi kintsuwa, akwai wasu kuɗaɗe da zasu shigo end of this month za'a cire wasu daga ciki ayi mata siyayya, Jamila kinsan abu na gaba wanda nake tunani?" Anty Jamila ta bata amsa da cewa"a'a ,ya za'ayi soyayya ta shiga tsakaninsa da Aisha? kinsan dai halin Ma'aruf miskilanci da jinkai, babbar damuwar ma ya ce yana ƙyanƙyamin ƴan ƙauye" Momy na gama maganar tai tagumi, Cikin kwantar mata da hankali anty Jamila tace "karki damu A'isha ƴa mace cefa, sannan wallahi tallahi sai Ma'aruf ya so A'isha fiye da ko wacce mace, amma kafin hakan ya yiwu sai an sha wuya, Hajiya in ba'a haɗasu aure ba, to bamusan wacce zai jajiɓo mana ba, tunda duk ƴan matan ba zama da shi tsakani da Allah zasuyi ba, saboda dukiyarsa zasu so shi, duk da cewar shi ɗin ba mai kule kulen ƴan mata bane" "Hakane, Jamila amma A'isha zata sha wuya sosai" Hajiya ta faɗa tana gyara pillow ta kwanta, "Hajiya na ɗan lokaci ne, bari Allah ya kai mu gobe insha Allah a kuɗin business ɗin a zan ware mata 50k kafin ragowar su zo" Anty Jamila tai maganar sbda tana son kwantar wa da Hajiya hankali. Fans nasan kuna son ku ji waye anty Jamila ko? Anty Jamila ƙanwa ce ga Hajiya mama, uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, bayan rasuwar mahaifin Ma'aruf ta dawo gidan Hajiya, tana business ɗin kayan kitchen sbda har babban shago ne da ita, shekarunta 37yrs  kafin zuwanta  tayi aure a Niger, mijin ya gudu Mali ya barta, yakai shekaru 7 bai dawo ba, daga ƙarshe ya aiko mata da takardar saki, shine ta dawo gurin Hajiya mama. Asalinsu ƴan Bauchi ne, dalilin haɗuwar Hajiya da mahaifin Ma'aruf, ta fita anguw a yayi tozali da ita, daga nan magana tayi ƙarfi har akayi aure ga Ma'aruf ɗin mu nan na A'isha komai dozin🤣, wannan kenan. Ko da Dady ya dawo daga masallaci ya samu saudart tana zaune saman kujera tana danna waya, "sannu da dawowa Dady" Saudart tayiwa dadyn yayinda take sauke kanta ƙasa, "Yauwa amma lafiya dai na ganki a gida ko?" "Kanta a sunkuye tace "Dady Ma'aruf ya sake..." "What!!! kinsan me kike cewa kuwa?" Kuka ne ya kufce mata ba tare da ta shirya Ba, sbda ita a gurinta abin farin ciki ne, yanzu kam ba ta san kukan me takeyi ba, Dady ya katse ta da cewa "kimin magana, sannan kuma ki tashi driver ya mayar dake gida" "Da gaske takeyi Habiby ba wasa bane, har saki uku yayi mata, wallahi nima nayi yunƙurin ta koma, amma abin ba zai yiwu ba, tunda har da shai da ya bata kaga kuwa magana ta ƙare, nidai ina roƙonka alfarma karka sake ka je ko ka kira iyayensa wannan tashin hankalin ya isa haka, Saudart fa ba wai ta rasa mijin aure bane, Dady yai gyaran murya kafin yace......! Uhm jiya na samu comments na mutum ɗaya idan har kinci karo da godiyar da nayi miki much love, comments da sharhi shine farinciki na. Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA*       🪻🪻🪻      Mom Islam    Page 25-26 "Kinsan komai Zainab ba sai nayi miki dogon bayani ba, duk da muna da tarin arziƙi, ba shine zai hana mu aurar da yarinyar mu ga wanda ya fi mu tarin dukiya ba, wannan shine dalili na" Dady yai maganar rai a ɓace. Rurin da wayarsa tayi ne ya sanya shi miƙewa yana cewa "ba zan zauna in zuba miki idanu ba, kina gama idda zan aurar dake insha Allah " Dady yai maganar yana bi ta gaban Saudart ɗin ya wuce, Cike da tsantsar tausayi momy ta rungume ɗiyar tata tana bubbuga bayanta, kafin tace "daughter ki yi hakuri komai yai tsanani maganinsa Allah, har yanzu dadynku bai fahimceni ba, amma a ganinsa mune ba mu fahimce sa ba, duk soyayyarsa da dukiya ai ya kamata ya kankaro miki mutunci" Dukkansu kuka suke mai cike da tausayi.   A tunanin Hajiya su Talatu sun tashi sunyi sallah, shiyasa bata leƙa su ba, a cewarta su huta sosai, Ƙarfe 9:am time ɗin sun kammala breakfast an jera a dining table, kalolin abinci ne sunkai uku, Dafaffiyar doya da miyar ƙwai sai Potatoes Salad sai Dambun couscous da  sai kuma drinks na Abarba da kwakwa, gabaki ɗaya sun hallara a dining, Hajiya da Anty Jamila da Ma'aruf,  Dafaffiyar doya da miyar ƙwai aka sa masa sai su anty Jamila da suke cin Dambun couscous, Hajiya ta yiwa ƴar aikin magana mai suna Dija tace ta kira mata yaran da suka zo jiya, da sauri Ma'aruf ya miƙe tsaye yana jan t-shirt ɗinsa, kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa yayi, kafin ya bar gurin, ko tsakiyar parlo bai kai ba, sukayi kiciɓis da Talatu ita da Gudidi, be yi aune ba suka wani tafi dashi kiiiii sai ya faɗi saman kujera daɓas, waro ido yayi yana kallonsu, ga mamakinsa sai ya ga suna ta dariya har da nuna sa da hannu kamar sun ga sabon mahaukaci, cike da bala'i ya miƙe sbda ba suyi tsammanin hakan ba, tunda suna ta wasa ne wanda suka saba yi a can garinsu, ya zare belt ɗin wandonsa kana ya shaƙo wuyan Talatu gudidi zata gudu ya sa mata ƙafa ta faɗi, ya shure ta da ƙafa, "ke wace irin daƙiƙiya ce, kinsan waye ni kuwa?" Ya zabga mata lafiyayyen mari wanda yai sanadin ɗaukewar jin ta na ƴan wasu lokuta, sai kuma ta tsala ihu, sbda take mata ƙafa da yayi da cover shoe ɗinsa, ƙarar muryarta da su anty Jamila suka ji ne ya sanya su tasowa a tare ita da Hajiya, har ma da ƴan aikin gidan, sukayo kanta, turus sukayi sbda aika aikan da ma'aruf yayi wa yaran, bakin Talatu sai jini yake, ita kuma gudidi tana riƙe da kai itama tasha mari dan zai kai biyar, Rai a ɓace Hajiya mama ta nemi guri ta zauna kafin tace "last warning Ma'aruf wallahi idan ka sake kuskuren taɓa yarannan Allah sai ranka ya ɓaci, "shikenan daga zuwansu ka sasu a gaba sam baka tunanin zumuncin dake tsakaninku?" "Allah ya kyauta wallahi gara in ƙare rayuwa bani da dangi da dai ace wannan mahaukaciyar itace dangina" Anty Jamila tace "har matarka ma, to ya zakayi idan hakan ya kasance?" Ma'aruf ya tofa mata miyau a fuska kafin yace "tur har abada wallahi da na haƙura da aure dama bani  da niyya" Cikin yanayin ɓaci rai Hajiya mama tace "Jamila ki daina yi masa misali ki rabu dani kawai zan yanke hukunci nan ba da jimawa ba, ko yayi masa dadi ko kar yayi masa babu ruwana" Tunda ya ji Hajiya ta tsomo baki yai tsit sbda ya san a inda yake magana, babu wasa, bai sake magana ba ya fice, Hajiya kam tana rungume da Talatu baki yayi sungumeme, fans a memakon kuyi mata sannu sai kunyi dariya irin sosai ɗinnan 🤣, Rarrashinsu Hajiya da Anty Jamila suke yi su ko sun ware baki suna ci gaba da cewa "mun higa uku me mato yazo ya mayar damu ƙauye rayuwar binni babu riba" ba Hajiya ba, har anty Jamila sai da tayi dariya. Har inda suke zaune ƴan aiki suka kawo musu abinci, aka bubuɗe musu kuloli, a tare suka matsa Talatu tana cewa "idan kinga me nama a ciki gudidi karkici" "Sabo da me, ke da kika sauya kamanni kamar goggon biri, gudidi tayi maganar tana riƙe da ƙafarta kana ta sheƙe da dariya, "Ka ji hegiya ba dan na taimaka miki ba ubanwa ya isa ya sa ki zo wannan tafkeken gidan?" Gudidi tace "a hakan dai gahi kin fini hyan wuya koba komai baki yayi sungumeme" Ta miƙe da faɗa zata daki gudidi, Hajiya ta riƙeta tana bata haƙuri. Suna breakfast ɗin suna faɗa, da gori da haka sai da suka cinye ragowar abincin tass kafin suka ture kulolin, ma'aikatan dai suna ganin ikon Allah, cike da gulma suka bar gurin suka koma part ɗin su. "Dija dame muka fi waɗancan ƙauyawan, mu fa ba dan talauci ba wallahi da baza a ganmu a nan ba, kinsan meye Hajjo?" "A'a" Hajjo tace, Dija tace "ina wannan yarinyar fara mai dogon hanci wacce alhji ya kumbura wa baki" "Naji dai Dija ci gaba ina jinki, ya akayi?" Dija ta taɓe baki kafin tace "wai ita Hajiya take so ta auri Alhji" "Kai kai kai, "Dija kunnuwanki basu jiyo miki dai-dai ba, saboda babu inda za'ayi kamar Alhaji ya auri wannan yarinyar, da idan tayi kwalliya kamar ka gudu" Hajjo tai maganar tana girgiza kai. "To shikenan Hajjo dama ni idan na kawo miki magana baki cika amincewa da magana ta ba" Dija ta faɗa tana ci gaba da tafiya. "Haba Dija ai abin ne banbara kwai babu daɗin ji" Daga nan suka kawar da maganar ta hanyar ci gaba da hira. Bayan su Hajiya sun koma ɗaki, Gudidi ta kalli Talatu kafin tace "kinga basu kawo mana ruwa ba, ruwan nasu ma marar garɗi kizo kawai muje wannan ɗakin mu hya me sanyi" "Riƙe min hannu in tahi wannan mai ƙirar samudawan sai mun ɗauki fansa a kansa, duk da dai gyatumansa sunyi masa faɗa amma ni naso a dalla masa mari yasin" suka wuce room ɗin su suna ɗingishi, Yau ma kamar jiya, suka shiga toilet ɗin, wani sanyin ƙamshi ne ya ziyarci hancinsu, sbda a rana sau biyu ƴan aiki suke gyara ko ina,  "yasin Gudidi duk inda za'ayi yau anan zamu kwana ni ko a ƙasa ma zan kwana" Gudidi na ɗingishi tace "uhm ni ƙafa ce ta dameni da zugi ɗiban ruwan dan Allah" Talatu ta ɗauki cup ɗin ta ɗibo mata ruwan tasha tace "ahhh sanyi me sanyaya zuciya, ina tunanin komawa ƙauye ina tunanin barin wannan lagwadar daɗin" Gudidi tace "hikenan da ina so in samo mana wata hyawara in kin amince?" Talatu tace "ina jinki" "Kizo mu je tsakar gidannan muga me akeyi muma fa ya kamata mu fara aiki ana biyan mu, mun zauna kara zube kamar wasu malalata" Talatu ta waro idanu kafin tace "ke ai bazasu barmu muyi komai ba, sai dai muje wani gidan mu nemi aiki kinga hikenan asirinmu a rufe" Gudidi ta kurɓi ruwan p-toilet tare da yin farrr da idanu tace "zan ɗura ruwannan a gora na rantse in samu na hya in zamu fita neman aiki" Talatu tace"to bari dai mu samu lafiya se mu fara zuwa" ƘAUYE Bayan tafiyar su Talatu. Ke ina Gudidi taci da ƙohi bata kwahe kayan wanke-wanken tayi ba, yarinyar dake zaune ta fara gyangyaɗi tsabar ƙoshi tace "Gudidi fa ta bi Talatu Binni tace in gaya miki " Tabaiyye ta zaro idanu tare da riƙe baki, mayafin ta dake rataye jikin igiyar shanya ta ɗauka fuuu sai gidan Inna, tana tafe tana sababi har ta iso gidan Inna, tun daga can zaure take kwaɗa sallama, lokacin kaka na zaune a tsakar gida, suka amsa da "wa'alaikumussalam, hannu da zuwa Tabaiyye " "Hmm kafin dai in amsa muku jama'a kuyi hakuri wai da gaske ne Gudidi ta bi Talatu binni?" Cike da mamaki suke kallonta wanda a iya saninsu Talatu ita kaɗai ce a cikin mota, Inna tace"any kuwa? gaskiya bata bi ta ba" "Tabaiyye tace ƙanwarta ce ta tabbatar min da haka hiyasa nazo kai tsaye" Sosai maganar Tabaiyye  ta basu mamaki, kaka tace "abinda ya kamata ke Inna ki tahi ki je gurin mai hyago ki ari Salular sa ki kirawo Jamila ko Hajiyar ki tambsyesu " Inna tace "to ai kuwa maganin kokwanto" Tabaiyye ta zabga uban tagumi gami da cewa "na saro rogo har na ɗubu da ɗari biyar amma tsiyar da ƴar nan zatai min kenan Inna tace "kiyi hakuri  bari inje in duba" Inna ta lulluɓa zani ta fice, kai tsaye gurin mai shago ta nufa, bayan sun gaisa tace "dan Allah idan salularka da kuɗi ka yiwa Hajiya flahin ta kira zan tambayeta ne" Yana yin flashin sai ga kiran Hajiya, bayan sun gaisa, Inna ta tambayi Hajiya, Gudidi ta biyo Talatu ne?" Hajiya tace "eh ta biyo ta" Inna tace "gahi nan zata ɗaga mana hankali dan Allah idan da hali ta dawo tun kafin mahaifinta ya sani" Hajiya tace "munyi shawarar hakan insha Allah gobe driver ze kawota yanzu kam dare yayi, Kasancewar lokacin da Inna tayi kiran har sun fara barci, anty Jamila kam tuni tayi barci. Inna ta mika masa wayar kana tayi masa godiya, Tana komawa gida Tabaiyye ta miƙe tsaye kai kace ance gudidin ta mutu, tare da dafe ƙirji tace "ya akayi Inna?" Inna tace "hamm walhi tare suka tafi, amma gobe insha Allah me mato zai kawota" Tabaiyye tace "alhmdulilah barin koma gida in san ƙaryar da zanyiwa babanta" Babu wanda ya tanka mata ta fice. WASHE GARI. Lokacin da Ma'aruf yai musu wannan dukan ashe Hajiya na ayyyana inda zata tari Gudidi da maganar tafiya, gashi kuma ya take mata ƙafa, duk da dai bata ji ciwo ba, Umarni ne na Hajiya duk wani baƙo da yazo za a kai masa ruwan wanka ƙarfe 12:am idan har baka son yi da safe, Cikin bin umarnin Hajiya Dija ta shiga ɗakin su Talatu ta samesu suna ta wasa suna ihu, haushi ma suka bata cikin yatsina baki kai kace ƴar wani mai muƙamin ta wuce toilet, ko da ta shiga suka bita da sauri, Talatu tace "karki kuskura ki kwahe mana ruwan daɗi dan wallahi bazamu barki ba, sai kinyi kuka" she's 18yrs Dija, su kuma 12yrs ta wani yi musu kallon tara saura kafin ta watsar ta kutsa kai cikin toilet ɗin, suma shiga sukayi, "ahe ma ba nan ta nufo ba" Cewar Gudidi, Talatu taje da gudu ta zauna a saman p-toilet tana turo kumburarren bakinta, da yake Dija bata fahimci abinda suke nufi ba, tai ficewarta, har ta kai tsakiya sai kuma ta tsaya, tace "ga ruwan wanka nan kuyi" Tana fita, Talatu tace "yasin bazamu yi ba, se kace wasu agwagi mtswww Hegiya kawai" ta tashi tsaye tana kwaikwayon tafiyar Dija tare da yanayin maganarta, suka sheƙe da dariya. Saboda kar ace ba suyi wankan ba, suka ɗauraye jikinsu, sabulun kam yasha gurza a cewarsu ƙanshinsa yayi yawa, gara yayi ya ƙare. Ko da suka fito daga wanka kayan da suka cire shi suka mayar,  suka lamɓaya mai suka fito. Ƙarfe 1:pm Hajiya ta fito da wata babbar jaka, wacce ke ɗauke da kayan abinci da kayan sawa sababbi masu tsada, Hajiya taje parlo gurin Gudidi da ke gaban TV kamar za ta shige ciki tace "ƴata kiyi hakuri mamarki ta kira jiya wai ki koma gida, ga wannan kayan ki tafi dasu" Gudidi ta kalli Talatu suka zaro idanu, Gudidi ta tsandara ihu tana cewa "yasin ni bazan koma ƙauye ba, bazan iya zama a can ba yanzu na higa uku wayo Tabaiyye zata cuceni waye daɗin binni wayo ruwan sanyi mai garɗi" Haƙuri Hajiya ke bata amma ina sai surutai takeyi sam bata ma ganewa, anty Jamila da ke fitowa yanzu hannunta rike da waya, ta ƙwalawa driver kira, yazo cikin ladabi ya durƙusa, tace masa ya sa kayan a mota, tunda Talatu taga da gaske ne, ta marairaice murya tace "gudidi kiyi hakuri zan dinga tara miki ruwan daɗin a jarka idan ya ɓubɓugo" koda suka iso harabar gidan da ƙyar ta shiga mota sai kuka takeyi, driver ya fice bayan an buɗe masa get suka nufi hanyar ƙauye...! Masha Allah naga comments naji daɗi ina fata zan dinga samu any time, Dan Allah kuyi haƙuri zan dinga hutawa Asabar da lahadi, saboda aiyukan gida, sannan inaso in ƙara muku yawan typing kamar read more shida inda zaku ji daɗin karatu, kunga komai sai da lokaci, yanzu dai insha Allah Monday zaku jini nayi muku alkawarin sa ku farinciki insha Allah. Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA*       🪻🪻🪻     Mom Islam Page27-28 Bayan tafiyar Gudidi, Talatu ta shige ɗakinta da gudu tare da rushewa da marayan kuka gami da kurma ihu tana shure-shuren ƙafafu, lokaci ɗaya zazzaɓi mai zafi ya kamata, bakinta ya fara karkarwa, ta haɗe guri ɗaya idanunta kuwa sunyi jajir kamar garwashi Daƙyar take buɗe su. Acan ɓangaren su Hajiya da anty Jamila, tun bayan tafiyar su Gudidi suka fita anguwa har misalin ƙarfe 5:pm basu dawo ba, Gidan tsit ba kajin ƙarar komai sai na TV,  a tare suka fito parlo suna sheƙewa da dariya, Dija tace "Hajjo nifa kinsan bakina baya shiru, yau ina waɗannan yaran masu kama da sheɗanu" Sai kuma ta rufe baki, Hajjo ta zaro ido kafin tace "Dija ki rufa mana asiri, dan ma Allah ya taimakemu su Hajiya sun fice, zo muje muga ƙwaƙwaf kodai an tafi da su ne?" Cikin sanɗa suke tafiya har suka iso part ɗin Talatu, a hankali suka murɗa handle na ƙofar, hangota sukayi ta kwanta saman Capet sai juyi takeyi, duk iya shegensu sai da ta basu tausayi, dukkansu sun tsorata, sbda a yanayin da suka ganta sai ka rantse idan ka matsa daga gurin zaka nemeta ka rasa. A ƙa'idar gidan duk wani wanda bashi da lafiya, muddin babu kowa a gidan, Hajiya tace ayi gaggawar sanar da ita tun kafin ta dawo, gudun kar suyi leifi yasa Dija dawowa parlo ta ɗauki wayar tafi da gidanka ta kira Hajiya, bayan ta ɗaga kiran ta sanar mata da cewa, ɗaya daga cikin wadannan yaran babu lafiya farar me dogon baki, Daga can ɓangaren Hajiya take sanarwa da Anty Jamila, kai tsaye anty Jamila tace "Hajiya me zai hana ki kira son ki gaya masa ya kai ta Hospital kafin mu dawo, amma fa sai kinyi masa gargaɗi. Number Ma'aruf Hajiya ta kira, sanin muhimmanci mai kiran ya sa shi ɗauka haɗe da sallama, bayan ya gaisheta ta amsa tace "kaje gida ka ɗauki A'isha babu lafiya yanzu yanzu fa, kuma idan har na samu labarin ka wulakanta ta sai ma saɓa maka" "Toh" Kawai yace, tunda ya tabbatar da umarni ta bashi. Kwance yake a saman Royal bed wanda aka lulluɓe shi da farin bedsheet, ya rungume pillow idanunsa a lumshe yake, yayinda ƙa'idojin Hajiya suka sake dawo masa, "wai kar ya kuskura ya wulakanta ta, Juyi ya dingayi a saman bed ɗin gami da tunanin shikam ya zai yi da rayuwarsa, ko dai ya kira drivern gidan ya ce masa ya kai ta ne?, Yana tsaka da tunani wayarsa ta sake ringing a karo na biyu, kafin ya ɗaga sai da kiran ya katse kafin ya ɗaga, kafin yai wata magana Hajiya tace "na kira su Dija sunce babu wanda ya shigo, me kake nufi ne Ma'aruf?" "Babu abinda nake nufi Hajiya wanka na shiga" Tabbas kalaman kare kanta da ya gaya mata, sunyi tasiri a zuciyarta, dole badan ya so ba, ya sanya ƙananun kaya wanda suka zamo a koda yaushe su yake da muradin sa wa, Kai tsaye Lokar da yake ajiye key ɗin motocinsa ya nufa, key ɗin MBW BJ 2020Silver ya ɗauko, kafin yaje gaban mirror ya ƙarewa fuskarsa kallo, lokaci ɗaya ya haɗe rai, bayan ya kammala shiryawa ya fito cikin takun isa da ƙasaita, kai tsaye gidan su Hajiya ya nufa, bayan yayi horn mai gadi ya buɗe masa ya kutsa kai ciki, parking yayi a harabar gidan ya danna horn, mai gadi ya taho da gudu ya durƙusa a gaban Ma'aruf yana cewa "Allah ya taimakeka ubangidana, babu wasa ko alamun zai yi murmishi, "ka shiga ciki ka ce ƴar ƙauyen nan ta fito ina jiranta" Cikin bin umarnin Ma'aruf yai sallama, Dija da Hajjo ne a parlo suna zaune saman Capet suna kallo, "wai yarinyar da tazo daga ƙauye ta fito inji Alhaji" Mai gadi yai maganar ya juyawa ba tare da ya jira amsar su ba. "Mtswww walhi Hajjo ina jin haushin yarinyar nan, ki ga wani har fita zai yi da ita" Hajjo ta kama baki, kafin tace "wato kin mance bata da lafiya ko ko ba ke kika kira waya ba?, Kuma Hajiya ta kira ɗazu kin ce be shigo ba" "Mtsw" Dija ta sake jan tsaki a karo na biyu, "Hmm in tayi wari ma ji, nidai na fara hasashen kina son Alhji ne, wanda idan mafarki kikeyi sai kin farka, saboda bazai taɓa sonki ba,  tunda kaf ƴan matan duniyar nan ya kasa ware ko da ɗaya ce ya ce yana so har yanzu, kinsan kuwa duk wacce aka sake aka haɗata dashi sai ta sha baƙar wuya, miskili ga jinkai da iko uwa uba sarauta kamar wani sarki bayan haka ga tarin dukiya, ke ni kaf anguwannin nan ban taɓa jin mai kuɗi irin nasu ba" "Ke Hajjo ki tsaya a matsayinki, idan ma nace ina sonsa ai halak ne, kuma naga zan iya ne ehe " Dija tai maganar cike da ƙufula, Allah ya baki haƙuri, Hajjo ta faɗa tana miƙewa zuwa kiran Talatu, a bakin ƙofa ta sameta sai juyi takeyi, tabbas abin a tausaya mata ne, duba da irin galabaitar da tayi sosai, har ya kai ga magana ma ta gagareta ga kuma rashin ƙarfin jiki ta kasa tsayuwa, rungumeta Hajjo tayi suka fito parlo, Dija ta sake jan dogon tsaki mtswww, a karo na uku, Ita dai Hajjo ko saurararta ba tayi ba, suka wuce inda motar Ma'aruf take, sai lokacin ta ɗan buɗe ƙwayar idanunta ta ɗora su a nashi, kallon tara saura kwata yayi mata, kafin yace "in zauna jiranku ne?" Hajjo tace "a'a alhji ayi haƙuri" ta buɗe motar ta sanyata kana ta rufe murfin motar, a ɗari ya figi motar, already yace wa driver ya buɗe masa get tun kafin isowarsu, tuƙi yake kamar zai tashi sama inda ita kuma Talatu, bata ma san yanayi ba, sbda barci da ya ɗauketa, Kai tsaye Hospital ɗin da Hajiya mama ta kwanta nan ya kaita, ko da suka shigo Hospital ɗin ko ta kanta beyi ba, ya fito dama fuskarsa na sanye da Black I glass wanda baka ganin ƙwayar idonsa, nurses na ganinsa suka taresa kasancewar sunsan waye shi, tunda tun mahaifinsa na raye suke zuwa Hospital ɗin, "akwai marar lafiya a backside" abinda ya faɗa kenan. Kai tsaye ya wuce office na doctor wanda aka sauya bayan rashin lafiyar Hajiya, doctorn ya kasance babban abokinsa ne, Sau ɗaya yayi nocking, daga cikin room ɗin doctor Habib yace masa "Yes come in" Bakinsa ɗauke da sallama ya shigo, Doctor Habib yai murmishi kafin yace "mutumina yau kai ne?" Sai da Ma'aruf ya zauna kafin yace "ka wani hakimce a kujera kamar mutumin kirki" Habib ya bigi ƙafarsa ta ƙasan table yace "da mutumin meye?" Suka sheƙe da dariya, Oh ashe dai Ma'aruf yana dariya?, sosai fa dariyar tayi masa kyau har point na kumatunsa na loɓawa, niko nace "wow, gaskiya har yanzu mun kasa ƙarasa kwatancen kyau da izza irin ta Ma'aruf, Bayan su gaisa doctor Habib yake tambayarsa ya Fadwa?" Doctor Habib yace "tana lpy baka san tayi nauyi ba ko?" Sai kuma ya jefo masa tambaya, "Ina amarya fa?" Lokaci ɗaya Ma'aruf ya nemi walwalarsa ya rasa, sbda kiran Saudart da doctor Habib yayi, "wani abin ne ya faru?" Doctor Habib ya sake jefo masa tambaya" Kaga abokina mubar wannan maganar marar lafiya na kawo.." Doctor yace suje ya ganta, Babu musu suka fito a office ɗin, "wane room aka shigar da ita?" "Room5" Ma'aruf ya faɗa a takaice, "To muje" "Sai dai kai kaje, zan leƙo ta window" Ma'aruf yai maganar ko a jikinsa. A tare suka nufo ƙofar ɗakin da aka shigar da Talatu, sai dai shi gogan fur ya ƙi shiga, kamar inda ya faɗa ta window ya leƙa ta, shi tun da suka zo gidansu be taɓa ƙare mata kallo irin na yau ba, ita ɗin fara ce amma ba can ba, zamu iya kiranta da wankan tarwaɗa, color na skin ɗin ta mai kyau, ni mom Islam nice nace muku me kyau fa😂 ba Ma'aruf ba. Ta da dogon hanci bakinta yana da ɗan girma ba irin mai sa muni ba, gashin girarta yayi luff baƙi wuluk, tanada faɗin fuska, tana da manyan idanu, uhm in taƙaice muku dai, Talatu kyakkyawa ce, Tsaki yaja mtswww, wanda yasa Doctor Habib waigowa yana kallonsa, sai kuma ya ci gaba da ƴan gwaje-gwajen da yake yi mata, Kafin ya sake juyowa ya ga babu Ma'aruf babu alamarsa, Sallamar su anty Jamila da hajiya ne ya sanya doctor Habib ɗagowa daga ƴan rubuce-rubucen da yakeyi, da sauri Hajiya mama ta ƙaraso tana cewa "sannu A'isha ya jikin dai?" Yanzu ne ma take ta ƙoƙarin buɗe idanuwanta, cikin murya irin ta marasa lafiya tace "da sauƙi" Anty Jamila ta kamo hannunta tana ɗan mammatsawa a hankali, Bayan sun gaisa da doctor Habib ya miƙe tare da cewa "insha Allah zata warware zazzaɓin cizon sauro ne yayi mata chronic insha Allah zata samu lafiya" Suka amsa da cewa "Allah ya yarda" A hankali anty Jamila ta tallafo kanta da pillow kafin ta ɗauko ɗaya daga cikin ledoji biyu da suka ciko da kayan ciye-ciye, ayaba ta ɓare cikin sigarallashi tace "A'isha ki daure ki ci ko kaɗan ne" Ba dan tana jin daɗin ba kinta ba, ta karɓa daƙyar ta haɗiye gami da runtse idanunta, Hajiya tace "a barta haka  tunda bata so, A'isha ki fadi duk abinda kikaso a dafa miki zan kira ƴan aiki sai suyi miki" in cold voice tace "ruwan daɗi zan hya" Hajiya ta buɗe leda ta fito da faro water ta buɗe murfin kafin tace "ga shi" a shagwaɓe tace "ai ba hi bane wannan" Anty Jamila tace "wane iri ne?" "Na cikin rijiyar banɗaki" Tai maganar irin ko a jikintan nan dan a iya tunaninta rijiya ne. Hajiya ta zaro idanu kafin tace "innalillahi wa inna ilahir raji'un" A'isha ruwan banɗaki kike sha?" Talatu ta juyar da kai tare da turo dogon bakinta, Dole Hajiya ta tilasta mata tasha ruwan kaɗan. Wayarta ta ciro a bag ɗinta kana ta fara lalubar number Ma'aruf, Yana picking tace "wa ka bari da marar lafiyar?" "Barci takeyi shi yasa na fito waje" Ma'aruf yai maganar sbda yana son ya kare kansa, "To mun zo gamu a hospital ɗin" Hamdala yayi a cikin ransa, a fili yace "toh barin je sallah dan har an shiga ma" Har akayi sallar isha'i Ma'aruf bai dawo ba, Hajjo ce ta kawo musu abinci, Dija kam tace ta tsani Talatu, A takaice dai Hajiya ta koma gida anty Jamila ce ta kwana da Talatu a hospital,... Please my lovely fans ayi haƙuri ba haka naso ba, walhi zazzaɓi nake tun ranar Saturday da safe, har yanzu jikina babu ƙarfi, ban samu na cika muku alkawari ba, am so sorry please I need your prayers. meson shiga group ɗin da nake posting littafin NA KASA JUREWA kuyi saving numberta kuyimin magana da done zanyi adding ɗinku. 08141799224 Mom Islam *NA KASA JUREWA*       🪻🪻🪻     Mom Islam Inayiwa ɗaukacin al'auma barkanmu da Sallah Allah ya sa muga ta haɗu, ya Ubangiji ka yafe mana zunuban mu, ya Allah ka kyautata farkonmu da ƙarshe = Page 29-30 Ko da doctor ya shigo ɗakin da aka kwantar da Talatu, ya ga jikin nata alhmdulilah, ya ce "anty Jamila ta biyo shi office,  bayan ta biyo shi, yayi mata ƴan bayanai kafin ya rubuta mata magunguna taje pharmacy ta siya, a take a gurin tayi masa transfer na kuɗin asibitin, bayan ta koma suka tattara kayan su ta kirawo driver ya zo ya ɗauke su suka koma gida, time ɗin Hajiya ta fito a wanka tana shiryawa zuwa Hospital ɗin sai ga su sun dawo. Sosai ta samu kulawa a gurin Hajiya da anty Jamila kai kace ƴar da suka haifa a cikinsu, Washe gari, kwana biyar da faruwar rashin lafiyarta. Hajiya ce zaune a parlo  ko wanne da waya a hannunsa, kasancewar suna yin online business, ajiye wayar Hajiya tayi, kafin ta kai dubanta ga anty Jamila, kana tace "Jamila kinga dai Ma'aruf ya ƙauracewa gidannan ina tunanin duk wannan rigimar bazai wuce haɗa aurensa da A'isha da nace zanyi ba" Itama anty Jamila ta ajiye wayarta, kafin tace "Hajiya nifa har yanzu na kasa gane wa son, kodai bashi da lafiya ne?" Hajiya tai murmishin yaƙe kafin tace "Jamila kenan kin mance shekarun da suka wuce har Hospital ɗin London mun tafi, ƙaararrun likitoci suka tabbatar mana da lafiyarsa ƙalau, Thinking anty Jamila ta farayi, ta ɗau few minutes kafin tace "am Hajiya inaga kawai ki tura ta Kano gurin Anty Tasleem wallahi Hajiya sai kin gode min da shawarar nan da zan baki, kinga Anty Tasleem  ƴar gayu ce, zata gogar da A'isha fiye da inda bakya zato, zata wayar da ita sannan ta sa ta a school, zamanta a nan Abuja bazai yiwu ba, sbda ma'aruf, tsoronsa zai dinga ɗauke mata hankali ta dinga tsorata ta kana samun nutsuwar" Sai da Hajiya mama ta ɗau tsawon mintoci tana thinking kafin daga ƙarshe tace "wallahi Jamila na yarda da zancenki, amma fa ni ba zani Kano ba, sai next months sai dai ku tafi tare, amma zan gargaɗeki akan maganar alkawarin aurenta da ma'aruf da mukayi, inaso ya tsaya daga ni sai ke". "Insha Allah" anty  Jamila tace tana danna wayarta ta fara lalubar number anty Tasneem, ringing ɗaya ta ɗaga tare da faɗaɗa murmishinta, kafin tace "Jamila manyan gari wato anty ta ɓoye ki ko? Kin dena kira waccan number taki ma bata tafiya" Anty Jamila tayi dariya kana tace "yanzu dai duk ba wannan ba, insha Allah gobe ina hanyar zuwa Kano a airplane zan taho, anty Tasneem tace mata Allah ya kawota lafiya cike da farinciki, Hajiya dake zaune gefen anty Jamila tace "yanzu me ya kamata a siya mata, kokuma kina ganin sai kunje kwa ƙare shawarwarin acan?" "Eh Hajiya da zai fi, amma fa akwai buƙatar isassun kuɗaɗe wanda zasu isa kinga duk da haka nauyi za'a ɗora mata, Hajiya tace "oh Allah aikin zumunci sai an daure, tun Ma'aruf yana ƙarami nake da burin in ga ya auri ƴar uwarsa amma burina bai cika ba" Hajiya ta ƙare maganar cike da yanayi na damuwa, "Hajiya ki kwantar da hankalinki ga ta an samu, A'isha ai rainon mu ce, sannan bazata cutar damu ba da izinin Ubangiji" Hajiya tace "Allah ya yarda, zanyi miki transfer na one million a fara dashi, sai kuma kuɗin jirgi ko?" Anty Jamila tace"karki damu Hajiya nidai fatana in ga hankalinki ya kwanta sosai, Jinginar da kanta tayi a saman kujera hawaye suka fara gangarowa a saman kumatunta, cikin muryar kuka tace "Allah sarki Alhji kafin rasuwarsa ya jaddada min aurar da A'isha ya barmin wasiyyar in kula da ita kamar ƴar cikina.. Ta sake fashewa da kuka, anty Jamila ta dafa kafaɗarta cikin raunin zuciya tace "insha Allah Hajiya zamuyi nasara ni kam na fara hangowa. Washe gari, ɗaya daga cikin dogayen rigunan da  anty Jamila ta siyawa Talatu ta sanya, pink color ce sai mayafinta light pink, kayan sun amshi jikinta, ta fito parlo ta zauna, har yanzu jikinta babu ƙarfi sosai, Dija da Hajjo suka fito domin ƙarasa aikace-aikacen gida, wata uwar harara Dija ta watsa wa Talatu, wanda karaf sukayi ido biyu, cike da masifa Talatu ta mike, ta fara nuna Dija da hannu tana cewa dama na daɗe ina tara ki, sai in fashe miki ƙaton baki, jibeta kamar wata kazar mayu" Kukan kura Dija tayi, wanda ta mance ko da wa take faɗan idanunta sun rufe sosai, ta cakumo wuyan Talatu, suka fara kokawar dambe, Hajjo dake ƙoƙari rabasu Talatu ta ɗura mata zagi, dole ta ja gefe ta zuba musu idanu, Jin hayaniyar tayi yawa sosai, ya sa anty Jamila fitowa tun daga ƙofar bedroom take cewa "wai meke faruwa ne?, tana maganar ne tana ɗaura agogo a tsintsiyar hannunta, Rai a ɓace ta janyo Talatu tana cewa "Dija mai ya haɗaku?" "Kafin Dija tayi magana Talatu ta ce Hajiyan binni wallashi ita ta fara wai cewa tayi, wannan Hajiyar nan farar nan wai muguntarta tayi yawa, wai bata biyansu albahi, bayan nan ta ce, wai ita ta gaji da zaman gidannan", Talatu ta ƙare maganar tana rushewa da kururuwar kuka, sosai maganar Talatu tayi tasiri a zuciyar anty Jamila, a duniya bata ƙaunar ɓacin ran Hajiya mama bata son abinda zai tunkareta na game da sauyawar yanayi fara'arta, Dija ko ta rungume hannaye a ƙirji tana mamakin bom ɗin da Talatu ta haɗa mata, cikin ladabi ta durƙusa har ƙasa, kafin tace "Hajiya wallahi ƙarya takeyi min" Dija tai maganar tana fashewa da kuka, tasan in har anty Jamila ta koreta a gidansu Hajiya ma bazata barta ba, sannan makomarta ma ta fara tunowa, aikin da takeyi ne yake taimakawa ƙannenta da mahaifinta da mahaifiyarta, kasancewar mahaifin nata yana fama da ciwon ƙafa, "Dija rashin mutuncin naki yayi yawa, ki tattara kayanki ki bar gidannan, yau wata saura kwana goma sha biyar ya ƙare ko?, barin baki kuɗinki, kiyi gaggawar fita tun kafin Hajiya ta fito dan zan ɗauki mummunan mataki a kanki, rashin godiyar Allah ne yasa kike wadannan maganganun. Anty Jamila ta ƙare maganar tana miƙa mata 50k, kasancewar kuɗin aikin nata 30k ne, ya zama ta ƙara mata 20k, Dija na kuka ta karɓi kuɗin, jiki a sanyaye ta kalli Talatu, itama Talatun ita take kallo, tayi mata gwalo wanda ya daɗa sosawa Dija zuciya, Hajjo dake can gefe a raƙuɓe tai saurin bin bayan Dija, koda ta shiga samun Dija tayi tana rusa kuka gami da cewa "wayo Allah nashiga uku na lalace, Hajjo ta dafa kafaɗarta cikin sigar lallashi tace "Dija kinga banbancinmu da ita kenan, shiyasa na..." "Dakata Hajjo, a halin yanzu duk wata maganar da zakiyi ba zata yimin amfani ba, kawai ki ƙyaleni" Dija tai maganar tana saɓo jakar kayanta kafin ta ɗora a kanta, Talatu kam ranta fess dan ko wata tambaya anty Jamila batayi mata ba. SINGAPORE Buland island Dariya suka sheƙe da ita, tare da tafawa, oga ya kalli fuskarsa matar da suke magana wacce zata Kai shekaru hamsin a duniya, "Mesha yaran nan zasu kai shekaru nawa?" Da yaren su yake magana.. "Reed ina tunanin sunkai 20yrs gaskiya, akwai wata matsalar ne?" Misha ta jefa masa tambaya, Girgiza kai yayi, kafin ya ɗan latsa wayarsa sai kuma ya ce "akwai abin da suke bukata ne?" "Misha tace "komai akwai sai dai bana son yawo da suke yi Reed" Og Reed ya sheƙe da dariya kafin yace "Misha wannan yawon da suke yi ai shine zasu sami kwanciyar hankali suyi ƙiba suyi kyau, kinga bokana ya gayamin cewar inhar suna yawan yin sex da maza sunfi kawo kuɗi idan lokacin da zamu kaisu kasuwa yayi, amma fa akwai wani babban gargaɗi da zanyi miki, duk wani Muslim da ya kawo ƴarsa gurina, bana nunar masa da haka, kawai ina nunar musu da zamu fitar dasu daga Musulunci ne" Murmishi tayi, kafin tace "haba Reed baka da matsala dani, sai dai motar da ka siya min ta fara tsufa ina buƙatar wata" hannun sa ya ɗora a saman kanta kafin yace "baki bani komai ba haka zaki wuce ?" Sai da ta ɗan turo ƙirjinta wanda kana ganinta kasan ita ɗin ba yarinya bace ta girma, tace "karka damu yanzu zan koma gida gobe zan dawo zakayi farinciki sosai, tai maganar tana miƙewa tsaye kana ta saɓa jakarta tana yi masa kiss a kumatu ta ɗaga masa hannu cike da nuna kulawa, murmishi yayi kana ya ɗaga mata hannu, Waye Reed Reed babban matsafi ne anan ƙasar Singapore, ya kasance gagararre ga duk wani ɗan adam, baya shakka ko jin tsoro yayin da zai gudanar da aiyukansa, a halin yanzu akwai ƴan mata sunkai hamsin a hannunsa, wanda basu taɓa aure ba sai harkar karuwanci, a cikin ƴan mata hamsin ɗin nan akwai guda biyu waɗanda ya ware su, sune ƴan Nigeria, da Hussaina mai suna Nyrah, sai Iham mai suna Anjali, rayuwa suke yi ta gata da samun kulawa, ko wacce a cikinsu bata san da wani labarin talauci ba, kudade ne gasu nan su da kansu suke ɗiba suna bawa samarinsu. Monday tushen aiki.. Katafaren gida ne mai hawa uku, gidan ya haɗu iya haɗuwa, komai nasa fari ƙal, ba ƙaramin mamayar guri akayi gurin gina wannan gidan ba, dan zamu iya kiran gidan da babban gida a hausance, amma sedai mutanen da suke cikin wannan gida idan ka gansu sai ka sake kallo, tsabar kyau da zubin halittar ko wacce, sannan ko wacce budurwa tanada ƴar aiki sai abinda ta zaɓa shi za'a kawo mata, rayuwarsu suke yi cike da gata, nasan zakuyi mamakin cewar mai yasa babu wacce take yunkurin guduwa?"..muje zuwa 👉 KANO Suna isa Kano suka wuce anguwarsu Anty Tasleem dake Unguwa uku, masu gadi biyu ne a gidan, ba sai na tsaya fasalta muku irin tarin dukiyar da aka narka gurin gina gidan ba. Wasu masu aiki dattijai guda biyu ne suka tari su anty Jamila sunata yi musu lale marhabun, abinda zai baka mamaki anan shine, Anty Tasleem bata ƙaunar kishiya bata ƙaunar abinda zai hada mijinta mu'amala da wata mace bayan ita, dalilin da yasa ƴan mata basa yi mata aiki kenan, Anty Tasleem ce ta fito harabar gidan tana sanye da Black abaya mai adon golden stone ta yafa veil a kanta, Masha Allah tayi kyau sosai, Anty Tasleem baƙa ce ba sosai ba, tanada jiki ba mai muni ba, sannan tanada cikar halitta sai dai shekararsu biyar da aure ko ɓatan wata bata taɓa yi ba, cikin farinciki ta taresu suka shiga ciki, mutuwar tsaye Talatu tayi, sbda ganin ƙyale ƙyalen da aka ƙawata gidan dashi, ko ina gunin birgewa, bazata iya cewa gidansu Hajiya ya fi na Anty Tasleem ba, sai dai ya fishi kayan ƙyale ƙyale, zama sukayi a saman couch mai masifar kyau, wani sanyin AC ya ratsa jikin Talatu har wani lumshe idanu takeyi, ɗaya daga cikin ƴan aikin ne suka kawowa su anty Jamila food flaks kala biyu, ɗaya tuwon shinkafa miyar egusi sai ɗayar farfesun kifi, gefe kuma jug ne wanda aka zuba kunun aya wanda ya ji peakmilk mai sanyi sosai, Anty Tasleem ce ta zauna kusa da Anty Jamila cike da fara'a tace "Jamila kinyi wuyar gani" Anty Jamila tai murmishi kafin tace "ke da sai a shafe shekaru ma bazaki kawo mana ziyara ba?, Talatu tace "ina yini"  Anty Tasleem tace "lafiya lau Jamila wacece wannan?"...! 08141799224 Mom Islam *NA KASA JUREWA*      🪻🪻🪻     Mom Islam Page 31-32 Anty Jamila tace "walhi yarinyar ƙanwar Alhji ce, kinsan kafin ya rasu ya bar wasiyya akan ko bayan ransa Hajiya ta kula da danginsa, shine take ta ƙoƙari, gurin taga ta kyautata musu, cike da kallon tausayi anty Tasleem ta bi Talatu, kafin tace "yanzu ya ake ciki?" Kafin Anty Jamila ta miƙa buƙatarta ga anty Tasneem sai da ta jinjina, cikin ƙarawa kanta ƙwarin gwaiwa tace "Anty Tasneem dama na kawota ne ta sami ko da 2months ne a gidanki kiɗan wayar mata da kai, sbda daga ƙauye tazo wallahi idan kinga inda suke rayuwa abin ba daɗi" Sosai anty Tasneem ta fara tattauna amsar da zata bawa Anty Jamila, can dai tace "shikenan dama nan da wata biyun zamu tafi Dubai kinga shikenan" Anty Tasneem tai maganar cikin fara'a, kunun aya kawai anty Jamila ta ɗan sha, ta miƙe tana cewa "anty Tasneem zamuyi waya, wlhi kinsan sana'ar tamu babu lokaci"  anty  Tasneem ta miƙe tana ce mata "ba dai tafiya zakiyi ba?" "Ai kuwa wlhi zan wuce, "am ki bani account number ɗinki zan tura miki da wasu kuɗi da Hajiya tace ayi wa yarinyar siyayya" Anty Tasneem ta karanto mata, a take a gurin taji alert na 1million tace "ya shigo", daga nan sukayi sallama anty Jamila ta wuce. Ko da anty Tasneem ta dawo ta samu Talatu a durƙushe a gaban fridge tana ta ƙare masa kallo, sai tayi kamar zata buɗe sai kuma ta fasa, haka ta dingayi, Anty Tasneem tace "karki damu zan nuna miki komai da kuma amfaninsa, amma meye sunanki?" Talatu ta washe haƙora kana tace "Talatu" Anty Tasneem tace "Talatu ba suna bane, daga yau duk wanda ya tambayeki sunanki ki gaya masa na gaskiya meye sunanki na gaskiyar." "Sunana A'i hya" dariya ma Talatu ta bawa anty Tasneem, tana dariya tace "gaskiya daga yau zamu fara, kice Aisha" Talatu tace "A'i, hya" sai da anty Tasneem ta maimaita mata sau biyar, anty Tasneem na faɗa Talatu tana nanatawa, da haka ta fara faɗa dai-dai, "Tashi muje in nuna miki ɗaki wanda zaki dinga kwana," Talatu ta miƙe tana bin bayan Anty Tasneem tana tafiya tana waige waige, koda anty Tasneem ta murɗa handle na ƙofar Talatu tayi mutuwar tsaye tare da dafe ƙirji tace "na higa uku inaga dai Allah ne ya yanke min wahala wannan irin daula haka?" Tana maganar tana jinjina kai. Wani haɗaden gado anty Tasneem ta nuna mata, tace "anan zaki dinga kwana, ta nuna mata TV dake manne a jikin bango, tace "wannan kinga inda ake kunnashi, sannan ta kirata suka shiga toilet, ta nuna mata gurin yin kashi da fitsari da bahon wanka da duk wasu abubuwan amfani, kasancewarta yarinya mai ƙwaƙwalwa yasa komai aka gaya mata yake zama daram a cikin ƙwaƙwalwarta, zuwa can yamma anty Tasneem ta sake yin wanka, ta sa Talatu itama tayi, lokacin da ake kiraye-kirayen sallahar magriba, suna kitchen ita da anty Tasneem, kasancewar anty Tasneem ƙwararriya ce gurin iya girki, dan har madia sunada labarinta, ta kasance mace mai baiwa gurin sarrafa girke-girke iri-iri, bayan sun fito daga kitchen Talatu ta hau yin tsalle, anty Tasneem ta haɗe rai, cikin rashin jin daɗin bata nutsuba, tace "A'isha ya kamata ki nutsu ki rage rawar kai bana jin daɗin ganinki haka" Talatu ta sunkuyar da kai, saboda a duniya bata taɓa tsoron wata halitta ba, kwatsam sai ga shi anty Tasneem tana yi mata kwarjini, tsawa ɗaya tayi mata sai ta daidaita nutsuwarta, a round 10:pm suna zaune a parlor suna kallo a makeken TV wanda kamar zaka yiwa mutum magana ya amsa, Alamar shigowa sukaji. A hankali ya murɗa handle na ƙofar cikin izza da kamala yai sallama tare da ƙarasowa cikin parlon, anty Tasneem ta miƙe cike da kewarsa taje cikin yanga ta rungumeshi, kafin tace "baby I miss you walhi, ƙwayar idanunta yake kallo itama shi ɗin take kallo cikin cold voice ɗinsa yace miss you too my, hannunsa na a ƙugunta itama irin riƙon da yayi mata tayi masa, sai wani marairaice masa takeyi, kai kace ƙaramar yarinya, Talatu kam kunya ce ta kamata, sai ta juya fuskarta jikin bango tv ma ta kasa kallo, shikam bai ma san da akwai wata bayan anty Tasneem a gidan ba, a rungume da juna suka wuce bedroom ɗinsa, sai da ta taimaka masa ya rage kayan jikinsa kana taje ta haɗa masa ruwan wanka, wanda ya ji turaruka masu sanyin ƙamshi, "Baby na gama haɗa maka ruwan" anty Tasneem tai magana cike da shagwaɓa, "zonan" Junaid yace, yana lumshe eyes ɗinsa, kasancewar ya zauna a bed ita kuma tana tsaye, ta tako a hankali tare da ɗan zama saman cinyarsa, "na gaji sosai baby" Junaid yayi maganar ne cike da yanayi na gajiya" cike da nuna kulawa tace "baby idan kayi wanka Zaka ji daɗin jikinka, duk da bata jima da yin wanka ba, sai da ya sa ta yin wani wankan. Bayan ta tayashi shiryawa, ta ce masa "baby mun yi baƙuwa fa" janyota jikinsa yayi kafin yace "wacece?" Anty Tasneem tace A'isha amma daga ƙauye take, anty Jamilan Abuja ce ta kawota, tayi masa cikakken bayani, ya gamsu, kana yai na'am, sannan ta roƙeshi alfarmar ya samo mata me koya mata lesson kafin ya yi tafiya...! Sbda kar ku jini shiru yasa nayi muku wannan, kuyi hakuri yayi kaɗan sosai, walhi aiki ne yasha kaina barkanmu da Sallah. Mom Islam *NA KASA JUREWA*         🪻🪻🪻        Mom Islam Page 33-34 Sai da ta tabbatar da Junaid ya amince kafin tayi murmishi, a hankali ta tura hannunta cikin nashi, cikin cold voice tace "Baby please ka tashi muje ka ci abinci" Tayi maganar tana kashe masa ido, Bayan ya tashi, kai tsaye dinning area suka wuce, kunun tsamiya da ƙosai kawai ya sha, yace ya ƙoshi, kwaɓe fuska tayi, cikin shagoɓa tace "haba baby gaskiya nikam ban yarda ba, shikenan abincin da zaka ci?" irin maganarta ya kwaikwaya kafin yace "kema ai banga kin ci ba" "to...to...to" tace tana yin raurau da idanu, sai kuma ta miƙe da sauri tabar gurin, Sarai ya san halin abarsa ya miƙe yana murmishi, wayoyinsa ya ɗauka ya wuce bedroom ɗinta, bata nan, ya fito ya nufi bedroom ɗinsa, acan ya sameta ta kwanta ta rungume pillow siraran hawaye na zubowa a kumatunta, zama yayi a gefenta, kafin ya tallafo kanta kana ya ɗora a saman cinyarsa, cikin sigar lallashi yace "baby  mai ya faru, ko duk akan maganar cin abincin nawa ne?, yai maganar yana tura hannunsa cikin rigarta, Ƙara sakar masa kukan shagoɓa tayi tana wani juyi tare da cino baki, sai kuma ta lumshe idanunta, "am sorry my lovely dan Allah karki hukuntani da hakan, wlhi na ƙoshi kafin in dawo gida na biya ta gidansu Umma na ci waina", Yai maganar yana kama kunnensa ɗaya, ɗayan hannun nasa yana cikin rigar, "shikenan ya wuce?" nayi tunanin gurin wata kaje" Dariya ma ta bashi, sai ya gimtse gudun kar ya sake yin lefi, a hankali ya zuge zip na rigarta tare da tura kansa cikin rigar, ya Subhanallah wani daddaɗan ƙamshi ne ya ziyarci hancinsa, ya jima yana sinsinarta kafin ya ci gaba da murza kan nipple ɗinta cikin salo na jiyar da ita daɗi, idanunsa a lumshe yake cewa "Baby kinsan me?" ƙara turo masa ƙirjinta tayi tana ce masa "a'a" Murya a matuƙar sanyaye yace "walhi duk lokacin da muka kasance a tare koda ina cikin damuwa sai inji ta shuɗe babu wacce nake kallo a duniya sai ke, babu wacce nake mafarki sai ke, my baby kullum sabuwar soyayyarki tana ƙara shigata, Tun ɗazu Talatu take gurin a tsaye, sbda ta zo kiran anty Tasneem ta ji Junaid yana ta dagargazo kalamai, mutuwar tsaye tayi lokaci guda ta sauke numfashi, ita dai bata san menene so ba, sannan bata san me akeji game da shi, janye ƙafafuwanta tayi, gudun kar anty Tasneem ɗin ta fito ko mijinta, suyi mata wata fassarar, kai tsaye bedroom ɗinta ta wuce, ta zauna tayi shiru. After 1week Alhmdllh Talatu ta fara nutsuwa sannan komai nata ya sauya, sbda ta rage guje guje da rawar kai, su kaɗai ne a gidan sai ƴan aiki, ko da yaushe idan anty Tasneem zata shiga kitchen tare suke shiga, sannan ko waya zatayi da mijinta a gaban Talatu takeyi, wani lokacin ma Talatun ce ma zata ji kunya itako anty Tasneem ko a jikinta, 9:am shine lokacin da mai koya mata lesson yake zuwa ya bar gidan ƙarfe ɗaya na rana, Sosai karatu yake zama a ƙwaƙwalwarta kasancewarta mai basira, Kuɗin da anty Jamila ta bawa anty Tasneem tass ta ƙarar dasu gurin yiwa Talatu siyayya, bayan wata ɗaya, Talatu tayi ƙiba tayi fresh ta murje harda kumatu, uwa uba harda mazaunai hips ɗinta ya fito ga shi mai ɗaukar hankali, gashin kanta kuwa koda yaushe cikin shan gyara yake, wata ranar sunday Talatu ta yi wanka ta sanya riga da skirt na atamfa, Masha Allah simple makeup tayi, sosai tayi kyau, idan ka kalli ƙirjinta ya fara fito da ƙirgen dangi sun tsa cak hakan yasa suka sake ƙara mata kyau sosai, Ƙarfe 4:pm time ɗin sun kammala girki, sosai ta mayar da hankali a TV, tana kallo, remote ne a hannunta, ta fara ƙoƙarin sauya tasha, nocking taji daga bakin ƙafa, cikin nutsuwarta ta miƙe kafin taje ta buɗe, sai kuma ta juyo ba tare da ta kalli fuskar mai shigowar ba, dawowa tayi kana ta zauna tana ci gaba da sauya tasha, sallama yayi tare da zama kusa da ita, ciki-ciki ta amsa kamar wacce ta cusa wani abu a bakinta,  "zama yayi a saman couch wacce take kallon wanda take zaune, ya ɗan danna wayarsa kafin ya ɗago kai ya kalleta, "bakya magana ne?" "Uhm" tace masa tana ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, tasowa yayi daga inda yake zaune ya dawo kusa da ita kafin ya zauna tana cewa "idan babu damuwa ki zo muje shan ice cream, tasan ice cream saboda duk anty Tasneem tana wayar mata da kai, kuma ya zamo best ɗin ta sbda tana yinsa sosai, ɗago fararen idanuwanta tayi, kafin ta ɗora su a nasa cikin siririyar murya tace "sai na tambayi anty" murmishi ya sakar mata mai kyau, kafin ya miƙe yana cewa "hajiyarmu" anty Tasneem ta fito fuskarta ɗauke da murmishi tace "Arman kai ne a gidan namu?" Shima murmishin ya mayar mata kafin ya haɗe hannayensa cikin sigar roƙo yace "anty Please zamuje shan ice cream tare da wannan baƙuwar walhi yunwa nakeji" dariya ma ya bata, amma sai tayi murmishi kana tace "ba yunwa kakeji ba, kawai dai yawo zakaje" Ya miƙe yana cewa "ƴar anty tashi muje ki rakani" Talatu ta miƙe tana cewa "anty in bishi" Inda tayi maganar a shagwaɓe sai abin ya birge Arman, anty Tasneem tace "jeki ɗauko mayafi" Ta sake kwaɓe fuska, kafin tace "anty nifa ban san wanne zan sa ba" anty Tasneem ta bi ta har bedroom ɗinta, bayan sun shiga anty Tasneem ta kamo hannunta kafin tace "A'isha ki kama kanki dan Allah ki riƙe mutuncin ki, Arman ɗan uwana ne, kinga bazan shede shi ba, sannan ki san maganar da zaki dingayi, inason ki kasance mai aji da iya magana tare da sarrafa harshe, Cikin girmamawa tace "Nagode anty" Anty Tasneem ta fito mata da mayafi, da hand bag irin takalmin suka fito a tare, tana cewa "Arman ka kular min da Aysha fa" "Insha Allah" ya ce mata yana karkaɗa key car ɗinsa,  Suka fice, kai tsaye motarsa suka nufa, mai kyau da tsada, kasancewar Arman ɗan uwan Tasneem ne uwa ɗaya uba ɗaya, infact ma shine autansu, suna ji dashi sosai, Har ya buɗe backside ya ce ta dawo gidan gaba, bayan ta dawo ya rufe murfin motar suka wuce, kai tsaye gurin shan ice cream ɗin suka wuce kamar inda ya faɗa mata, sunyi nisa babu mai cewa kowa komai, a hankali yace "dama sunanki Aysha ne?" gyaɗa masa kai tayi tare da sunkuyar da kanta, me kikeson ci idan munje?" Lumshe idanunta tayi kafin ta jingina da jikin bangon kujerar da take zaune, har suka iso bata ce dashi komai ba, Koda yai parking ya fito, yaje ya buɗe mata, tana fitowa, ta gyara zaman mayafinta, ashe ɗaya wayar da yayi kamar yana danne-danne yana yi mata photo ne, sosai tayi kyau, idanu sai suka dawo kanta, sbda dama gurin ya haɗa da samari da ƴan mata, Arman yana tsaye can gefe yana waya, da alamu wayar da yakeyi mai muhimmanci ce, wani saurayi matashi wanda bazai girme masa ba ya tako zuwa inda Talatu take a tsaye, cikin faɗaɗa fara'arsa yace "amincin Allah ya tabbata ga kyakkyawa mai kyan hali tare da kyan zuciya, da fatan banyi laifi ba da nayi miki magana?" Sai da ta sake gyara tsayuwar ta, kafin tace "babu damuwa, amma mai ya kawo ka gurina?" dama tun ina zaune na hango tsayuwar motarku, walhi tunda nayi tozali da kyakkyawar fuskarki lokaci ɗaya na ji na rasa nutsuwata, dan Allah kiyi min wata alfarma, yai maganar yana kallon Arman dake tahowa, kasancewar tsakaninsu akwai nisa, cikin sauri ya miƙa mata wata takarda kana yace "ki yimin koda flashin zan kira mu dinga gaisawa, yana kai ƙarshen maganar Arman na isowa, cikin takunsa mai ɗaukar hankali, shi kuma saurayin yana barin gurin, "waye wancan?" Arman yai maganar cikin yanayi na ɓaci rai, cikin siririyar muryarta tace "oho nima ban sanshi ba" ta ɓoye takardar da ya bata, koda ta kalli yanayin fuskarsa sai da gabanta ya bada rass, amma sai ta basar tare da kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunta, shi haushi ma ta bashi, ko shan ice cream ɗin ma basuje ba yace ta shiga mota, babu inda ta iya, dole ta shiga motar suka wuce, again dai wani gurin shaƙatawar suka nufa, wanda ya doke wannan a kyau da tsari, dakaga gurin kasan na zuwan ƴa ƴan manya ne, koda suka fito a mota, ba samari ba, har ƴan mata hankalinsu na gurin Talatu, wata anan sukayi faɗa da saurayinta ta tashi ta barshi, kujeru ne iri iri masu kyau gunin ban sha'awa, yayi mata nuni da ta zauna a wata wacce babu kowa, kuma tana can nesa da mutane, kamar inda ya umarceta hakan ko tayi, ta zauna anan tana ta ƙarewa ko ina kallo, wasu harufan ta haɗa ta karanta wasu kuma sun gagareta ta ƙyalesu, yana can shi dai yaje sama musu abin sha, ita kuma tana zaune tayi shiru kamar mai nazarin wani abu, "Aslmu alaikum Beautiful girl dafatan na sameki lafiya?" tuno nasihar da anty Tasneem tayi mata tayi, na cewar karta yarda ta wulakanta mutane, sbda ɗan Adam daraja ce dashi, sai tayi amfani hakan, ta amsa masa sallama, hakan ya bashi damar zama ya fara gabatar masa da kansa, "da farko dai sunana Ibrahim keda?" yai maganar yana jifanta da ƙayataccen murmishi, "Aysha" ta faɗa ba tare da ta kalli inda yake zaune ba, Sosai furta kalmar Aysha ya birgesa, domin kuwa ji yayi muryarta tayi kamar ana busa sarewa tsabar daɗi, kai tsaye yace "ko zan iya samun lambar wayarki?" Karaf a kunnen Arman dake dawowa hannunsa riƙe da wata takarda, wani mutumi ma'sikacin gurin yana biye dashi da wani kyakkyawan faranti an jere kayan ƙwalama a ciki, sam bata ma nunar da tasan da zaman Ibrahim a kusa da ita ba, sai ta wani sha ƙamshi tana sake gyara ɗaurin ɗankwalinta, ajiyar zuciya ya sauke, wace na kusa dashi yana iya tabbatar da hakan, rai a ɓace yace "malam kasan dai haramunne, yin magana da matar da ba muharramarka ba ko?" jiki babu power Ibrahim ya miƙa tare da kama bakinsa da hannu, kafin yace "dan Allah a gafarceni abokina, ya bar gurin, itako shi take kallo, saboda a inda yai maganar sai ka rantse ita ɗin matarsa ce, Tunda yaga kallo ya koma kanta, ya tattara kayan yaje ya karɓo leda, yace ta tashi su wuce, haka dai ta tashi ba tare da tayi masa musu ba, Koda ya fara driving, sai satar kallonta yakeyi, magana ya farayi a cikin zuciyarsa, "bai kamata in sanarwa da yarinyar nan ina sonta ba, saboda wallahi zata yimin wata fahimta da ban, zan bari idan ta ƙara girma sai in sanar mata, Yes hakan ma shine dai-dai" Ya ƙare maganar yana murmishi yana shafa sajensa, har suka iso gida bai ce mata ba, itama bata ce masa ba, koda suka iso parking space, ta fara shirin buɗe murfin mota Arman ya hanata, yana son ya yaudarar da ita suyi hira, yace "Aysha dan Allah ki tsaya kiyi karatu ki mori lokacinki karki fara soyayya yanzu Please and please na roƙeki, idan kika duba shekarunki kwata-kwata bazasu wuce 14yrs ba, kinga kinada sauran lokaci....! Kaina bisa wuyana, insha Allah daga yanzu da izinin Ubangiji zaku dinga samun update koda yaushe. Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻          Mom Islam Page 35-36 Sunkuyar da kanta tayi, kana ta janyo zaren mayafinta tana wasa dashi, gaskiyarsa ne, sai dai bata ma kai shekaru goma sha huɗun da ya ambata ma, Har ya gama yi mata nasiha ƙala bata ce masa ba, sai dai jinjina kai da takeyi, Daga ƙarshe dai suka fito a motar suka wuce ciki, gurin anty Tasneem,  a parlor suka sameta tana zaune tana waya, sai dariya takeyi,  "Aysha kinji ana ta kiraye-kirayen sallahar magriba Please kafin in dawo ki ajiye min abinci" To kawai ta ce masa ta miƙe, ko da ta shiga kitchen ɗin  tunani iri-iri ta farayi, sosai ta san da cewar ta shigo sabuwar rayuwa, sannan ta ga sauyi sosai a tare da ita, bayan ta gama zuba masa abincin ta kawo parlor ta ajiye a saman table ɗin dake a tsakiyar ɗakin, kafin ta wuce domin ta kabbara sallah, sbda anty Tasneem ma lokacin da ta dawo daga kitchen bata parlor, Sai da akayi sallahar isha'i sannan Arman ya dawo, time ɗin dukkansu suna zaune a parlor, Tasneem ta kalli Talatu kafin tace "Aysha ina tsarabar mu?" murmishi kawai tayi, kana kuma tace "yana can mota" Anty Tasneem ta sake jefo mata tambaya, "to wa kuka barwa?" Shiru tayi bata ƙara cewa komai ba, sai ga sallamar Arman, fuskarsa ɗauke da murmishi yake cewa "anty wai yarinyar nan taki bata magana ne?" Anty Tasneem ta kalli Talatu kafin tace "Arman me ka gani?", Sai da ya sake kallon Talatu kafin ya sake cewa "walhi anty shiru-shiru kamar ma yin magana yana wahalar da ita" a yanayin inda yake maganar sai ya bawa anty Tasneem dariya, itako Talatu tashi tayi a gurin sbda da gasken ita kanta tana jin kamar an sauya mata ƙwaƙwalwa da ma komai na jikinta, babu wata magana da anty Tasneem zata gaya mata ko faɗa bata riƙe shi a ƙwaƙwalwarta ba, a duniya tana mugun girmama anty Tasneem ko mai yasa oho, ta sauya ɗin kamar inda Arman ya faɗa, domin kuwa ada idan ka ji wacce ba'a ɗagawa ɗan yatsa sai ta karyeshi to ita ce, a yanzu kuma ko hannu ka sa mata a baki bazata ciza ba, ko meye dalili oho, Bayan tafiyar Talatu bedroom ɗinta, Arman ya matso kusa da anty Tasneem kasancewar tana saman couch mai zaman mutum biyu, "Anty gaskiya inada shawarar da zan baki, inhar wannan yarinyar zata daɗe a gurinki, kinsan me?" Anty Tasneem tace "a'a, ƙanina sai ka faɗa ina sauraronka" Arman yace "anty dan Allah karki bari yarinyar nan ta san menene so, sannan tasan abubuwan da suka shafi soyayya, dalilina na sanar dake, shine, ya kamata ta mori ƙuruciyarta da lokacinta da tunaninta, tayi karatu mai kyau, kinga da farko dai babu wani namijin da zai kalli Aysha ya ji bata shiga ransa ba sai dai in ƙarya yakeyi, saboda Ubangiji yayi mata baiwa ta ɓangarori da dama". Ya kai ƙarshen maganar yana cewa "anty Please ki fahimceni" Anty Tasneem tace "wallahi Arman duk wannan maganar da ka faɗa gaskiya ce, sannan insha Allah zanyi ƙoƙarin ganin na inganta mata komai nata wanda zata yi alfahari dashi a nan gaba, bana son rabuwa da Aysha, kasancewarta yarinya mai shiga rai, ga jin magana, tunda tafiyar da zamuyi next week mai zuwa Junaid yace sai end of the year zamuyi, kaga zan sake nusar da ita abubuwan da suka dace, wlhi Arman Aysha nima ta shiga raina ba sai an kai ga maza ba, yanzu dai abinda nake so, a nemo min makaranta mai kyau sannan mai tsada wacce ake karatu sosai, Sallama yayi mata kana ya wuce, da niyar zai bincika makarantar da za'a sakata, Washe gari, tunda Aysha tayi sallah bata koma barci ba, tunda ta fara azkar har sai da gari yayi haske sosai, ta fito taje bedroom ta gaishe da anty Tasneem da masu aikin gidan kana taje kitchen ta ɗora ruwa, can anjima ta shiga wanka. Ƙarfe 12:pm lokacin suna lesson a parlo, sbda har da Islamic duk yana koyarda ita, Arman ne yai sallama, suka amsa a tare, sam beji daɗin ganin wannan mai koyar da ita karatun ba, sabda sai wani kallonta yakeyi kallon ma mai ɗauke da fassara iri,  iri, bayan sun gaisa da malamin kai tsaye ya wuce ciki gurin anty Tasneem, daga corridor yake ƙwala mata kira, ta fito da sauri tana cewa "Arman wannan kira haka walhi ka tsoratani, murmishi yayi kafin yace "anty an samu makarantar, St Thomas, kuntau science Academy. Anty Tasneem tace "wow kenan yau zaku tafi ko sai gobe, amma kuɗina yayi ƙasa abinda ke account ɗina bai wuce 100k ba, nasan ba zai isa ba" Arman yace "karki damu ba sai kin bada kuɗi ba, amma ta shirya mu wuce, ina sauri zan wuce office daga nan" Har anty Tasneem ta fara tafiya, sai ta dawo da baya, kana tace "dama inason in ce maka, a aji nawa za'a saka ta, kaga tayi girma fa?" Nazari yayi kafin yace "gaskiya zan ce a sata a pr 3 yayi ko?" Badan ranta ya so ba tace yayi sai ɗan babu inda zata iya, a hakan ma adu'arta ɗaya idan aka zo yi mata intabiyu ta basu haɗin kai, Kai tsaye parlorn ya wuce ta samu Malamin tace masa, zasu je makaranta tunda dama shi ya bada shawara sannan yace idan ta dawo gida sai ya dinga zuwa yana sake tuna mata karatun, sosai ya ji daɗi yace "inada tabbacin insha Allah zatayi ƙoƙari sosai a makaranta, anty Tasneem ta faɗaɗa fara'arta kafin tace "Allah yasa" Talatu dake zaune gaban malamin tana rubutu, itama farinciki takeyi, dan ko a yanayin mood na fuskarta zaka tabbatar da haka, Cikin bin umarnin anty Tasneem ta miƙe ta sauya kaya zuwa riga da skirt English wear ta zura hijabi kana ta ɗauko wata ƙaramar jaka, wacce ma babu komai a cikinta sai lipstick, man baki. Ta fito, time ɗin Arman yana can kitchen dan ya kasa zaman parlor, sosai yake kishin duk wani wanda yake da burin yin taraiyya da Talatu, malamin yayi musu sallama ya fice, duk wannan abin da Arman yakeyi anty Tasneem bata sani ba. Sai da sukayi breakfast sannan suka wuce, ada Talatu farkon zuwanta bata jure yunwa, amma yanzu sai ta kai ƙarfe 1:pm bata ci komai ba, sabda haka rayuwar anty Tasneem take, bawai babu bane kawai ra'ayin ci ne bata da shi, amma bata hana wanda zai ci ya ci ba.    KEFFI Kwanci tashi asarar mai rai, Saudart har ta gama idda, tunda Dady yaga ta gama idda ya fara yi mata siyayya,kamar su kayan makeup har gurin gyaran jiki yake kaita, cikin ƙanƙakin lokaci Saudart tayi ƙiba ta murje gunin ban sha'awa, Wata ranar Asabar tana zaune a parlor tana danne-danne a wayarta, gefe kuma tirai ne na apple cikin shauƙin bin waƙar da ke tashi a wayar ta kai hannu zata ɗauki apple ɗin wayarta tayi ringing ga shi babu suna, sai da tayi ringing ta ƙatse ta sake yin ringing kafin ta ɗaga, "Aslmu alaikum da wa nake magana?" Saudert tai maganar sabda tana neman sani, "Dariya yayi, kai da kaji Muryar ma kasan ba ta saurayi bane, muryarsa ko daɗi babu, yace "yarinya nine Alhaji Alherin Allah, ina fatan dai kin sanni kuma zaki amshi soyayyata, saboda idan har kin amince bana son bikinmu ya wuce wata ɗaya dan nikam a shirye nake" Abinda ya bata mamaki bai wuce, tunanin da ta farayi ba, kamar tana yawan jin labarin Alhaji Alherin Allah a gurin dadynta, Daga can ɓangaren nasa yace "yarinya naji kinyi shiru?  Ko in baki lokaci ne?" "Eh" tace masa, sabda ko sautin muryarsa bata buƙatar ji, yana katse kiran ta miƙe zuciyarta na yi mata zafi wani dummm takeji a kwanyarta, cikin sauri ta wuce ɗakin momy, tana shiga ko sallama bata ma yi ba, dan ko lura da Dady dake kusa da momyn batayi ba, ta rushe da kuka mai tsuma zuciya, cikin muryar kuka take cewa "momy tsabar wulaƙanci da rainin wayo ko wane tarkace sai ya zo yace yana sona, walhi nidai na gaji momy zan bar garinnan Allah kuwa" Dady ya ɗan matsa a jikin momy kafin yai gyaran murya, kana yace "Saudart ki tsayar da hankalinki guri ɗaya, ba wani bane kike kira da tarkece face aminina Alhji alherin Allah, kuma nine na zaɓa miki shi a matsayin miji, Saudart ya kamata ki gane waɗannan samarin da suke ruɗarki,  basa wani iya riƙe aure ya kamata ki nutsufa, kuma kinga shi ba da wasa yakeyi ba" Saudart ta tashi zaune tana sake duban Dady wanda bata ma san yana ɗakin ba, Cikin ɓaci rai momy tace "hmm Alhji which tallahi zaka cutar da yarinyar nan, daga ƙarshe nadama ne zai biyo baya, saboda, yarinya da ƙuruciyarta ka ce zaka aurar da ita ga abokinka wanda a shekaru ma ya girme maka nesa ba kusa ba, tai maganar a hassale, Dady yayi murmishi, wanda daga ganin murmishin kasan ya tara ma'anoni da yawa, yace "wato Zainab har yanzu baki san me duniya take ciki ba, ya kamata ki nutsu ki san me kikeyi a duniya, kinsan Allah idan baki mori duniya ba, sai ki tashi jahili ma ya fiki muƙami, kinga kuwa Naira abar so ce ga kowanne halitta" yai maganar yana gimtse fuska, Nidai na gaya maka bazan amince ba, tun yanzu ayita ƙirga mata ɗakin aure, wancan auren tayi maka biyayya, wannan ai sai ka bari ta zaɓi wanda takeso ko?" Momy tai maganar tana bubbuga bayan Saudart, "Wato Umarni kenan kike bani?, to bari kiji ko ƴan uwana ne suka shiga cikin lamarin aurannan wallahi zan iya ɓata wa dasu, saboda akan kuɗi babu abinda bazan iya yi ba, sosai ta jinjina kai, sabda sarai tasan halinsa, farin sani ma kuwa. Shiru tayi bata ce dashi komai ba, har ya tashi ya fice, BAYAN SATI ƊAYA. Alhaji Alherin Allah bai sake kiranta ba har tsawon sati guda, kamar kullum idan ta ɗan taya momy aiyukan takan je ta kwanta barci, hakan ko tayi inda take ta mafarkai iri daban daban, guɗa takeji, tayi tunanin ma a farkin ne akeyi, sai tajiyo Muryar momy a kanta cikin condition na ɓaci rai tana ce mata, Saudart ki rungumi ƙaddara walhi mahaifinki har ya karɓi kuɗin aurenki miliyan huɗu, da sauri Saudart ta tashi zaune, tana jujuya hannaye ta kasa magana, sai wani irin yanayi takeyi, daga ƙarshe dai ta fashe da kuka, momy ta rungumeta tana cewa "bari inje kayan sa lalle suka kawo, wai bikin nan da two weeks," Saudart kam ta kasa magana, har momy ta fice, sai dai bin bayan momy da kallo da tayi, ganin maganar momyn takeyi kamar a mafarki, ta fara mutsike idanu domin tabbatarwa, "ba fa ƙarya bane tunda ga shi can anata surutu a parlo" tai maganar tana share hawaye, Acan parlor kuwa akwatuna ne guda goma cif cike suke da kaya na gani na faɗa, masu kawo kayan ma cewa suke yi saura akwatiin ɗaurin aure" ita dai momy bata um bare u um, ko da suka zo tafiya, lokacin Dady ya dawo ya basu 100k, sukayi masa godiya suka wuce, kai tsaye parlorn ya shigo, inda ya samu momy da Saudart a zaune sun tasa akwatuna a gaba kowanne yayi tagumi...! More comment more typing Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*     🪻🪻🪻 Mom Islam 37-38 "Ku kuma mai ya faru kun wani yi tagumi kamar anyi muku rashi?" Dady yai maganar yana neman guri ya zauna, Har yanzu babu wanda ya bashi amsa sai ma kuka da suke yi ita da momy, Tsawa ya daka, musu tare da cewa "Saudart ki tabbatar da kin lallashi zuciyarki, domin kuwa aure babu fashi, sannan idan naji wata magana ta ɓullo ki kuka da kanki, yanzu ma dai duk ba wannan ba, zo nan" Ta taso jiki babu ƙwari, nuni yayi mata da inda yake zaune, tazo ta zauna kusa dashi, ya ciro wayarsa kana ya shiga jiji app, wasu haɗaddun kayan furniture's ya nuno mata, kai da ganinsu ma kasan ba a Nigeria aka yi su ba, sunyi kyau sosai, sai dai a idanuwanta ne kayan suka birgeta a zuciyarta kuwa sam basu bata sha'awa ba ko kaɗan, "ki zaɓi wanda kikeso," Dady yai maganar yana sake nuno mata wasu, "ko wanne ka zaɓamin Dady sunyi" Saudart tayi maganar  cikin rashin walwalah, Ganin kar suyita jayayya yasa ya kashe datansa ya koma kan momy, "Zainab kafin biki nake son mu tashi daga gidannan mu koma wanda na siya" itakam momy ma bata da masaniyar ya siyi wani gida, sbda ada ne yake shawara da ita ban da yanzu da ya kama gashin kansa, "Bata amsa masa ba, sai ma ce masa da tayi, "yaushe Anam zata dawo?" shiru yayi na ƴan wasu lokuta kafin yace "kwanan nan" Kwata-kwata yanzu ta kasa yarda da Dady, ta kasa jure wasi wasinta sannan tana tunanin kar fa, ya je ya aikata wani abun da ƴarta, hankali a tashe tace "Habiby ka kira min ita mu gaisa koda yaushe bana samun ta a waya WhatsApp ma ta daɗe bata hau online ba" "Haba Zainab da ba haka kike ba, yanzu kin sauya sosai, na ce miki tana nan lafiya ko? ki kwantar da hankalinki, ai basuyi hutu ba" Gudun kar suyita jayaiyya a gaban Saudart yasa tai shiru. Bayan kwana bakwai, biki ya rage saura sati biyu, babu abinda momy ta yiwa Saudart, sannan ko tattauna maganar bikin basayi, kowa harkar gabansa yakeyi, sai dai shi dadyn in ya shigo ya fara damunsu da maganar abubuwan da za'ayi shine suke ma tunawa da maganar wani buki, Waye Alhji alherin Allah?, Wani babban mutum ne, wanda ya gurmewa mahaifin Saudart ɗin nesa ba kusa ba, yana da dukiya ta ban mamaki, yanada mata ɗaya, da yara biyar a cikinsu huɗu sunyi aure uku mata ɗaya namiji yarinya ɗaya ce take gaban matarsa Hajiya Zaliha, Hajiya Zaliha ƴar asalin garin mai duguri ce, kirarin ta shine, bata zama da kishiya, wasu ma har sunayi mata kirari da wai shiga da alwalarka, Matan su uku biyu sunyi aure a ƙasar waje, ɗaya kuma tana nan a Keffi anan tayi aure, tsakaninta da gidan iyayenta beyi 200 ba, sunanta Salma, tunda taji mahaifinta zeyi aure, tasa aka yiwa Hajiya Zaliha sabon furniture's da odar magungunan mata, a cewarta ƙarya ne amarta ta nuna mata wani abu, itama Hajiya Zalihan tana nan tana faɗi tashi gurin bokaye da ƴan bori, sabda taga an fasa auren, sai dai kash duk inda taje, sai suce mata wannan auren duk wanda yai shishigi a lamarin auren yana iya rasa rayuwarsa, ɗibarsu tayi ta watsar sbda ta dangana komai ga kanta, ita zata ji da komai, dama koda yaushe cikin ado da tsafta take, ya kasance ta ƙara a nada, duk da ta fara manyanta har gyaran jiki akeyi mata, ga gyaran gashi da ake turarashi da turaren mai duguri, tun kafin bikin kullum basa zama a gida ita da yarinyarta Salma, Salman bata taɓa aihuwa ba, sunyi neman magani har sun gaji, koda mijin yayi niyyar ƙaro aure, Salma na jin labari zasuje gurin boka a rufe masa baki, sai maganar ta shiririce. Kwanci tashi asarar mai rai, yau ta kasance Friday wato ranar sa lalle, momy kam bata gayyaci kowa ba, ta ɓangaren dady, kam yayi gaiyyata harda su gaiyyar soɗi, an cika gida sosai, 200k Dady ya mikawa Saudart, bayan kaya wanda zata sa daga yau har zuwa gobe ɗaurin Aure da yayi mata, dan ko na akwatin ma ba'a taɓa ba, har yanzu a cikin gasgata maganar auren takeyi, sbda ko kaɗan bata jinsa a ranta, ƙarfe 5:pm wayarta tayi ringing, lokacin suna zaune da Dady a ɗakinsa ita da momy, tai banza da kiran, wayar ta sake ringing, Dady ya lura da yanayinta, yace "amma kamar kiranki akeyi ko?" "Eh...eh" Saudart ta amsa masa bakinta na rawa, Wayarta ta sake yin ringing a karo na uku, dole ta ɗauka ba tare da ɓata lokaci ba, "Assalamu alaikum" ta faɗa tana cin ɗaci a ranta, daga can ɓangaren ya amsa da wa'alaikumussalam masoyiyata" gabaki ɗaya muryarsa bata yi mata daɗin sauraro, babu inda ta iya, dole ta ci gaba da jin me zai ce, "gani a ƙofar gidanku ki fito ina jiranki, Momy dai ta mayar da hankalinta a kan wayar da ke hannunta, bata ma san me Saudart ɗin take ciki ba, sai Dady da yake sa mata idanu, ɗagowa tayi ta kalli Dady wayar na ƙare a kunnenta, sai kuma ta juya ta kalli Momy da take ta murmishi ga dukkan alamu bata ma san wainar da ake toyawa ba, "Idan wata matsala ta biyo baya walhi ki kuka da kanki" Dady yai maganar cikin ɓacin rai, miƙewa tayi ba tare da ta sake magana a wayar ba, ta fice, kasancewar dama da hijabi a jikinta, bayan ta buɗe get ta hango motarsa a gefe, jiki a sanyaye ta ci gaba da takowa har zuwa gurinsa, tsayawa tayi cak, tare da rungume hannuwanta a ƙirji, yana daga cikin mota yana ƙare mata kallo, sai wani lashe baki yake kai kace maye, "innalillahi walhi zan more, kai kai dole in dinga bawa yarinyar nan kulawa ta musamman, da zarar ta shigo gidana zan nuna mata so da ƙauna" har ya kai ƙarshen zancen zuci da yake yi bata ƙara so ba, tana tsaye ta sunkuyar da kanta ƙasa, Allah sarki Saudart yarinya mai biyayya. Rage gilashin motar yayi, kana yace "haba my wife ki ƙara so mana" cikin suɓutar baki tace "waye wife ɗin?" Cikin samun ƙwarin gwaiwa yace "ga ki tauraruwata" yai maganar yana nunota, "hmm" kawai tace, ya buɗe mata ɓangarensa yace ta shigo, "a'a" nan ma yayi, ta faɗa tana gyara tsayuwarta, "motsin buɗe get da taji ne ya sa ta yi saurin matsawa, ta fara ƙoƙarin shiga motar, murmishi yayi sabda hakan yayi masa daidai, koda ta shiga sai wani irin kallo yakeyi mata, kai kace yau ce rana ta farko da ya taɓa sanya mace a idonsa, ya ɗan matso kana yace "shekaran jiya nayi miki text message akan ki gayamin abubuwan da kike buƙata sannan kamar nawa ne zai isheki yin siyayya?" "Bana buƙatar komai, saboda inada komai" Tai maganar tana matsawa, saboda a inda ya matso suna iya jiyo numfashin juna, "A matsayina na mijinki ya kamata ace mun fahimci juna kafin ki shigo gidana, amma naga kamar bakya wani mararin kasancewata a tare dake" kamar jira takeyi ya gama magana caraf ta karɓe da cewa "eh mana auren dole Dady zai yimin, kaima son ranka kabi, baka tunanin ya rayuwa zata kasance, ko kana tunanin auren da akayi shi ɗaya bayaso ana samun farinciki?, washe baki yayi, kafin yace "haba (SaudatatulBash) sunan da nayi miki laƙabi dashi kenan, ai duk wannan ba damuwa bane, zan sa ki soni sosai da sosai, sannan nayi miki alƙawari idan munyi aure da sati ɗaya zamu tafi yawon shakatawa acan zaki fi sakewa, sai ƙasar da kikeso nan zamuje" ita dai jinsa take, abu ɗaya wanda ta ƙudurewa zuciyarta shine, idan ma ta tayar da hankalinta ba fasa auren za'ayi ba, tasan halin Dady sarai idan har ya sawa zuciyarsa zai yi abu to babu makawa sai ya aiwatar yake jin daɗi, shi yasa ta ƙudurewa zuciyarta Tata ƙaddarar kenan babu inda zata yi, dole ta rungumi ƙaddara, koda ta gaji da surutansa, ta ce masa, "zan koma gida inada aiyyuka da yawa" Washe haƙora yayi kana yace "eh lallai kam nasan kinada aiyuka sabda gobe I War haka kina gidana" wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokareta, ta fito ba tare da ta jira maganar da zai ƙara yi ba, "Lokacin da ta ji alamun buɗe get tayi tunanin Dady ne yake shirin fitowa, sai taga babu kowa, Da sauri ta buɗe get ta shige, koda ta shiga masu aikace-aikace dangin Dady sai guɗa suke yi mata, sam baya mata daɗi sai takejin inama Allah zai ɗauki rayuwarta ta huta tsabar takaici, ko da ta dawo kai tsaye ɗakinta ta wuce, acan ta sami Momy tana ta kuka, duk a tunaninta ita kaɗai ce wannan auren be yiwa daɗi ba, ashe har da mahaifiyarta, cikin raunin zuciya tace "Momy kwata-kwata bana ganin Anam ko a WhatsApp ne fa, Anam ɗin da ko kwana ɗaya bamayi bamuyi magana ba, cikin suɓutar baki Momy tace "shikenan na rasa ki Anam, shikenan Anam" tai maganar tana sake rushewa da kuka mai tsuma zuciya, da sauri Saudart ta riƙe hannun Momy, itama ta fara kuka, cikin muryar kuka tace "Momy me kike nufi? mutuwa tayi ko me?" Momy ta toshe bakinta da hannunta sabda bata so Saudart ta fahimci komai ba, bata son ta banƙaɗo ɓoyayyen sirrin da suka birneshi tun shekaru ashirin da biyar da suka wuce, ko momy ta hau girgiza kai alamar "a'a" Saudart kam kuka ya ci ƙarfinta, ta sake cewa "Momy idan na rasa Anam shikenan bani da wata abokiyar shawara Momy acan kenan ta mutu, "Saudart kiyi hakuri Please Anam tana nan kuma cikin ƙoshin lafiya babu abinda ya sameta, nidai ina roƙonki kiyi ta yi mata adu'ar kariya daga azzalumai nima ina nan inayi mata, sannan wannan auren da mahaifinki yake shirin yi miki kiyi hakuri, babu inda zanyi, ƴan uwana ma basu isa suyi wani abu ba, shiyasa babu wanda na sanarwa walhi, duk da nasan yin hakan babban laifi na jawo wa kaina, amma idan na gaya musu komai yana iya faruwa, idan kika riƙe addini walhi bazaki taɓe ba, Ubangiji zai ci gaba da duba lamuranki" Saudart ta rungume Momy suka sake fashewa da kuka, sallamar Dady ne ya katse musu kukan nasu, kowacce tsoro ya shige ta, cikin nuna bai ma damu da kukan da suke yi ba, yace "Zainab bazan dai na gaya miki ba, idan har Saudart ta tafi gidan mijinta batayi masa biyayya ba, to akwai sa hannunki" Momy ta zaro idanu, lokaci ɗaya ta ji gidan nasa ma ya fitar mata a kai, tunda ya siyarda farincikinsa, to me zata zauna tayi, ya nuna kuɗi sun fiye masa matarsa da ƴa'ƴansa da komai ma, baya kallon komai sai dukiya, Wannan karon ne First time da Momy ta mike tsaye cike da ruwan masifa tace "nagaji da cin mutuncin da kake yi min, wallahi wannan karon kam bazan jure ba, ka sauwwaƙe min kawai, kaga idan na koma garinmu, sai ka sauya mata layi saboda kar in kashe mata aure, idan har da ban so tayi maka biyayya ba, ko kallon wannan tsohon ma zatayi ne?" Momy ta fice masa a giya, ta nunar masa da fushinta fiye da tunaninsa, sanin kansa ne, idan har Momy ta cire abu a ranta, ta cire kenan cikin sigar lallashi ya fara magana "ke Saudart jeki ɗakin momynki zamuyi magana.. Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*       🪻🪻🪻     Mom Islam Domin samun more pages kuyi following ɗina a Arewabook danna blue link👇 https://arewabooks.com/u/momislam11 Page 39-40 Saudart tana fita, Momy ta miƙe, cikin ɓacin rai tace "walhi tun wuri ka gayamin gaskiyar magana, ina Anam ko itama ka siyar da ita ne?" Cikin siyasa da tausasa harshe yace "ai shine nace ki zauna inyi miki bayani" Badan zata karɓi uzirinsa ba ta zauna tare da ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, tana karkaɗawa,  Ya fara magana yana wani marairaice murya kamar almajiri, kai kace ba shine yanzu ya dinga surfa bala'i ba, "Zainab kin tambayeni Anam nace miki tana can makaranta sai sunyi hutu zata dawo" Momy ta taɓe baki tare da cewa "hmm, to mai yasa wayarta baya shiga?" Dady yayi gyaran murya kafin yace "wannan kuma ina tunanin wayar ce ta samu matsala" cikin ɗaga murya Momy tace "kafin ku tafi ai sabuwar waya ce a hannunta, kana tunanin wayar 1 million har ta lalace?" Cikin sassauta murya yace "na gaya miki ki daina ɗaga murya mutane zasu ji maganar da muke yi" yana maganar ne zufa na karyo masa, "kin gane ne?, ai lokacin da muka sauka sai aka samu matsala wayar tata sai ta faɗi mota tabi ta kai, to shine kika ga bakyasamunta" Gabaki ɗaya yanayinsa da inda yake furta magana sam beyi kama da mai gaskiya ba, Ta gaji da sauraron labarin ƙanzon kuregen da yake bata, bata jira ya sake magana ba tai ficewarta, kai tsaye ɗakinta ta wuce, nan ta samu Saudart tana ta rusa kuka har idanunta sun kumbura sosai, da kallon tausayi ta bita, kana ta jingina da bango tana nazarin inda zatayi ta samowa rayuwarta mafita, ta sani idan har danginta sukaji wannan labarin babu makawa sai sun ɗauki hukunci mai tsauri, sannan ranta zai yi matuƙar ɓaci, sabda harda laifinta, idan da ace tun da tariga da ta ɗauki mataki da duk hakan bata faruba, kukan ta take ƙoƙarin tarewa da rafin hannunta ne ya kufce mata, lokaci ɗaya ta saki wani numfashi mai tattare da tsantsar tashin hankali, sosai Saudart ta tsorata, ga shi bata son dangin Dady su san halin da suke ciki, da sauri ta buɗe ƙaramin fridge ta ɗauko ruwan gora mai sanyi ta yayyafa mata, cikin hukuncin Ubangiji sai ga shi ta farfaɗo, tare da sake nisawa kamar inda tayi lokacin da zata suma, Murmishi Saudart tayi, wanda hawaye kuma yake zuba a idanunta, gefe ɗaya tana murmishin momynta ta farfaɗo, gefe guda kuma tana kukan auren dolen da Dady zai yi mata, Wunin ranar dai a ɗaki suka yi shi, sallah ne kawai yake tayar dasu, acan harabar gidan kuwa dangin Dady da suka zo kwanansu biyar sai gulmar Momy suke yi, wasu suce tana yiwa yarinyarta baƙinciki da shiga gidan daula, wasu suce zasuyi saki na dafe, shiyasa kaf dangin Dady da suka karanci halin da ake ciki, suka kama part ɗin su da ban a cikin gidan, itama momyn bata shiga sabgarsu, Ƙarfe 9:pm Dady sai juyi yake yi a gado tunani iri iri, har ya fara zargin kansa, yasan bai kyautawa Saudart ba, amma babu inda ya iya, dole ya amince ta auri abokinsa idan ba haka ba, shi kansa zai iya shiga tashin hankali sosai, Gefe guda kuma lamarin Momy ya fara bashi tsoro, saboda tana gaf da ƙure masa gudu, duk wasu kalamai da zai yi mata sun ƙare ya rasa da wacce kalma zai yi mata magana domin ya kare kansa, har zuwa ƙarfe 10:30pm yanata juyi, tashi yayi ya nufi bedroom ɗin Momy, koda ya shiga babu kowa, yayi tunanin ma tana toilet ne, har ya zauna ya kai kusan 30 mints baiji motsin kowa ba, daga ƙarshe dai ya fito, tsayawa yayi tare da rungume hannayensa a ƙriji, kana ya fara tunanin inda zai dubota, dan yasan idan ma ya kirata ba ɗagawa zatayi ba, tunanin ya duba ɗakin Saudart ne ya faɗo masa, da sauri ya nufi hanyar ɗakin Saudar ɗin, Ko da ya tura ƙofa, cikin sa'a ya hangota, ta rungume Saudart kamar wata jaririya, sai da ya tsaya ya gama ƙare musu kallo basu sani ba, kafin ya ci gaba da tafiya a hankali ya shigo ɗakin, ciki-ciki yayi sallama inda babu mai jinsa, domin zuwa yanzu jikinsa yayi sanyi, hamdala yayi, da yaga Saudart ɗin ma tayi barci, ya matsa kusa da Momy kana ya ɗaga Saudart daga cinyar Momy ya kwantar da ita a saman bed, Momy dai bata ko ɗago kai ta kalleshi ba,  cikin tausasa harshe yace "dan Allah Zainab ki zo muje ɗakina ba danni ba dan Allah" Yai maganar yana kamo hannunta, miƙewa tayi, har yanzu bata ce dashi komai ba, tana dai kallonsa kawai, sbda itakam yanzu mamaki yake bata gami da tsoro, sabda tsoransa takeji sosai. Bayan sun shigo bedroom ɗinsa, ya zaunar da ita a saman bed kai kace ƙaramar yarinya, ya je yayiwa ƙofar key wai duk sabda kar ta fice, ya durƙusa a gabanta harda kuka ya fara magana "Zainab nasan kin rufa min asiri, inason ki sake rufamin dan Allah Zainab ki fahimceni, duk wata fafutuka da nakeyi domin muji daɗi nakeyi, Zainab idan har kika tona min asiri me kike tunanin zai faru, zagi zato fargaba, duka zasu shigemu, amma idan kika rufamin asiri tabbas nikuma zanyi miki halarcin da kaf maza kafin a samesu sai an tona, Zainab a yau ki faɗi duk wani abu da kikeso a duniya wallahi tallahi sai nayi miki shi, amma fa kiyi hakuri, yau bazan ɓoye miki komai ba, Zainab ko hakan zai zamo silar rabuwata dake" Momy ta fashe da kuka, sbda ji take kwanyarta kamar zata tarwatse tsabar tashin hankali, Dady ya ci gaba da cewa "Tabbas Anam bata gurina, tana gurin ƴar uwarta Hussaina, walhi Zainab na rasa mafita ne, kuma kinsan tun dama munyi alƙawarin idan kin sake aihuwa dole zan kai musu ya zama biyu, Zainab yanzu ko da kin sake aihuwa babu mai taɓa miki yaranki ko ɗari zaki haifa" da wannan kalaman ya sace zuciyar Momy ta biye masa, sannan ta share hawaye, ya rungumeta yana yi mata kiss, "akwai alƙawarin da nakeso kayimin Habiby, idan har ka cika min alƙawari, nima zan sirrinta komai naka, Na farko shine ka yarda bazaka yimin kishiya ba, na biyu kuma inaso a fasa auren Saudart da wannan tsohon" da sauri Dady ya ware idanu tare da cewa "Zainab alƙawari ɗaya zan iya yi miki, bazan ƙara aure ba har abada, amma batun auren Saudart wallahi bazan iya ce komai ba, saboda wallahi tallahi, wannan mutumin da kike gani ciniki mukayi dashi" momy ta tashi a firgice, tare da dukan ƙirjinsa idanunta sunyi jajir ta cakumoshi tana cewa "cewa za kayi itama saudart ɗin ka siyar da ita kenan?" Tai maganar tana sake bugar ƙirjinsa,  "da na siyar da ita ai da ban bawa wani aurenta ba" Dady ya faɗa yana ƙoƙarin ƙwace riƙon da Momy tayi masa, "Wannan duk shirme kake faɗi, karfa ka mance sukenan min Saudart da ƴar uwarta sai Anam, ga shi har yanzu Allah bai bani wani cikin ba, gaskiya ka cuceni walhi tallahi nayi nadamar aurenka, kawai ka sauwwaƙe min in tafi gidanmu momy tai maganar hawaye Masu zafi suna bin kumatunta, shiru yayi bai ce da ita komai ba, yana kasa yi mata bayani inda zata gane, daga ƙarshe dai yace "Zainab ki sakeni walhi tallahi yau ɗin nan bazan ɓoye miki komai ba" momy ta juye masa fur taƙi sakinsa tace "tun ɗazu kake cewa bazaka ɓoyemin komai ba, nifa yanzu tsoronka nakeji wataran ni zaka bayar a baka dukiya, kaga kuwa idan ina gidan iyayena babu abinda zai sameni, Dady yace "wallahi tallahi Zainab tunda na aureki ban taɓa tunanin rabuwa dake ba, har yanzu ina sonki, duk abinda kikaga inayine saboda farincikinki, Zainab abinda baki gane ba, walhi kuɗi sune masu ƙarawa ɗan adam daraja kinga dole mu nemesu, ke kanki bazaki iya rayuwa a gidanku ba, a halin yanzu, bance baku da shi ba, kunada kuɗi dai-dai gwargwado sai dai bakai inda nakeda shi ba, inada tarin dukiya fiye da tunanin mai tunani, sannan a halin da ake ciki ma zaɓen da za'ayi insha Allah, zan tsunduma neman shugaban ƙasa saboda har nayi rijistar, momy ta waro idanu "sai kuma ta fara tunanin idan har ta sake ta rabu da Dady tabbas, bazata zamo First lady ba, lokaci ɗaya ta fara hasaso rayuwar da zasuyi a lokacin da irin muƙamin da Dady zai rike da kuma taurarin da zasu dinga samu idan har hakan ta kasance, kawai wata zuciyar ta faɗa mata ta rungumeshi, ai ko ta rungumeshi tare da sake fashewa da kuka, "Habiby kaine duk abin da kake yi baka yin shawara da kowa, amma nidai karka bari Anam taje gurinsu" Dady yace "kash Zainab da wane yare kikeson in dinga yi Miki magana ne? Anam tana gurinsu, amma insha Allah zan sanya a yi ta roƙon Allah har Hussaina duk zasu dawo, duk dai da wannan daɗin bakin ya gama yaudareta kana ya siye zuciyarta da maƙudan kuɗaɗe yace taje ta rarrabawa mata mazauna gida irin waɗanda basa sana'a, "wow ta faɗa idanu duk sun kumbura tsabar kuka, sai kuma tace "to maganar Saudart shiɗin dai zata aura ko?" Eh mana, biliyan goma ya bani, saboda yace yana mutuwar sonta fiye da tunani, walhi saudart zataji dadin zama dashi, ai bawai girmansa zata aura ba," momy ta sake rungume Dady sbda tsantsar so da ƙaunarsa tana daɗa ratsa zuciyarta. Ni Ko nace kuɗi masu gidan rana🤔. Bari mu waiwaya gurin haɗaɗɗen saurayi mai ji da naira. Bashi da alaƙa da ita, dan haka ko da suka bar gidan bai cigiyesu ba, sabda dama ba ƙaunar zamansu yakeyi a gidan ba, Zaune yake a office, yana shan ice cream da chocolate sai wani lumshe idanu yakeyi, ga dukkan alamu yana jin daɗin yanayin da yake ciki, nocking ɗin da akeyi ne ya sa shi ɗago kai tare da sake lumshe idanu, kafin yace "come in" Muhammad ne ya shigo, yana sanye da shadda sky blue, sai zuba ƙamshi yakeyi, koda ya ja kujera ya zauna, ya zubawa Ma'aruf idanu cikin zolaya yace "yau kuma taka ƙaddarar anan ta sauka na shan kayan zaƙi?" "Idan kai ka siya min ka kwashe mana" Ma'aruf yai maganar cike da jin haushin Muhammad, Shi fa ya mugun tsanar Muhammad saboda munafurcin da yake yi masa a faɗarsa, Muhammad yace "mai da wuƙar kaga dama nazo in gaya maka ne, next week aurena insha Allah, ma'aruf ya washe haƙora kai kace ba shine magana take gagararsa ba, sosai kyawawan fararen haƙoransa, masu kyau da ɗaukar hankali suka baiyyana, dimple's ɗinsa suka loɓa, ya miƙa wa  Muhammad hannu suka tafa, kafin yace "wai dama kana nan kana soyayya ko? ɗan yaronka da kai" Muhammad yace "to me zan jira nifa bazan iya rayuwa babu soyayya ba, malam soyayya duniya ce, kai daga ƙarshe ma idan banji Muryar ta ba bana iya barci itama haka"  Ma'aruf ya jinjina kai yana murmishi kana yace "kuma ka tabbatar da bata iya barci itama ɗin" eh mana" wato dai bakasan menene so ba, bakasan daɗinsa ba, sannan baka san zafinsa ba" Ma'aruf yace "duk daɗin soyayya bai kai ice cream da chocolate ɗin da nake sha daɗi ba...! Kuyi hakuri jiya baku samu update ba. Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ Follow me on TikTok 👇 Page 41-42 Muhammad ya kwashe da dariya, shikam har ga Allah Ma'aruf yana birgesa, saboda babu ruwansa da kula ƴan mata, gefe guda kuma ya fara tunanin kodai yana da wata matsar ne?, Allah shi ya barwa kansa sani. Sallama yayi masa kana ya wuce, bayan tafiyar Muhammad Ma'aruf ya fara tunani, "to ma meye abin so a rayuwarnan in banda kasuwanci?" Yayiwa kansa tambaya, kawar da tunanin nasa yayi ta hanyar danna wayar tafi da gidanka, ɗaya daga cikin ƴan aikin Company ɗin ce ta shigo, cikin girmamawa ta gaishe shi, cike da shan ƙamashi ya amsa, kana ya miƙa mata cover shoe ɗinsa, already tasan me za'ayi dasu, tunda ƙa'idarsa ne, kullum 3:pm nayi zai sa akai a goge masa, tana fita daga office ɗin Ma'aruf sukayi kiciɓis da Layla, "Ah Sara ina zuwa?" Layla ta jefo mata tambaya, Sai da Sara ta waiga taga babu mai tahowa, cikin ƙasa da murya tace "aikin da aka saba yi, gugan takalmi mtswww" Layla ta karɓi takalmin kana tace "kinga koma gurin aikinki zan kai a goge sannan zan kai masa har office" Sara tace "kin tabbata?" "Eh mana" Layla ta amsa mata. Koda yaushe mai polish ɗin takalma yana zama a ƙofar get ɗin company, cikin amincewar shugaban Company wato Ma'aruf, Wacece Layla? Layla na ɗaya daga cikin ma'aikatan da ake ji dasu a wannan company, sosai take bada gudunmawa, hakan yasa take sake jajircewa, gurin ganin an samu sauye-sauye, hakan yasa ta samu shiga a gurin uban gaiyya wato Ma'aruf, duk da hakan ba wai ya sake mata fuska sosai bane, kawai yana yawan karbar shawarwarinta, idan har ya ga akwai nasara a ciki. Sara kam bata kawo komai ba, sabda ita kam sam bata wani son shishigewa Ma'aruf, duba da irin halinsa na miskilanci, ita dama ba wata bace a Company face mai gogo-goge, Sara Christian ce ba musulma ba. Cike da shauƙi Layla ta kai polish ɗin takalmin Ma'aruf, ko da aka gama, rungumesu tayi a ƙirjinta, ji takeyi kamar Ma'aruf ɗin ne yake tare da ita, tana tafe tana zancen zuci har ta kawo ƙofar office ɗinsa, lumshe idanu tayi tare da jan dogon numfashi, aduniya Ma'aruf yana birgeta ko wane namiji ta gani komai kyawunsa bazata iya haɗashi da na Ma'aruf ba, ko mai yasa oho, sai da ta kalli fuskarta a jikin wayarta kafin ta buɗe hand bag ɗin dake maƙale a kafaɗarta ta ciro powder ta sake shafawa, kana ta ciro lipstick shima ta goga a lips ɗinta, sannan ta ɗauko turare mai sanyin ƙamshi ta fesa, kafin ta mayar dasu jaka, bata sake gyara lips ɗinta, kafin tayi nocking tana waigen ko akwai wanda yaga time ɗin da take makeup, "yes come in" Ma'aruf ya bata izinin shiga duk da bai san cewar ita ce ba, a hankali ya ɗago idanunsa ya sauke su a na Layla, tana rungume da takalmansa har ta ƙaraso cikin faɗaɗa murmishinta tace "Sir Barka da wannan lokaci" "Barka" Ma'aruf ya faɗa a taƙaice. "Sir zan iya zama?" tai maganar cikin zaƙaƙa muryarta, "eh zaki iya" Ta ja kujera ta zauna tare da zuba masa idanu, shigo gabaki ɗaya hankalinsa baya gurinta, sbda rubuce-rubuce yakeyi, sai da ya ɗau tsawon mintoci kamar 20mints kana ya ɗago yana kallonta wanda tayi nisa a hasashen da zuciyarta ke ƙirƙiro mata, "zaki iya fadar abinda ya kawo ki" Ma'aruf yai Maganar ya miƙa hannu zai karɓi takalman da ke hannunta, miƙa masa tayi tare da narkar da idanunta, lokaci ɗaya ta fashe da kuka tare da ficewa a office ɗin, sam baya ƙaunar jin sautin kuka ko wane iri ne, hakan yasa kukan da ta fara yi ya shige masa rai, yanada numberta, ya danna tare da cewa "mai yasa kika tafi baki faɗi abinda ya kawo ki ba?" marairace murya tayi, cike da shagoɓa kafin tace "uhm dama inason faɗa maka wata magana ne" Ta ƙarashe maganar tana sake sakin kuka, "Ya Salam" Ma'aruf ya ambata da daddaɗar muryarsa mai ɗauke da daɗin amo, kizo office yanzu sbda ina shirye-shiryen tafiya gida, Dama wannan lokacin take jira, Ta tattaro kayanta na tafiya gida, kai tsaye ta wuce office ɗin nasa, yana zaune a hakimce kamar ɗazu, ta ƙara so tana cewa "Barka Sir" gyaɗa mata kai yayi tare da yi mata nuni da gurin zama, koda ta zauna zuba masa idanu tayi, kamar ɗazu da ta shigo, dama shi kam ba ita yake kallo ba, sabda shi ɗin ba irin mutanen nan bane da zasu ƙurawa mutum idanu har su gano kyawunsa da muninsa, "Ina jinki" Ma'aruf yai maganar yana rufe files ɗin da ya kammala cikewa, "Uhm dama..dama..." Ta fara inda-inda kamar wata marar gaskiya. "Dama me? kiyi magana kina ɓatamin lokaci!!" Ma'aruf yai maganar cikin daka tsawa. Sosai take jin tsoronsa, sai dai soyayyarsa ta rufe mata idanu, Layla tace "Dan Allah kayi haƙuri Sir, kasan akwai wata halitta da Ubangiji yake jarabtar ɗan Adam da ita, Ubangiji yana sawa bayinsa wani abu..." "Ke dalla ni kimin magana inda zan fahimta kin wani tsaya yimin wa'azi ko nace miki banyi islamiyya bane?" Ya ƙare maganar yana wani haɗe rai alamun ransa ya ɓaci, "Okay Sir, dama na jima ina ɗawauniya da doyayyarka, dan Allah ko baka sona kace..." Tunda Layla ta cigaba da magana yake sauraronta, tunda yaga ta sauya layi ya sake daka mata tsawa a karo na biyu, Cikin sexy voice yace "oh kema ashe irinsu ce?, gaskiya kin cini game da har na tsaya jin wannan labarin ƙanzon kuregen da kikeyi min" Ya buga table da ƙarfi, kana ya sake cewa "tashi ki ficemin bana son ƙara ganinki a office ɗina" Ko da yayi maganar tana zaune, ta ɗora gwaiwar hannunta a saman table ɗin, tayi tagumi, tana daɗa zuba masa idanu, bata ma san yana yi ba, belt ɗin wandonsa ya ciro, kana ya fara nannaɗewa, sai a lokacin ta ɗago kai, sam batayi tunanin komai ba, sai gani tayi yana shirin kai mata duka, ta miƙe tsaye, kafin ta kai ga guduwa ta faɗi a gurin timmm, duk da haka nufo inda take yakeyi, cikin zafin rai ya bita da gudu, amma ta tashi itama ta ari na ƙare, kayanta ko dama suna maƙale a jikinta, dama ta ɗibosu ne, idan zai wuce gida ya sauketa a anguwarsu tunda duk hanya ɗaya ce. Rai a ɓaci ya dawo ya zauna sai huci yakeyi, a fili yace "wai ma raini ne yasa wannan shegiyar yarinyar shigomin office tana gayamin maganganun banza ko ya akayi?" Tunani ya farayi, duk rashin kula ƴan mata da bayayi sai da aka sami mara kunya ko?, Time bai ƙarasa ba, ya haɗa kayayyakinsa, already ya danna wayar tafi da gidanka, Sara ta shigo tayi masa Barka, ya miƙa mata kayayyakin da zai tafi dasu, ta kai masa mota, kana shiga ya fito, cikin takunsa na ƙasaita, Wacece Layla? Alhaji Adam shine mahaifin Layla, Hajiya Rashida ita ce mahaifiyarta, Layla na kiran mamanta da Mamy, baban kuma tana ce masa Abbie, iyayenta sun kasance masu rufin asiri, sai dai wata jarabawa ta sami Abbie, bashi da dukiya kamar da, filayen da ya mallaka duk sun dulmiye, ada yana sana'ar siyarda motoci, Allah ya kawo tsautsayi ya gifta, yanzu dai yana sana'ar siyarda biredi, wato rarrabawa mutane biredi kama daga masu shayi da masu shaguna, Ta haka yake ciyar dasu Layla harma da tufafin da kuma uzurorin rashin lafiya, Layla tayi karatu sosai inda ta karanci business, alhmdulilah shine taimakonta, a koda yaushe tana tura takardar neman aikinta a website, cikin hukuncin Ubangiji Allah ya taimaketa, Muhammad ya gani, wato abokin Ma'aruf, sai da yayi mata magana kana suka tattauna, sannan ya zo ya sami Ma'aruf, cikin tausasa kalami, domin Muhammad ya tausayawa Layla sosai da sosai, ko da Layla ta zo tayiwa iyayenta albishir da samun aikinta, duk da a zahiri bata tabbatar ba, sukayi ta addu'a akan Ubangiji ya taimake su, cikin hukuncin Allah, sai ga Muhammad yayi mata albishir da Ma'aruf ya amince, sosai tayi murna tayi tsalle tsabar jin daɗin albishir ɗin da Muhammad yayi mata, Dalilin da yasa ta samu karɓuwa a Company shine, tanada tunani mai kyau tare da iya sarrafa computer cikin sauƙi tare da binciko muhimman abubuwa, Tunda tayi tozali da kyakkyawar fuskar Ma'aruf ta rasa tunaninta, duk da cewa kwata-kwata bata wuce 6months a Company ɗin ba, abubuwan da suke yi a Company sune. Sarrafa Taliya Macaroni Shinkafa Gishiri Sannan kuma sunada gidajen abinci a Abuja har ma da Legos Enugu da Hotel babba a nan Abuja da Kano, Sunan da suke amfani dashi a duk wata kafa tasu shine, M.M Food delivery service) shine sunan gidan abincin su, hotel kuma M.M Central hotel, company ɗin su kuma F.D INDUSTIRIES,tun bayan rasuwar mahaifin Ma'aruf ya ƙudurce wa kansa riƙe muƙamin da mahaifinsa ya riƙe, ta fannin kasuwanci da tattalin dukiyarsu, lokacin da mahaifinsa ya rasu F.D INDUSTIRIES company, ne kawai suke dashi, amma yanzu sunada hotel's da food delivery shima har biyu, bayan nan sunada filaye da gidaje, har da wasu masana'antun ma a ƙasar waje. Driving yakeyi, ransa a ɓace, wannan yarinyar ta ɓata masa rai, ga shi be iya fushi ba, ko da ya iso bakin get da ƙarfi ya danna horn, mai gadi ya buɗe cikin girmamawa yana ɗagawa uban gidan nasa hannu, gyaɗa masa kai Ma'aruf yayi, kana ya shige ciki, bayan yayi parking ya fito tare da ɗibar kayansa ya wuce ciki, a hankali ya tura ƙofar door ɗin parlor kana ya kutsa kai ciki bakinsa ɗauke da sallama, kai tsaye upstairs ya hau yana ɗan gudu gudu, har ya iso ɗakinsa, ƙare wa ɗakin kallo yayi, kafin ya nemi guri saman beautiful couch ya zauna, "ya Allah" ya ambata jikinsa duk gajiya, hamma ce ta taso masa mai cike da ma'anoni iri-iri, ga yunwa ga barci ga gajiya, saboda tsabar gajiya, yana jin Bama zai iya shiga kitchen ba, shawarar samo ƴan aiki yayi wanda zasu dinga yi masa girki gyaran gida da wanki sabda wanki a washing machine ɗin ma wahala yake bashi, da wannan tunanin ya ɗan gyara zama kana ya kwanta saman couch mai zaman mutum uku, nan da nan barci mai daɗi ya ɗaukesa, Tun 5:pm yake barci har aka kira sallahar magriba bai san an kira ba, A hankali ya fara jin sanyi na shigarsa, sabda iskar da akeyi, tashi ɗaya gari ya haɗa hadari da alamun ruwan sama zai sauka, sosai gari yayi sanyi lokaci ɗaya ya fara ƙudundunewa, a hankali ya buɗe idanunsa, da sauri ya tashi zaune yana mutsike idanu, agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa ya kalla yaga har ƙarfe 7:40pm, cike da mamaki ya kunce agogon tare da wucewa toilet, yai alwalah kana ya fito, a parlonsa ya shimfiɗa sallahya kana ya kabbara sallah, bai tashi a gurin ba har sai da akayi sallahar isha'i, kana yayi addu'oinsa kafin ya ninke sallahyar sannan ya wuce bedroom ɗinsa, sam bazai iya yin wanka ba, ya rage kayan jikinsa ya bar iya farar singileti, ya ciro white sleek jallabiya, ya sanya, kana ya ɗauki wayoyinsa, da eyepiece ya fito parlonsa, fridge ya buɗe yaga iya Hollandia da yoghurt da Five alive ne a ciki, sam bazasu yi masa maganin yunwar dake damunsa ba, badan ya so zuwa gidansu Hajiya ba, ya fito harabar gidan, kana ya buɗe get, jin ƙarar buɗe get ɗin yasa mai gadi fitowa da gudu, ganin uban gidan nasa yasa ya gaishe sa, yana komawa ciki, kai tsaye ya nufi gidan Hajiya, nocking yayi a bakin get ɗin, dama idan baku manta ba, abaya nayi muku bayanin katangar gidan Hajiya tana jinkin katangar gidan Ma'aruf, bayan an buɗe masa get, mai gadin ya gaishe sa ya amsa kana ya wuce ciki, kasancewar kafin mutum ya kai ga shiga cikin gidan akwai tafiya tunda gidan nada daɗi da tsayi sosai, yau kam tafiyar tayi masa nisa, sbda har ya fara tunanin dama ace da mota yazo ba da ƙafa ba, yana isowa ƙofar parlor yai sallama, Hajiya da anty Jamila suna zaune sun ta sa kuɗaɗe a gaba, sunata lissafi, ƙarasowa yayi kana ya zauna kusa da Anty Jamila, cikin marairaice murya yace "anty yunwa nakeji" yai maganar yana shafa cikinsa, ajiye kuɗaɗen hannunta anty Jamila tayi kana tace "Hajiya karki hada da waɗannan lissafinsu daban yake, anty Jamila ta miƙe kai tsaye sashen da ƴan aikin suke ta je, ko da yake Dija kam an koreta bayan tafiyar ta ma Hajiya sai da tayiwa anty Jamila faɗa, duk da hakan dai ba'a dawo da ita ba, hajjo ta ƙwalawa kira, cikin sauri ta zo tare da durƙusawa a gaban anty Jamila, kafin tace "Hajiya gani" Please ki shiga kitchen ki dafawa Son indomie and vegetables, karkisa masa busashen kifi, saboda baya so, kawai ki ɗauko masa kunun aya mai sanyi, "to" ta amsawa anty Jamila, kai tsaye ta wuce kitchen, akwai ruwan zafi a flaks hakan yasa ta samu sauƙin girkin, ba wani long time ta ɗiba ba, ta kammala, kana ta juye a kula, kana ta buɗe fridge ta ɗibo kunun aya mai sanyi guda biyu, ta ɗauko fork da plate kana ta fito a kitchen ɗin ta nufo hanyar da zai sada ta da parlon Hajiya, sallama tayi daga bakin ƙofa su Hajiya suka amsa, shiko Ma'aruf ɗin yana daga kwance a saman kujera yana danne danne a wayarsa, ƙarasa shigowa hajjo tayi tare da ajiye abincin a saman table ɗin dake tsakiyar ɗakin, tace "anty an kammala" Hajiya tayi mata sannu" ta amsa da "yauwaa" kana ta wuce. Saukowa yayi kana ya je ya ɗauko table ɗin cak ya ajiye a gabansa, ya zauna a saman kujera mai zaman mutum ɗaya, bayan ya buɗe kular yai bismillah kana ya fara cin abincin, har sai da ya cinye tass sannan ya kora da kunun aya mai sanyi. "Abin kunya ace kamar ka, kana wuni da yunwa, ta hakan zaka gane cewar mata ma rahama ce a gareka, bai ce da ita komai ba ya ɗora ƙafafunsa a saman table ɗin yana shafa sumar kansa, Anty Jamila tace "Hajiya kawai ki zuba idanu insha Allah yana nan da budurwarsa... Ya katse wa anty Jamila maganarta, kafin yace "anty Jamila har yanzu kun kasa ganewa, idan har mutum ya fara soyayya ya shiga uku, bashi da lokacin kansa ma bare na aikinsa, kinga hakan ko bazai yiwu ba sam, har yanzu kun kasa fahimtata". Ya ƙare maganar yana miƙewa alamun fita zeyi, Hajiya tace "Allah ya shiryeka" anty Jamila ta amsa da cewa "Amen" ****** Kwanci tashi asarar mai rai Talatu ta fara zuwa school an gama mata komai na shirye-shiryen zuwa, sabda komai Arman ne yayi, ya hana anty Tasneem ta bada ko nera biyar a cewarsa shima yana son ya samu lada, da safe drivern gidansu ne yake kaita, zuwa ƙarfe 5pm shi yake zuwa ya ɗaukota sabda a lokacin yake tashi daga gurin aiki, A aji huɗu aka sata primary 4 next year sai ta rubuta jarabawar fita, Yau ma kamar kullum, tana zaune ita kaɗai a harabar makarantar, saman wata kyakkyawar kujera tanata zuba idanu ta ina zai ɓullo, can dai taga mai gadi ya buɗe get, da sauri ta tashi ta fara takowa, cikin sa'a taga shine yake tahowa, har da ɗan gudunta, yana daga cikin mota yake ƙare mata kallo, tunda yake a duniya bai taɓa ganin ƴa macen da ta taɓa birgesa ba irin Aysha, komai nata birgeshi yakeyi, ƙaunarta har cikin ƙarƙashin zuciyarsa yake jinta, koda ta iso tana sanye da hijab guntu iya kafaɗa sai skirt iya guwaiwa, farar Safar da tasa ne ya kai mata har cinya, fuskarta ɗauke da murmishi lokacin da yake rage tsayin gilashin motar, tace "Yah Arman inata jiranka Allah yasa lafiya kowa ya tafi sai ni kaɗai" "Ƙanwata lafiya lau, ina lunch box ɗin naki?" Arman ya tambayeta yana buɗe mata gidan gaba, Marairace murya tayi, wanda shagoɓa ta zame mata sa bo da yinta a rayuwarta, tace "Mun makara bamu tashi da wuri ba, shiyasa ko breakfast banyi ba, anty dai ta bani 1k gashi a hannuna ban siyi komai ba" "Kai ƙanwata muje restaurant kici abinci, zama da yunwa fa babu daɗi" ya figi mota kana ya fice a makarantar, kai tsaye gurin cin abincin suka wuce kamar inda ya faɗa, bayan ya miƙa ATM ɗinsa aka miƙa masa list ya tambayeta ta bashi amsa, suka wuce wani guri mai kyau da kyawawan ciyayi masu ban sha'awa, wani sanyin ƙamshi ne yake kai wa Arman ziyara a hancinsa, in 1time ya fara jin kasala, idanunsa suka wani ƙankance, lokacin da aka kawo musu abincin tare da ice cream, Talatu tace "Yah Arman baka da lafiya ne, naga yanayinka duk ya sauya?" "Lafiya ta ƙalau kawai ina cikin wani yanayi ne" Yai maganar cikin cold voice ɗinsa, Jinjina kai tayi, ta ɗauki ice cream ɗin kana ta buɗe robar ta sanya ɗan ƙaramin cokalin robar ta fara sha, lumshe idanu tayi, cikin zolaya tace "yah Arman kasan me?" Saboda yanzu tana iya zama tayi hira dashi, Yace mata "sai kin faɗa" "Wlhi ice cream ɗin gurinnan yafi na wancan ɗinnan daɗi, gaskiya zan kai wa anty tsaraba" Arman yace "A'a, bazaki kai mata ba, kar ki sake ki gaya mata cewar munzo nan idan ba haka ba wlhi zata ɓata min rai, ko kuma kinason ɓacin rai na?" Inda yai maganar ya bata tausayi saboda yanayinsa ya mugun sauyawar ba kamar inda suka zo ba, ya ce mata "ba komai ne idan anyi ko na yi miki zaki gaya mata ba, yin hakan yana iya zamowa babban laifi ki kiyaye" "Insha Allah" tace masa, sai kuma tace "ka sha mana" "Uhm" ta tsinci kanta da cewa "in baka a baki?" Ya gyaɗa mata kai, karku manta Talatu bata san menene soyayya ba har yanzu, sabda haka ta faɗa hakan ne cikin tausaya masa ko bashi da lafiya ne, Ɗaukan robar ice cream ɗin dake gabansa tayi, kana tasa cokalin ta fara bashi a hankali yana sha idanunsa a lumshe, Allah kaɗai yasa halin da yake ciki, ji yakeyi kamar ya janyota ya rungumeta ko zai rage raɗaɗin da yake ji a zuciyarsa, tabbas soyayyar Talatu tana neman haukatashi, amma yayi alƙawarin bazai taɓa nuna mata gaskiyar hakan ba har sai ta girma ta mallaki hankalin kanta tasan menene SO, Abin mamaki ga dukkan tunaninta bazai iya shanyewa ba, sai ga shi ya shanye tass tasa Hankey ta share basa baki, shikam tuni ya kula duniyar tunani har wani ajiyar zuciya ya sauke, a hankali ya kai hannunsa saman nata, cikin sigar wasa yace "ƙanwata me yasa bakya yanke farce, kin fara zama ƴar gayu ko?" Ta cuno baki gami da cewa "anty ma ai bata yanke farce" dariya ma ta bashi, yace "wato kina koyi da ita kenan?" Tai murmishi, tashi mu tafi kar a ga kin daɗe" ta miƙe tsaye, a hankali ya matsa kusa da ita sun ɗan fara tafiya kafin su kai gurin motarsa, ya ɗagata ya goyata a baya, sai cewa take "yah Arman baka da lafiya dan Allah ka saukeni" shi kuma yana cewa "karki damu kin gaji da yawa" Sai da suka zo bakin mota kana ya sauketa, suka shiga ya tada mota suka wuce gida, bayan an buɗe musu get ya shiga yayi parking suka shiga ciki, anty Tasneem tana zaune a parlor ita da ƙanwar Junaid kasancewar duk hutu idan sukayi suna zuwa, to yanzu ita ta fita daga makaranta tazo tayi kwana biyu, aiko suna haɗuwa da Talatu suka ƙulla ƙawance, kasancewar Talatun bata da duhun kai, tun daga ranar suka kasance ƙawaye gunin sha'awa, sunan yarinyar Umaimah, amma ta girmewa Talatu, sabda takai 18yrs dan har tanada waya, tunda ta gano Talatun tayi zaman ƙauye ta fara sake ƙoƙarin wayar mata da kai, duk da cewar kafin ma ta zamo hakan sai da anty Tasneem tasha fama sosai da sosai, suna kwance a saman bed lokacin ƙarfe 9:30pm, anty Tasneem ta kwanta kasancewar tana son gobe ta tashi da wuri zataje anguwa, sukuma sunata hira, Talatu ta bata labarinta from AtoZ Umaimah tayi dariya, tare da cewa "yanzu duk wanda ya ganki wlhi ba zai ce kinyi zaman ƙauye ba" tayi murmishi, labarin saurayin da suka haɗu dashi a gurin shan ice cream ta bata, sannan tacewa "Umaimah harda number waya ya bata, Umaimah tace "dalla ki wanki Gara kawo number in sa miki a kirashi, ringing ɗaya ta shiga ya ɗaga tare da cewa "hello waye?"....! Alhmdllh hannu yayi sauƙi ga typing nan asha karatu lafiya da na yau dana gobe kinsan weekend bana posting sai aka samu matsala jiya banyi ba da shekaranjiya ciwon hannu nakeyi, masu Comments Nagode sosai mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ Page 43-44 toshe bakinta tayi da tafin hannunta, Umaimah tayi mata nuni da tayi magana mana, A hankali tace "ni ce Aysha" muryarta kaɗai ta isheshi, ba sai tayi masa dogon bayani ba, , a fili ya furta "godiya ga Allah da ya sake haɗani da kyakkyawar budurwa a karo na biyu, ya faɗaɗa murmishinsa kamar tana ganinsa, kafin yace "da fatan kina cikin ƙoshin lafiya, wlhi nayi kewar ganin kyakkyawar fuskarki, duk da dai gani na dake sau ɗaya ne, sai da na kasance a ko wane dare sai nayi mafarkinki, sannan sai na ɗauko hoton da nayi miki farkon haɗuwarmu, na rungume kana nake samun sassauci a zuciyata, "A halin yanzu nafi buƙatar ganinki akan inji muryarki" Umaimah ta raɗa mata, cewar "nima hakane" Ta faɗi maganar da Umaimah ta gaya mata, daga can ɓangaren yace "yaushe kike ganin ya dace in zo?" Zaro idanu tayi tare da cewa "taɓɓ so kakeyi anty tayimin duka ko?" Yai dariya mai sauti, kana yace "anty bazata dukar min ke ba" suna tsaka da firar tace "sai anjima karmu cinyewa mai wayar kuɗi" Babu komai, "ki tura min da account number zan sa miki kuɗi sai ki siyi waya." Ƙirjinta ne ya bada rass, ta dafe ƙirjin tana kallon Umaimah, Umaimah ta gyaɗa mata kai, Bayan sunyi sallama, Umaimah ta miƙa mata hannu suka tafa kafin tace "Aysha kin cika tsoro wallahi, ga dukkan alamu wannan guy ɗin yana sonki sosai, yanzu dai barin tura masa da account number idan ya turo sai muga wace irin waya ya kamata a siya" Talatu dai har yanzu tana cike da jin tsoro har yanzu, Bayan Umaimah ta tura masa da account numberta, tace "Aysha ki kwantar da hankalinki, idan har aka siya miki waya, zaki ƙara samun nutsuwa tare da farin ciki, Talatu ta dafe ƙirji a karo na biyu kafin tace "hmm Umaimah Wlhi ban san haka soyayya take ba, in one time kawai guy ɗin nan ya fara shiga zuciyata" Umaimah tayi dariya kana tace hmm yarinya ai ba komai kikaji ba, Wlhi idan kika fara soyayya bazaki iya yin wuni ba tare da kinji Muryar saurayinki ba" suna cikin hirar suka ji alert na dubu ɗari biyu, Umaimah tace "wow yayinda take duba saƙon, Nunawa Talatu tayi, kana tace "kinga gobe anty Tasneem zataje anguwa sai mu fita da wuri kafin ta dawo, Talatu ta dafe ƙirji sbda tana mamakin yan bariki basu damu da kashe kuɗi ba, idan da a ƙauyensu ne, duk wanda yake da dubu ɗari biyu ai yanada babban kuɗi, sai ta tuno lokacin da zasuyita faɗa ita da Gudidi akan Naira biyar, yau itace ta mallaki wadannan maƙudan kuɗaɗen?" Umaimah ta katse mata tunani sbda ta fahimci tunanin da takeyi, tace "ki kwantar da hankalinki, sannan ki tsarkake zuciyarki, soyayya babu abinda bata sawa a bayar Wlhi zuwa gaba ma zai iya yi miki kyautar da tafi wannan, to inaga ƴan matan da samari suke siya musu motoci Masu tsada kuma basu da tabbacin auransu zasuyi?, da wannan shawarar suka kwanta barci ya ɗauke su, bayan sunyi adu'oin kwanciya barci, Acan ɓangaren anty Tasneem ƙarfe 12:am ta farka daga barci, kasancewar ta kwanta da wuri, alƙawari ne ma koda yaushe idan har Junaid baya gida sai ta farka a dai dai lokacin, a hankali haske yake fitowa a jikin wayarta, tana mutsike idanu ta janyo wayar tare da karawa a kunnenta cikin sanyin murya irin ta mai barci tace, "Babyna, Kaine wanda ka dace da sarautar zuciya ta don haka na baka ita kyauta, Zan iya aiwatar da komai har idan ina jin kalaman ka masu sanyaya zuciya, Na yarda da kai na aminta da kai don haka na mallaka maka kaina" Daga can ɓangaren Junaid ya lumshe idanunsa in Cold voice ya fara magana "Ina fatan zaki ci gaba da kula min da kan ki har zuwa lokacin da zan dawo gida. Allah ya tsare min ke matata, ina son ki. Sonki kamar numfashine a gareni, taya zan dai na? Cike da shaukin SO ta janyo heart pillow ta rungume idanunta a lumshe ta, wani marairaice masa murya, tana shagoɓa tana cewa "gaskiya baby bazan iya sake jure muyi nesa da juna ba, NA KASA JUREWA, tai maganar hawaye na kwaranyowa a idanunta, sheshekar kukanta ne ya tayar masa da hankali, cikin tausasa harshe yace "Please ki hau online ina WhatsApp" yana faɗar haka ya katse kiran, Kai tsaye ta kunna data ta hau WhatsApp, yana online ɗin kamar inda ya faɗa, "Baby kin jefani cikin damuwa gami da tashin hankali, kin sani bana son jin sautin kukanki, amma kika fara whay?" In voice yake mata maganar, tayi masa video call idanunta sun jiƙe da hawaye, sosai yake ji a ransa kamar ya biyo jirgi ya dawo gobe, saboda ya rarrashi farincikin ransa, ya wani gyara zama dama yana sanye da sleeping dress ne, itama hakan, wando ne iya guwaiwa sai riga mai botir, "baby kaje ka kwanta sai da safe" tai maganar tana gyara gyalen da ta ɗaura a kanta, ina.. bazan iya koda runtsawa ba, matsawar ban ga kinyi murmishi ba" kodan hankalinsa ya kwanta, tayi masa murmishi tare da cewa "i love You baby" shima yace "love You too babyn baby" "Zuciya ta na cike da kewarki, zan samu sassauci ne kawai idan na ji ki a kusa da ni. Ki kula min da kanki har zuwa lokacin da zan dawo kulawarki ta dawo hannu na. Ina Son Ki" kana ya sauka online badan ya gaji da jin muryarta ba. Cikin farinciki ta kwanta tare da yin adu'ar kariya daga dukkan sharri, lokaci ɗaya barci ya ɗauketa, WASHE GARI Kiraye-kirayen sallahar asbha da ake yi ne ya sanya ta farka, tare da karanto adu'oi kamar kullum, tashi tayi ta ɗauro alwalah tayi raka'atanil fijir kafin ta kabbara sallah lokacin har an fara kiran shiga. Bayan ta idar ta yi adu'oi kana ta ninke prayer mat ɗin ta fito zuwa ɗakinsu Talatu, samunsu tayi suna sallah, tayi hamdala tare da wucewa kitchen, har masu aikin gidan su fito, suka gaisa ta ci gaba da aikinta, indomie tayi da ƙwai kana ta ɗibo dankalin turawa tana shirin ferewa, sai ga Talatu da Umaimah sun shigo kitchen ɗin, "anty good morning" suka faɗa cikin haɗin baki, "morning too" da fatan kun tashi lpy, suka amsa da lafiya lau anty, Talatu ta ɗauko dankalin Umaimah ta ɗibo musu wuƙa, da ruwa suka fara ferewa, bayan sun kammala suka miƙa mata, tayi musu godiya tana murmishi, a ƙa idar anty Tasneem bata taba bari ƴan aiki suyi mata girki, ko ya kai kala nawa ne, Bayan sun koma ɗaki suka fara planing ɗin anty Tasneem na fita suka zasu fice, da wannan shawarar sukayi wanka, Umaimah ce ta fara shiga toilet bayan ta fito Talatu ta shiga, ko da suka shafa mai Talatu ta ɗauko powder zata shafa, Umaimah ta karɓe tana cewa "ni zan yi miki makeup kinsan na karanci tsara kwalliya sosai" Talatu tayi murmushi cikin sigar zolaya tace "shikenan kin huta idan bikinki ya zo" suka kwashe da dariya, ƙarfe 8:30am, anty Tasneem ta shigo ɗakinsu tare da cewa "breakfast yana dinning ni zan wuce Please ku kula da gidan, "anty sai kin dawo" Suka faɗa cikin haɗin baki, Tana fita Umaimah ta ƙwalawa Talatu kira, kasancewar anty Tasneem ta bar mata sallahun ta miƙawa su Inna mai aiki abincinsu, bayan ta miƙa musu ta dawo ta samu Umaimah tana searching a jiji app, Umaimah taga Infinix hot 12 kuɗinta dubu ɗari da sittin da biyar 165.000, basu wani ɗau lokaci mai tsawo ba gurin shiryawa, dukkansu abayar suka saka, Talatu ta sanya baƙa mai adon duwatsu masu ɗaukar idanu golden, itakuma Umaimah ta coffee brown sleek itama mai adon duwatsu, veil ɗin sukayi rolling nashi, wow Masha Allah, sunyi kyau sosai, ko wacce ta ɗauki hand bag ɗinta, hand bag ɗin Talatu babu komai a ciki daga abin share fuska sai lipstick da powder shikenan, suka fito cike da salo da ƴan mata masu tashen budurci, har Talatu ta so tafi Umaimah iya taku, sai da suka je gurin su Inna masu aiki suka ce musu zasu je siyan kati, kana suka wuce harabar gidan, mai gadi ma yana ɗakinsa, motsin buɗe get ne yasa shi fitowa, yana ganin sune yayi musu Allah ya kiyaye suka wuce, basa son hawa motar gidan, sbda suna tsoron kar bincike ya biyo ta kansu wataran, shiyasa suka yanke shawarar hawa napep. Sai da suka isa bakin titi kana suka tari napep ya wuce dasu kasuwa, acan suka je suka siyi wayar, koda suka siya sun sami har ragin 5k saboda mai siyar da wayar saurayin Umaimah ne, kuma ɗan uwansu ne. Chanjin da suka samu yakai dubu talatin da biyar 35.000, suka wuce gurin da ake siyarda su chocolate da su shawarma, daga ƙarshe dai sun siyi simcard canjin hannunsu ya rage saura 5000, daga nan suka wuce gidan wata ƙawar Umaimah da tayi aure sati biyu da suka wuce, sosai ta ji daɗin kawo mata ziyarar da sukayi, har ta tashi zatayi musu girki sukace zasu tafi, Umaimah ta jona wayar a chaji kafin su tafi, Can anjima sukayi mata sallama suka wuce, ta basu cincin da dublan sukayi mata godiya, kai tsaye suka hau napep zuwa gidansu, lokacin da suka dawo ƙarfe 12:pm, dalilin da yasa basu wani damu ba, anty Tasneem ta ce musu sai 4:pm zata dawo wai ana yiwa ƙawarta kishiya shine taje gidan bikin, Koda suka shiga gidan basu wani kula breakfast ba, ana ta zumuɗin sabuwar waya, Talatu ta sakawa ƙofar key kana ta dawo ta zauna, Umaimah ta sake jona chaji, can anjima ta ciro ta saka mata numberta tunda anyiwa simcard ɗin register da NIN ɗin Umaimah, itama ta ɗauki nata number, kana ta buɗe mata WhatsApp ta nuna mata inda ake amfani dashi, sannan tasa mata number saurayin nata tayi masa serving, kana aka sake mayar da wayar chaji, Suna zaune suna hira, sukaji ana nocking ƙofar ɗakin Talatu tace "nasan ba zai wuce Yah Arman ba" aiko cikin sa'a tana buɗe wa ta hangoshi, parlor ya koma yana jiran isowarta, "Barka da zuwa yah Arman" tai maganar cikin dadaɗar muryarta, lumshe idanu yayi kafin yace "ina kikaje ɗazu na shigo bakya nan?" "Uhm dama Umaimah ce tace in rakata siyo kati zata kira dadynta" Arman ya wani haɗe rai gami da cewa "duk yawan ma'aikatan dake gidannan sai kun fita da kanku, idan haka ne meye amfaninsu?" Talatu tayi shiru, "ki kawomin abinci Please idan kuma babu ko indomie ne ki dafamin yunwa nakeji" yai maganar yana shafa cikinsa, Kai tsaye ta wuce dinning ta ɗauko masa abincinsu, saboda Allah-Allah takeyi ya wuce, bayan ta zuba masa plate ta ɗauko fork ta ajiye masa da Black tea ɗin da anty Tasneem tayi, har zata wuce yace "ban baki izinin tafiya ba" ta wani rausayer da kanta, dole ta zauna a kujera mai kallon tasa,"acan bedroom ɗin su, Umaimah tayiwa saurayin Talatu flashing har ya kira, ta rasa inda zatayi wayar tayi ringing har sau uku bata ɗaga ba, cikin ɗaya murya tace "Aysha kizo ki karɓi waya anty Tasneem ta kira, tace in baki" Talatu tasan duk low ne ta tashi da gudu tana cewa gani nan, ƙila abinci za'a ɗora mata, da haka ta zame ta barshi a gurin, Koda ya gama cin abinci ya mayar da hankalinsa ga kallon TV har aka kira sallahar azhar, ƙarfe1:pm ya miƙe ya fice. Talatu na shiga ɗakin Umaimah ta miƙa mata waya, kana tace "ya kira fa, amma ni nayi masa flashing" Talatu ta dafe goshi, Bayan ya sake kira yace, "Kyakykyawar Zuciya tana rayuwa ne a karkashin inuwar Aminci da Amincewa, Zuciyar da aka cudanyata da tsarkakakkiyar soyayya tana samar da ingantacciyar lafiya a gangar jikin mamallakin ta shaukinta yakan bi sassan jini dana ruwa domin cigaba da ginin gangar jiki mai'inganci so kalmar datafi komai dadin fade da saurare shike haifar da zaman lafiya a kowane karni. Keba zinariya ba, keba luuluu ba, ke ba a zurfa ba, amma dukkanin su kinfi su kyau " Koda ya gama rera mata nau'i'kan kalamnsa, tayi murmushi mai sauti kana tace "uhm zan kiraka da number ta, mun siyo wayar ammafa Umaimah ce ta matsa min" Yana dariya yace, "wacece kuma Umaimah?" Ƴar uwata ce" Talatu tai maganar tana murmishi, "Bata" Talatu ta mikawa Umaimah, Umaimah ta karɓi wayar, tare da cewa "Barka da wannan lokacin haƙiƙa kayi sa'ar tsinto zinare daga cikin wani gu wanda mai samunsa sai mai tsananin rabo" daga can ɓangaren yace "gaskiya ina godiya bisa gudunmawar da kika bayar dan ganin soyayyarmu tayi zurfi Nagode sosai" B"abu komai Allah ya inganta soyayyarku" Ya amsa da amin, ta mikawa Talatu, sun daɗe suna waya har yake ce mata bata tambayi sunansa ba, ta zaro ido cike da mamaki itakam ta mance, sai da ta bashi haƙuri kafin ya gaya mata sunansa Zayden, ta maimaita sunan cikin harafi mai daɗi, wanda shi kansa sai yaji kamar tafi kowa iya ambaton sunanta, "Aysha inason kiyimin alkawarin bayan ni bazaki sake kula wani namiji ba a faɗin duniya da niyyar soyayya?" tabbas bata san menene so ba sannan ita farin shiga ce a fanin soyayya, bata san meye ƙalubalen soyayya ba, lokacin Umaimah taje ɗauko musu breakfast tace "nayi maka alkawarin, amma nima sai kayimin, yace na me "kayimin alkawarin bazaka sake kula ko wacce mace ba bayanni sannan kayi haƙuri, bazaka dinga samu a any time ba, saboda idan har aka san na riƙe waya zan iya fuskantar ɓacin rai" ta ƙarashe maganar tana marairaice murya, "calm down my beauty karki damu na shirya gwagwarmaya akan soyayyarki insha Allah sai burinmu ya cika" zan jure duk wani ƙalubale da izinin Ubangiji, sukayi sallama tare da furta mata i love You, tace love You too" Dai dai lokacin da Umaimah ta shigo taji ana zancen love ta tuntsure da dariya, tana dukan Talatu tace "Aysha tashi Sooo" KEFFI, A yau ne dubban al'umma suka shaida ɗaurin auren Saudart da mijinta Alhaji Salisu Alherin Allah, lakadan ba ajalan ba, ɗaurin auren da ya samu halartar mantar shuwagabanni da governor's da ƴan siyasa harda shugaban kasa sai da yazo, kai har da turawa ƴan ƙasar waje duk sun samu halartar taron, Acan gidansu momy kuwa ba'ayi girki ba, odar ɗinsa akayi, tunda momy ta ji Dady ya kusa zama president ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda bata son a sami matsala a auren, ta kwantarwa da Saudart hankali, cike da tausasa kalamai har tana cewa idan ta musguna wa mijinta Dady itama zai saketa, idan sun zauna lafiya shine farincikinta, da haka dai Saudart take daurewa, badan tana jin zata iya samun rayuwar farincikin a gurin wannan dattijon ba, Tun gyaran jikin da akayi mata bayan fitowar ta daga gidan Ma'aruf shine, kuma har yanzu da haskenta, a jiya ƙawayen momy suka zo, har danginta sai jiya ta sanar musu, ada ta yanke shawarar babu wanda zata gayawa, kasancewar sunada hannu da shuni (dukiya) yasa ba ayi mata wani faɗa ba, da asubha wasu suka hallara, aiko an ɗurawa Saudart magungunan mata sosai, sannan a daren aka dinga turarata da turaruka masu zama jiki, Masha Allah tayi kyau, ranar bikin tasa kaya sunkai kala goma sha biyar, kuma ko wanne haura dubu ɗari uku, wasu suna cece kauce wasu kuma sunata farincikin, A ranar da yamma aka wuce da ita gidanta dake Badiko gidane na gani na faɗa amma yana tsakiyar gidan talakawa, gidan ya mamaye anguwar, sannan ita kaɗai ce a ciki, a cewarsa ta ɗan zauna na wani lokaci kafin subar ƙasar, ko meye dalili oho, Duk wanda ya zo kawo amarya sai ya tafi da maganar gidannan a baki, saboda kyawun gidan da yanayin tsarin gidan da ya mamaye anguwa guda, gidan sama ne mai hawa ɗaya, ƙofar shiga ma kana danna lamba zata buɗe ta gilashi ce mai ɗaukar ido, zallar parlorn ya ishi mai surutu ya je yayita zabgawa, bare a kai ga shiga asalin cikin gidan, get biyu ne a gidan, dana baya dana gaba, har da gurin shakatawa, gashi komai akwai a gidan furniture's duk Alhjin ya hana Dady ya siya komai, ya zamo nashi kawai idanu da fatan Alheri, Zuwa dare kowa ya watse daga ita sai ƙawayenta guda biyu, wanda suka zo da amincewar momy ragowar duk ta hanasu zuwa, "daga can parlor ake ta ƙwala musu kira, suka miƙe ɗayar tace "Saudart kekam kin samu aljannar duniya saura ta lahira, nasan babu abinda zaki nema ki rasa wallahi, dan Allah kiyiwa mijinki biyayya kina gani dai gamu daga masu mashin sai masu Aron mota suzo zance gurinmu, ɗayar tace "hm Saudart Wlhi tallahi kin gama hutawa irin wannan aljannar duniya haka, ni Wlhi ko gidan da bai kai wannan ba na samu nasan zan huta bare ke kalli TV a ko ina har toilet, taɓɓ gaskiya kin zo duniya da hannun dama, daga nan suka wuce bayan sunyi mata sallama, tabbas bata taɓa mafarkin shiga irin wannan gidan ba, dadynta yanada mahaukatan kuɗaɗe duk iya yawonsu basu taɓa zuwa irin wannan gidan ba, sosai take mamakin wai yau itace a wannan duniyar?, dan wannan gidan ya wuce a kirashi da gida sai dai duniya, tunanin inda zata koyawa zuciyarta son Alhjin takeyi, saboda ta faranta wa iyayenta rai, duk da yin hakan a gurinta abu ne mai matukar wahala amma zata daure ta danne zuciyarta ta kwatanta hakan, sallamarsa taji sai da gabanta ya bada rass, lokaci ɗaya hankalinta ya tashi...! Idan har naga comments zaku samu fiye da haka. Mom Islam ce taku ta gargajiya ga numberta ga duk wani mai son magana dani 08141799234 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ 45-46 Cikin sauri ta fara ƙoƙarin gyara zaman mayafin da aka lulluɓe mata fuska dashi, kafin ta ji sautin muryarsa ɗazu tayi wa zuciyarta alƙawarin zama dashi, lokaci ɗaya zuciyarta ta raunata, cikin sanyin murya ta amsa da "wa'alaikumussalam" Kallo ɗaya tayi masa ta cikin mayafin, kasancewar ba mai duhu bane, ta kawar da kai, tare da ƙoƙarin danne zuciyarta, "Masha Allah" ya ambata lokacin da yake kutsowa cikin ɗakin hannunsa riƙe da ledoji guda biyu manya, "sannu da zuwa" Saudart ce masa tana goge hawayen da ya fara zarya a kumatunta, tabbas shikam fuskarsa wasai take, kai kace wanda aka yiwa bushara da gidan aljanna, sai wani washe haƙora yakeyi, bayan ya ajiye ledojin a saman wani haɗaɗɗen table na glass mai ruwan golden color anyi masa ado da flowers masu kyau da ban sha'awa, ya tako a hankali zuwa inda take bayan ya amsa mata, "amarya bakya lefi, Barka da shigowa gidana, yarinya ki kwantar da hankalinki zan baki farinciki fiye da yadda kike tsammani, ina fatan zaki farantamin?" Yai maganar yana ƙoƙarin yaye mata mayafi, bata da zaɓin da ya wuce ta amsa masa, murya a hankali tace "insha Allah" sannu a hankali yake matsawa kusa da ita, har ya zo daf da ita, yana murmishi yace "tashi ki ɗauko plate a kitchen kinji, kokuma muje in rakaki tunda baki san ko ina na cikin gidan ba" ya ƙare maganar yana miƙewa tsaye, a hankali ta zuro ƙafafuwan ta da suka sha zanen lalle baƙi, kana ta gyara zaman mayafinta a kafaɗa, ya lura da kuka tayi, sbda idanunta sun ɗan kumbura, a maimakon yayi gaba ita ta dinga bin sa, kawai sai ya wani tsaya a baya yana yi mata kwatancen inda kitchen ɗin yake, dalilinsa ko na tsayawa a baya, ya kasa haƙura da maitar son ya kalleta, sai bin ta yakeyi da wani irin fitinannen kallo yana lashe baki, koda suka iso kitchen ta buɗe ta shiga, kanta kusan juyewa yayi, lokaci ɗaya ta fara tunanin shima kitchen ɗin yana cikin wata duniyar kenan, "wai wannan mutumin wane irin dukiya yake dashi, irin wannan kitchen ɗin ai ya ninka parlon gidan Ma'aruf a kyau, ya lura da tunanin da takeyi, "ɗauko mana Habibty" yai maganar cikin Muryar lallashi, "wow wannan sunan yayi mata daɗi, inama ace wanda takeso ne matashi ya aureta ba wannan tsohon ba, da ta ji daɗi wlhi, Wani haɗadden plate ta ɗauko, wanda samun irinsu a Nigeria yana iya yin wuya, tunda kaf kayan ko cokali ma daga ƙasar waje aka kawo su, koda ta ɗauko plate ɗin zata juyo ya rungumeta, tare da cewa "muje kici abinci" Tofa🤣 Lokaci ɗaya ta mance da wa take tare, domin idan baku mance ba, bazawara ce... Da sauri ta dawo haiyyacinta ta turo baki tare da cewa za "meye haka?" Alhaji yace "kam yayi da uwar ƙaton ciki yace "shauƙin ƙaunarki" A hankali ta zame tare da wucewa ta gefensa tunda taga hanya, a saman table ɗin ta ajiye plate ɗin, kana ta koma saman gado ta zauna, Mamaki ta bashi, sai ya nemi guri saman couch ya zauna mai zaman mutum biyu, kafin ya ɗauko ɗaya daga cikin ledojin ya buɗe guda ɗaya, soyayyen naman ɗawisu ne, a cikin wani bowl mai masifar kyau ɗan ƙarami, sai wasu kayan ciye-ciyen wanda nima ban sansu ba, "Habibty taso kici" "Naƙoshi " Saudart ta faɗa tana gyara kwanciyart, ita dama ba ci zatayi ba, kawai ta bishi ta ɗauko ne gudun kar ya ga kamar ta fara yi masa wulaƙanci tun yanzu, Yoghurt ya ɗauko tare da glass cup wanda ya ɗauko acan kitchen, ya tsiyaya a cup ɗin, wanda ya ke haɗe da kwakwa da dabino da madara kai nama rasa sunan ragowar🤔, sai da ya cire babbar rigarsa kafin ya ɗauki yoghurt ɗin kana ya isa gareta, cikin sigar lallashi yace "haba Habibty ya kamata ko wani abun kisa a bakinki" itakam ta riga da tayi barci bata ma san yanayi ba, badan yaso faruwar hakan ba, ya dawo ya ajiye cup ɗin tare da zama gefen bed ya fara ƙoƙarin cire agogon hannunsa, kana ya cire rigar ciki, innalillahi lilahi wa inna ilahir raji'un, ba mutuwa akayi ba, shirgegen ƙaton cikin Alhaji na hango. Har yakai hannu zai buɗe toilet, yaji ana nocking da ƙarfi kamar za'a ɓalle door ɗin, ɗaga kansa yayi sama, kana ya kalli makeken agogon dake manne jikin bango lokacin ƙarfe 11:pm na dare, kawar da tunanin zuwa buɗe kofar yayi ta hanyar murɗa handle na ƙofar ya shiga toilet ɗin, wow ya Subhanallah, banɗaki har TV ni mom Islam, uhm wasu na'urori ne suke sarrafa kowane kayan amfani na banɗakin, ruwan zafi ruwan sanyi da sauran abubuwa, kai harda jaridu wato drowarsu a banɗakin, nidai a tunanina idan kashi zakayi sai ka ɗauka ko?🤣hhh, Sai da ya cire kayan jikinsa, kana ya tara ruwan wanka ya shiga ciki, lumshe idanu yayi tare da hango inama ace shi da Saudart ne a cikin wannan ruwan suke yin wanka, sai kuma ya sake jin nocking ɗin kamar ba na mai hankali ba, a gurguje ya yi wanka ya ɗauki ɗaya daga cikin towel ɗin da aka rataye su, ya goge jikinsa kafin ya fito, tare da ɗaura wani towel ɗin a ƙuginsa, fitowa yayi zuwa ɗakinsa har yanzu ana nocking, ya ɗauki jallabiya ya zura, har ya iso parlo wata zuciyar ta bashi Shawara akan ya kira mai gadi ya ji ko su waye, Hakan ko yayi, koda ya kira mai gadi yace "masa wasu mata ne guda biyu Wlhi bai gane fuskarsu ba, thinking ya fara yi shin waɗanne mata ne zasu zo masa gida a dai-dai wannan lokacin?" Bashi da amsar tambayarsa hakan yasa shi, jingina da jikin bango tabbas ya fara tunanin anya ba Hajiya Zaliha bace?" Itama wannan tambayar da yayiwa kansa bashi da amsarta, ya yanke shawarar ya koma ciki, sam bazai bari kowa ya shigo masa gida ba, kai tsaye ya koma bedroom ɗin Saudart ya bi lafiyar gado, tare da matsawa kusa da ita, kana yayi hugging ɗinta yana sa wayarsa airplane mode. Acan bakin ƙofa kuwa, Hajiya Zaliha ce ita da babbar ƙawarta, cike da masifa suke tsaye a gurin zuciyarta sai turiri takeyi, rai a ɓace tace "wato wannan ɗan rainin hankalin ni zai nunawa yayi aure ko?" Ƙawar Tata tace "Zaliha kawai kizo mu koma gida in ya so gobe da sassafe sai mu yi sammako mu zo" "Hadiza Wlhi tallahi bakisan irin tuƙuƙin da zuciyata takeyi yi ba, abin kunya abin takaici kamar Alhaji ya auri ƴar cikinsa, haba, sannan tunda nake dashi bai taɓa raɓar wata mace ba bayan ni, inafa zan iya barci ai kwanan zaune zanyi, ina nan anan billahillazi" Hajiya Zaliha takai ƙarshen maganar cike da ɓaci rai da takaicin abinda Alhjin yayi, dole Hadiza ta biye mata, nan fa suka fara tunanin inda ya kamata su kwana, Hadiza tace "ai baza'a rasa ɗakin baƙi ba, barin tambayi mai gadi, Hajiya Zaliha ta dakatar da ita, tare da cewa "ni zanje dawo" fuu ta tafi gurin mai gadi tana zuwa ta riƙe ƙugu kana tace "akwai wani emtin ɗakin kwanan baƙi ne anan?" tunda ya ga yanayinsu yasha jinin jikinsa da cewar akwai wata a ƙasa, tabbas waɗannan matan akwai abinda ya kawosu, cikin daka tsawa ta sake cewa "magana nakeyi baka ce min komai ba?" "Bab...bab...bu.." yai bata amsa muryarsa na rawa, Hajiya Zaliha ta yaye mayafin dake yafe a kafaɗarta tare da yafashi a gefe ta turo ɗaurin ɗankwali gaba, kafin tace "kai sa idonka a nawa, na rantse da Allah idan baka bamu gurin kwana ba sai nayi maka tijarar da har ka koma ga Allah baka mance ba, kasan ko Ni wacece?" Ya girgiza kai alamar "a'a" Ta kwashe da dariya, kana tace "ni matar mai gidan ce, dama nayi tafiya ne yau na dawo, nayi kiran duniya yaƙi buɗemin kuma kayana suna ciki, tunda na jima da tarewa a gidan, da yaji tsoro yanzu kam ya washe haƙora kana yace "ahh Hajiya ai kin firgitani, ai bai kamata a baki ɗakin baƙi ba, barin buɗe miki ɗakin manyan baƙi, amma ko kin kira Alhjin a waya?" Hajiya Zaliha tace "eh amma inaga yayi barci ne" Tai maganar cikin siyasa, saboda taga yin masifar ba zai kai ta ga nasara ba. Kai tsaye ya wuce dasu ɗakin da Alhjin yake sauƙar manyan baƙinsa, haɗaɗɗen ɗaki ne, wanda ya amsa sunansa ɗaki, ga shi an yalwatashi da kayan alatu na zamani da ƙyale ƙyalen turawa, kasancewar sun gaji gado suka haye, Hajiya Zaliha ta buɗe hand bag ɗinta ta sa car key ɗinta kana ta kwanta, koda barcin ya ɗauke su ita a wani hali ta kasance, saboda mugayen mafarkai da ta dingayi akan Alhajin da matar da ya aura, bata ƙaunar ta ji wannan lamari ya faru ko kaɗan, sam bata so, bata son Alhaji yayi taraiyya da Saudart, saboda Alhaji nata ne ita kaɗai, ƙarfe 2:am na dare ta farka cike da tarin baƙinciki da takaici mai cike da tsantsar nadamar saken da tayi har wannan lamari ya faru, miƙewa tsaye tayi tana mutsike idanunta masifar kishi na cinta, tace "wayo Allah, ta dafe dai dai saitin da zuciyarta ke bugawa, Itako Hadiza barci takeyi harda munshari, Hajiya Zaliha ta fara zagaye ɗakin tana neman mafita, Bazata iya bari gari ya waye ba, bata ɗauki mataki ba, tayi tunani iri iri, daga ƙarshe dai ta buɗe ƙofa ta fito harabar gidan tana sake ƙare masa kallo, gingina kai takeyi tana taɓe baki gami da yin tsaki mtswww, takai kusan 30mints barci ya ƙauracewa idonta tsabar zafin kishi. Har yanzu dai ta kasa haƙura gari ya waye ta sake zuwa gurin ƙofar ta bubbuga kamar zata ɓalle door ɗin, a firgice Saudart ta buɗe ido, ta fara ƙoƙarin tashi zaune, kallon hannun Alhjin da ya rungumeta sosai tayi, a hankali ta zame daga jikinta tare da saukowa daga saman bed ɗin ta tsaya cak a tsakiyar ɗaki, zuciyarta ta rabu gida biyu, shin taje ta buɗe ƙofar taga waye yake nocking kokuma ta tashi alhaji?, "Ina!!" Ta faɗa a fili a hankali ta juya key ɗin ƙofar dan batayi tunanin komai ba, kofar ta buɗe.... SINGAPORE Buland island Tun tafiyar Anam da sukayi da Dady, aka juyar mata da hankali, ta koma sai inda akayi da ita, duk da sanin Dady, wannan abin ya faru. A estate ɗin su, A ranar da aka kawo Anam aka sauya mata suna zuwa Neria, ita kuma Hussaina sunanta Misha, ikon Allah kenan, lokaci ɗaya jininsu ya haɗu, sosai Misha ta ja Anam a jiki kasancewar ta shiga ranta, gata yarinya ƙarama a shekaru bata wuce 16yrs ba, duk da ƙarancin shekarunta sai da suka san inda suka sa ta fara tarbiyya da maza Christian ƴan uwanta, tunda yanzu ta fita a musulunci, tun tana jin kunya tana ɓoyewa har ya zamo ta zamo ƴar gari, amma sai dai duk wanda zasuyi taraiya dashi sai anyi taste an tabbatar da lafiyarsa kana kuma ya sauke maƙudan kuɗaɗe, yau ma kamar koda yaushe, suna zaune a ɗakinsu, kasancewar Misha tace Anan ɗin ta kwaso kayanta, ta dawo ɗakinta, bayan sun gama tsara kwalliya aka fara koyar da ita sanya kaya matsatstsu kuma iya cinya, da yawo babu ɗankwali, dole takeyi dan bata iya yin musu sai dai wani abun a ƙasa ranta tana jin zafinsa amma bazata iya furtawa ba, A yau ne oga ya shirya babban taro wanda ya kasance jimami ga dukkan ƴan matan dake cikin estate ɗina, abinda ke faruwa shine, haka kawai aka ga uwar ɗakin nasu ta faɗi ta mutu babu wanda yasan abinda ya faru da ita, a ranar ansha giya kamar ba gobe, wasu alamomin sukanyi nuni da kamar ogan yanada masaniya akan mutuwarta. Bayan sati ɗaya da mutuwarta ya shirya babban taro a hall ɗinsa dake nan Buland island, babban Hall ne, wanda ya amsa sunansa, ko wacce budurwa an jere mata drinks da snacks da giya da sauran kayan shaye-shaye, bayan ya buɗe taro da yaba musu da yayi kana ya fara gabatar da dalilinsa na haɗa wannan taro, "Mun samu canji sosai, bazance mutuwar uwar ɗakinku alheri bace a gareni, haƙiƙa naji mutuwarta, kuyi hakuri zaku sameni mai baku duk abinda kukeso a faɗin duniya, Abu na farko da nakeson sanar daku shine, akwai wani cigaba da na hango mana, wanda kuma zaku sake samun canji duk da nasan a cikinku babu wacce zata ce ta buƙaci wani abu bata samu ba, na farko dai shine.. "Inason ko wacce budurwa a cikinku idan ƙarshen wata yayi kokuma in ce lokacin da ta fara period ta kawomin pad ɗinta na adadin kwanakin da takeyi, akwai wani magani da za'ayi na rigakafi" ya kai ƙarshen maganar yana tuntsurewa da dariya, ragowar abokan aikin nasa ma dariyar sukeyi, yayinda suma ƴan matan suke dariya gami da yin tafi, Sosai taron yayi masa daɗi, hakan ya sake tabbatar masa da cewer, aikin bokansa yana tafiya inda ya kamata, Bayan nan yace "yau a club ɗinsa akwai shagali na musamman" Suka sake yin tafi raf...raff.., Daga nan ya rufe taro da yi musu faɗa akan duk wani abu da suka rasa su gaya masa, Duka suka cewa "toh" Daga nan taro ya watse kowa ya nufi sashensa, Bayan Oga ya dawo gida, ya tuntsure da dariya, babban dalilin da yasa ya kashe uwar ɗakin nasu shine, sam bata goya masa baya a wasu abubuwan nasa, to meye amfanin zamanta a duniya tunda har bazata bari su haɗa kai su yi kuɗi na ban mamaki ba. Washe gari. Akwai wani babban kamfani da yake dashi wanda suke safarar haramtattun magunguna wanda suke ƙirƙira sannan suyi rubutu da sunan wata ƙungiya, sau biyu ana yi masa worning amma yaƙi fahimta, cikin basaja mutanensa suke kai magunguna tare da nuna shaidar amincewar gwamnati, hakan yasa masu asibitin basu da tabbacin banbance marar kyau da mai kyau, Safiyar yau Monday an tsananta bincike game da masu aikata laifin, Oga Reed na zaune saman tsafaffiyar kujerarsa, ɗaya daga cikin securities ɗinsa yayi masa magana, da cewar yayi baƙo da alama akwai alƙairi game da zuwan bakon, Cikin amincewar Reed aka shigo da baƙon, fari ne tass Balarabe ɗan ƙasar Saudiyya, abinda ya bawa Reed mamaki bai wuce, ya akayi wannan Balaraben ya san da zamansa har ya kawo masa ziyara?" ba yanzu zai buƙaci wannan amsar ba, Tabbas idan har mutumin bai zo da wata ƙullalliya ba, zai yi musu amfani, idan kuma ya kasance mai kishin musulunci ne yazo leƙen asiri ne, Reed yayiwa baƙon nasa umarni yace "inayi maka maraba, da Yaren su, kasancewar Balaraben yana ji, ya amsa da yauwa tare da miƙawa Reed hannu cikin muryarsa mai daɗin amo yace "sunana Thabit ina fatan zamu zamo abokai" Reed ma ya miƙa masa hannu kana ya kasa ɓoye mamakinsa yace "amma mai ya baka sha'awar siyarda ranka har kazo inda nake kai tsaye ba tare da kayiwa zuciyarka shawarar ka ci gaba da rayuwa a duniya ba?" Thabit yai ɗan gajeren murmishi, kafin yace "wato Reed idan har mutum yana neman hanyar da zai zamo wani abin kwatance a duniya ba sai ya tsaya jin tsoro ko makamancin haka ba, kawai kai tsaye zai miƙo buƙatunsa idan anyi na'am dasu to, idan kuma rai yayi halinsa duk ɗaya" Sosai maganar Thabit ta shigi zuciyar Reed lokaci ɗaya yaji ya fara amincewa dashi, sai dai ya yi umarni da a kawo masa wata kujera Thabit ya zauna a kai, kujerar itama tsafaffiya ce sosai, wadda take auna abinda ke zuciyar mutum na alkairi ko na sharri, koda aka Thabit ya zauna a wannan kujera sam bata bada wata matsala ba, hasali ma tayi nuni da gyara tare da ci gaba zai kawowa Foundation ɗinsu" dama Reed ya daɗe yana jiran wannan rana, ranar da zai samu mutumin da zuciyarsu zatazo iri ɗaya, tabbas ranar yau ta zamo ranar shagali a gareshi, ranar yau ta zame masa haske, ya mikawa Thabit hannu suka tafa tare da rungume juna, Tun a daren suka fara gabatar da aiki gadan gadan babu wasa... ƘAUYE A ranar da gudidi ta koma ta dinga ihu tana birgima a ƙasa, sam bata ƙaunar sake rayuwa a cikin ƙauyen, koda mahaifiyarta Ramma tayi mata tsawa, itama tsawar ta daga mata tare da cewa "yasin wannan baƙinciki ne, ina cikin ni'imar Ubangiji kin wani dawo dani nan, a aljanna ta ɗaya muke, ramma tace "kiyi hakuri Gudidi gonar rogo na siya nasa aka haƙomin kaɗan daga ciki nakeson in fara siyarwa ko Allah zai taimake mu, Gudidi ta kwaɓe fuska kafin tace "yasin hedai ki nemi wanda zeyi miki talla naje binni nahya ruwan garɗi kuma yanzu kice wani talla yasin bazanyi ba, bari ma kiga in samu kuɗi Wlhi binni zan koma zaman ƙauye ai sai wanda yayi niyya, tunda ba anan aka binne cibiyar mutum ba, tai maganar tana taɓe baki. Ramma ta zaro idanu tana dafe ƙirji kafin tace "Wlhi idan hakane zaman binni bai tsinana miki komai ba, kwata-kwata kwanan ki ɗaya kika dawo, amma duk kinbi kin fetsare, to Wlhi tallar rogo babu fahi sai kinyi kinji na gaya miji" Ramma tai maganar tana nunata da yatsanta, kuka sosai takeyi tana ta shure-shure, Washe gari, samarin ƙauyen suka dinga shigo da rogo a buhu, bayan sun gama kawowa, Ramma ta haɗa wutar kara ta dafa rogo ta saka a farar ledar buhun suga, ta zuba ƙuliƙuli dakakke wanda aka zabga masa farin maggi da gishiri, "Gudidi kizo ki higa wanka ni na kammala nawa aikin ke nake jira, abin mamaki ko musu batayi ba, ta tashi ta shiga wanka, tana fitowa ta tsantsara kwalliyar hauka, janbaki har a saman gira, harda wani wai hawayen masoyi, ta zabga farin janbaki abin dai sai wanda ya gani. Wasu daga cikin kayan da Hajiya mama ta bata, ta ɗauki atamfa ɗinkin buba ta saka, Wow Masha Allah tayi kyau sosai, Masha Allah, Bayan ta gama sanya kayan ta ɗauko wani baƙin mayafi duk ya tattare ta ɗaureshi a ƙugu, kana ta ɗauki tiren tana cewa "na tafi" Ramma dake ɗakin girki ta fito da gudu tana cewa "Gudidi bakici komai ba" Gudidi tace "na nawa zanci?" Ramma tace "na Ahirin" babu musu Gudidi ta wuce, mamanta nayi mata Allah ya tsare...! Idan kinason shiga group wanda nake posting kimin magana ta WhatsApp 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 Mom Islam Page 47-48 Tun a hanya ta fara ciniki, kafin takai ga gurin da take zama har rogon ya ƙare, sai dai anyi ba ayi ba, wai matar bakanike ta haifi sifana, Da sallama ta shiga gidan murya a sanyaye tace "Ramma na dawo, jin Muryar Gudidi yasa Ramma fitowa da sauri daga ɗakinta, fuskarta ɗauke da murmushi tace "hannu da dawowa Gudidi mai kasuwa da sunan Allah, ajiye tiran ki higa ɗaki ki ɗauko fura da nono ɗazu yaro ya kawo talla na siya miki.." Duk da tsananin fargabar da take ciki bai hanata zuwa ɗakin Ramma ba, taje ta iske fura da nono mai sanyi, sai da ta cika cikinta kana ta fito tana goge baki, Bayan ta dawo gurin Ramma ta kunce ɗamarar da tayi, kana ta durƙusa har ƙasa, idanunta cike da hawaye tace "dan Allah dan Annabi Ramma ki dubi sallahar iyayenki ki yafemin" Ramma ta tsorata sosai dan ita bata san dalilin neman yafiyar ba, "tashi ki zauna kiyimin bayani inda zan fahimta" Ramma tayi maganar tana kallon Gudidi, da har yanzu kuka takeyi, Sosai sautin kukan gudidin ya cika mata kunne, ta daka mata tsawa saboda haushin da ta bata, kafin tace "wallashi ko kiyi magana ko in zaneki da tsumagiya, jin haka yasa Gudidi share hawaye tare da zuƙo majina ta shanye🤣 kafin tace "Ramma Wlhi na yi ciniki sosai, na kamo hanyar dawowa gida, na nemi kuɗin na rasa" Da sauri Ramma ta tashi tsaye tana dafe ƙirji kana tace "Na higa uku Gudidi kin cuceni, Wlhi da ki yimin wannan ɓarnar ai gara ki gaura min mari" Ramma ta wani rarumo ƙatuwar sanda tare da cewa "gara in karyaki Hegiya kawai, kuma wallashi kije duk inda kuɗi yake ki nemo min kuɗina dan wallhi bazan ɗauki asara ba, saboda suma masu rogon ba yafemin zasuyi ba" ta ƙare maganar tana bin gudidi da gudu ko mayafi babu a jikinta, cikin ɗaga murya Gudidi take cewa "dan Allah Ramma kiyi hakuri Wlhi tallahi ban gansu ba, ni ban ci miki kuɗi ba" Har yanzu dai surfa mata masifa takeyi, na,,, taje duk inda kuɗi yake ta kawo mata idan ko bata samu ba, sai ta kusa sumar da ita, Tana tafe tana share hawaye, ta hango ƙulin baƙar leda irin wanda ta ƙulle kuɗin rogon a ciki, tana ci gaba da kukan ta sunkuya ta ɗauki ledar kana ta kunce, "alhmdulilah ta ambata tana kuka tana dariya" ta waiga taga babu kowa, ta ruga da gudu, tayi nisa sosai da gidansu, sai da ta isa gindin bishiyar mangoro kana ta nemi guri ta zauna, ta ciro kuɗin a leda kana fara ƙirgawa, dubu biyar ne cif, ta washe haƙora, kome ta tuna oho sai kuma ta turɓune fuska kamar zatayi kuka, kalmomi biyu da mahaifiyarta tayi mata ne yasa ta sauya yanayi, na farko, Taje duk inda zataje ta nemo mata kuɗinta, na biyu, kar ta sake ta dawo mata gida babu kuɗi" "Ko bin maza zanyi kenan?" Tai maganar tana tura kuɗaɗen cikin ɗankwalinta. Da sauri ta miƙe tsaye kana ta fara tunanin meye mafita a gareta, Tafiya tayi mai nisa wanda ita kanta bata san inda zataje ba, tabbas akwai wani abu da yake birgeta da rayuwar ƴar binni, tana bala'in son ilimi a rayuwarta bugu da ƙari tana son itama ta zamo kamar ƴan gayun da ta gani lokacin da suka je binni, tuno, rayuwar da Talatu zata ci gaba da yi tayi, hakan ya ƙara mata ƙwarin gwaiwar son taga ta fita a ƙauyensu, tana tafiya tana tafiya sai gata a tashar mota, gabaki ɗaya ta riƙiɗe sosai, bata ma san inda zata nufa ba, duk a tunaninta idan ta shiga mota, kai tsaye gidansu Anty Jamila za'a kaita, hakan yasa ta kwantar da hankalinta tare da zama daram a mota, har ta fara hango idan har ta je suka haɗu da Talatu zasu zuba yanga, tana tsaka da tunani karen mota yace "ta kawo kuɗi, ta tambayeshi nawa ne yace mata dubu "uku" ta ƙirgo ta miƙa masa ya rage saura dubu biyu kenan, ta ƙullesu da kyau, kana ta zubawa masu zirga-zirgar wucewa idanu, Ta ɗan ɗauki lokaci a tasha motar bata tashi ba, dan har adu'ar kar Allah ya haɗata da wanda ya santa ta dingayi har motar ta tashi, ... ANGUWAR ME GISHIRI Dake cikin Ƙauyen Saminaka. Wani gida na hango wanda aka gina shi da jar ƙasa, ko da yake yawancin gine ginen haka suke, gidan zagaye yake da katangar buhu, kasancewar katangar gidan ta fadi, malam Habu na Lami tsoho ne amma ba irin tukuf ɗin nan ba,, yanada matarsa ɗaya, Baaba Lalai, Baaba Lalai itama ta tsufa, saboda ko girki bata iya yi, sai dai surukarta wato matar ɗanta idan tayi take zubo mata, yawancin cimar tasu ma daga kunu sai fate, sai tuwo, duk da arziƙin dabbobi da Allah yayiwa malam Habu bai sa ya azurta iyalansa ba, a lissafin mutanen ƙauyen idan aka tashin lissafa masu tarin dukiya har dashi a ciki, saboda ko wacce shekara idan ka ka tayi lokacin da ake kwashe amfanin gona, Allah ya albarkaci nomansa, hakan yasa koda yaushe a cikin siyo dabbobi yake, wato ya siya ya siyar, Yauma kamar kowane sati, kasancewar duk ranar Laraba ake cin kasuwar Saminaka, acan yake siyo dabbobin, kama daga Akuyoyi da raguna harda kaji na gida, sannan kuma ya siyar a kasuwar idan har aka ɗora masa riba, Tun bayan da ya dawo daga sallahar asbha yake ta gyaran igiyoyi wanda zai ɗaure dabbobin nasa, bayan ya gama gyaran igiyar ya ƙwalawa magidancin ɗansa kira, kasancewar a gida ɗaya suke, "wanda ya kira da halliru ya fito yana cewa "hannu baba ka gama gyaran igiyar?" "Eh halliru na gama, ungo ɗauresu sai mu tafi" Cikin umarnin mahaifinsa ya ɗaure dabbobin kusan su ashirin, suka wuce kasuwa a ƙafa, koda suka isa babu wasu mutane sai dai shi malam Habu ƙa'idarsa ne zuwa da wuri, dan sai dai aje a sameshi badai ya sami wasu ba, bayan ya gama gyaran rumfarsa, ya ɗaure ko wacce dabba a tirke kana ya nemi gurin zama ya zauna. 8:am, lokacin ne mutane suka fara halartar kasuwar, kasancewar anata hidimar babbar sallah dabbobi sunyi tsada sosai, dabbobin malam Habu Masha Allah sunada kyau ga ƙiba shiyasa duk wanda yazo siya ya gaya masa gaskiya kuɗin inhar da gaske yake yi, bazai yi masa musu ba, alhmdulilah kafin ƙarfe sha ɗaya 11:am har dabbobi sun ƙare, saura guda biyu, wani abokinsa dake yawan zama a gurinsa ya ƙare musu kallo kana yace "malam Habu waɗancan dabbobin akwai shiga rai, Wlhi daga ganinsu naji sun higa raina, badan bani da kudi ba ai da siya, sai dai tausayin da nakeyi musu ba zai bari in yarda a yanka su ba" malam Habu ya jinjina kai, kafin yace "Muzammilu kana bani mamaki, wani lokacin idan kayi magana sai kace ƙaramin yaro, to ai naga dai Ubangiji ne ya halasta mana cinsu amma kana wasu maganganu" Sallamar wani mutum wanda yai parking motarsa acan nesa dasu ne ya katse musu maganar da sukeyi, kallo ɗaya zaka yiwa mutumin ka gane nera da hutu sun samu mazauni, musamman ma idan ka kalli matarsa dake gefensa jajir da ita sai kace baturiya, tanada pink lips mai kyau, cikin shagwaɓe murya tace "Hayati Please kar mu wuce dabbobinnan gaskiya sunyi min" wanda ta kira da Hayati ya ƙare wa dabbobin kallo kana yace "My life ke har kinsan wasu dabbobi ne, ta ɗan ɗora kanta a saman kafaɗarsa tana dariya marar sauti, tunda har my life tayi magana sai shima ya sake ji sun shigar masa rai, Bayan su Malam Habu sun amsa sallamar suka ƙarasa, matar ta fara shafa macen ragon, macen ragon ta lumshe idanu alamun tana jin daɗin hakan, ko da Matar ta matsa gefe, macen ragon sai ta fara kuka sosai, matar ta sake dawowa kana ta ci gaba da shafa ta, bayan sunyi ciniki mutumin ya siyi dabbobin aka sanyasu a mota suka kamo hanyar dawowa gida, Yaseen da Yusra, masoyan juna kenan, nickname ɗinsu (Yasra) ko ni soyayyar su tana birgeni bare ku masu karatu da zaku so jin cikakken tarihin masoyan, Yaseen da Yusra a makarantar Jami'a suka haɗu, tun suna yiwa junansu ikirarin abokai, kwatsam sai abota ta juye soyayya mai ƙarfi wacce duk wanda yaga inda suke gudanar da tsaftsracciyar soyayyarsu sai sun birgeshi, kafin yiwuwar auransu sai da aka dinga kai ruwa rana, kafin iyayensu suka amince, Yaseen babban ɗan kasuwa ne, saboda yayi gadon mahaifinsa, mahaifin Yusra kuwa mataimakin gwamna ne, ko wanne iyayensa na damawa da nera sosai da sosai, Anyi shagali sosai a bikinsu dan sai da aka shafe sati biyu ana shagali, a ranar bikin kuwa ɓangarorin iyayen biyu sun nuna bajintarsu, duk inda ka shiga a kafafen sada zumunta posting ɗin hidimar bikinsu kawai zaka gani. Bayan anyi aure, burin masoyan biyu ya cika, nan fa rayuwarsu ta sauya cike da farin ciki da ƙaunar juna, a halin yanzu watansu tara da aure, suna zaune a Kaduna iyayensu ma duk acan suke. Sunyi tafiya mai nisa kafin suka iso Kd, kai tsaye gidansa ya wuce, bayan an buɗe masa get ya kutsa hancin motar ciki, motocin da akayi parking ɗin su sunkai biyar, kuma duk mallakarsa ne, sababbi fil sai sheƙi sukeyi, yana yin parking motarsa ya fito, Yusra ma ta buɗe ta fito, damuwarta bai wuce Yaseen ya buɗe dabbobin nan taga lafiyarsu ba, kamar yasan tunaninsu takeyi, yana ɗaga murfin Boot ɗin dabbobin suka fara kuka, Yaseen ya fito dasu tare da cewa "gidan gona za'a kaisu tunda dai kwanakin sallahar da saura" Yusra ta matso kusa dashi kana ta yi hugging ɗinsa cikin sanyaya murya tace "Please Hayati ka barni a tare dasu" mamaki ma ta bashi, ita da take ƙyamar dabbobi yau take maganar ya barsu?, Hannunta ya kama yana cewa "kinga my life muje ciki, Ɗan Lami ka shigar da awakan garden kafin zuwa gobe a haɗasu da ragowar dabbobin" Cikin bin umarninsa ma'aikacin gidan ya amsa, sukuma suka wuce ciki, Suna shiga ta fashe da kuka mai cike da shogoɓa tana wani mannewa a jikinsa, a duniya idan akwai abinda ya tsana bai wuce kukan Yusra ba, sai kuma iyayensa, da sauri ya ɗagata sama kasancewar ita ɗin irina ce siririya, kai tsaye ya haura da ita upstairs yana yi mata waƙa, murmushi takeyi wanda ya sake ƙawata pink lips ɗinta, tana ta ƙoƙarin zillewa shigo ya riƙe ta gama. Har ɗakinta ya kaita tare da direta a saman bed, lokacin ƙarfe 4:pm basuyi sallah ba, a hankali ya matso da fuskarsa kusa da nata, suna jiyo numfashin juna kafin ya kai hannunsa ƙasan mararta in Cold voice yace "mai yasa kike yawan ɓata ranki, shin baki san yin hakan illa bane ga babynmu?" bakinta ta matso dashi kusa da nasa, tare da yi masa hot kiss har sau uku, tana dariya, cikin shogoɓa tace "uhm ba kaine ba ai kaine" "Am sorry my life sai inda kikace duk abinda kikeso shi za'ayi, yanzu dai tashi muje muyi alwalah, yai maganar yana miƙa mata hannu, alamar ta taso...! Afuwan masoya masu karanta littafin NA KASA JUREWA, jiya baku ga update ba, ina mai yi muku albishir da gobe Asabar zanyi muku posting ranar Lahadi kam bazan samu yi ba sai Monday, ga wannan babu yawa kuyi manage. Wanda suke son shiga group ɗin da nake posting suyimin magana WhatsApp only 08141799224. Mom Islam *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ Page 49-50 Wunin ranar dai Yaseen bai je ko ina ba a gidan ya ƙare shi. Ko da ya dawo daga masallaci ya samu Yusra tana tsaye a parlor, ta yane jikinta da mayafi marar nauyi, ba taji shigowarsa ba, bare ta san da cewar yayi sallama, tunda ya lura da hakan ya, taho a hankali kana ya zagayo ta bayanta, ba tare da ta sani ba, ya sanya tafin hannuwansa biyu kafin ya rufe mata idanu yana murmushi, tabbas badan tayi nisa a tunani ba, da tuni ta san da shigowarsa, saboda ko bataji motsinsa ba, iya ƙamshin turarensa ya isheta sanin shi ɗinne, WASHE GARI Bayan Yaseen ya tashi Yusra shikuma ya wuce masallaci, koda ya dawo ya sameta tana saman sallahya tana ta rusa gyangyadi, tafin hannunsa ya kai saman fuskarta, ya shafa a hankali, ta buɗe idanu, lokacin gari yayi haske, cikin sassanyar murya tace "Hayati Barka da safiya, "my life dafatan kin tashi cikin ƙoshin lafiya ya babyna" Tai murmishi idanunta a lumshe da alamu gyangyadin yayi mata daɗi, ɗagata yayi kana ya ɗora ta saman bed ya kwantar da ita, shi kuma ya wuce parlo bayan ya ɗauki system ɗinsa, Ƙarfe 9:am ta tashi a barci lokacin har Yaseen ya tafasa shayi already sunada bread ya soya ƙwai, sai da tayi wanka kana taci kwalliya sannan ta fito. A hankali takai lallausan tafin hannunta kana ta ɗora su a nasa, sannan tace "Hayati" cikin sanyin murya tayi maganar, My "life" ya faɗa yana kamo hannunta, a hankali suke tafiya har suka zo inda kyawawan kujerun da suka ƙawata parlorn suke, ya zaunar da ita, kana shima ya zauna a kusa da ita, "my life" ya kira sunanta, bata amsa ba, sai ma zuba masa idanunta da tayi tana kallonsa, "mai yasa ba zaki rage tunani ba, kinsan yin hakan yana barazana ne da lafiyarki?" hankalinta ya kasa kwanciya, burinta bai wuce ta je ta gano waɗannan dabobi ba, taga a wane hali suke. "Hayati dan Allah ka kaini gurin dabbobin nan" Alƙawari yasa ta ɗaukar masa, na sai taci abinci, Bai kaita gurin dabbobin ba, har sai da taci abincin. Ya sani sarai idan ta so abu tana iya fashe masa da kuka, har yanzu mamaki take bashi, any time zancen dabbobi, daga ƙarshe dai yace "tashi muje" ta miƙe tana ɗan yatsina fuska, tare da sanya hannu a mararta, cikin bai wani girma ba, sai dai sauyin yanayi da takeji, hijab ɗinta ta ɗauko zumbulele kana suka wuce garden kai tsaye, Bayan ya gaishe su kana ya buɗe musu sannan suka ƙarasa ciki, Lumshe idanunta tayi, lokaci guda taji wani sanyi mai ni'ima yana shigarta "Masha Allah" ta furta a hankali, wanda ita Yaseen dake kusa da ita ne zai iya jiyo hakan, sosai taji tana son taji ɗumin mijinta sabda wannan sassanyar isar dake ratsa kowanne kafar ɗaidaikun gashin da yayi luf a fatar jikinta, a hankali ta ɗan matsa kusa da Yaseen tare da saƙalo hannunta cikin nasa, ta rungume kana suka ci gaba da tafiya har suka iso garden ɗin. "Alhmdllh, suna cikin ƙoshin lafiya" Yusra tace tana faɗaɗa fara'arta. Sake hannun Yaseen tayi kana ta ƙarasa gurinsu da sauri, tana shafa musu jiki, suka fara kuka a tare. Neman guri tayi kana ta zauna, tana son cewa Yaseen ya shigar da waɗannan dabbobin corridor tana tsoron amsar da zai bata sbda tasan ma ba yiwuwa maganar Tata zatayi ba, "Yusra tashi mu shiga ciki yamma tayi sosai, jiki babu ƙwari ta mike, tare da bin bayansa shi yana gaba, tana tana tafiya tana waigen dabbobin. Bayan tafiyarsu, dabbobin suka koma gefe su biyu, da rago da tinkiya, ragon yace "Najma gaskiya mutanen gidannan sunada kirki, musamman ma matar Wlhi tana da mutunci, wacce ragon ya kira da Najma tace Yaya Majeed, yanzu babu inda za'ayi mu koma kamar inda muke a da?" Majeed ɗin yace "Najma Ubangiji shine wanda zai iya yi mana sakaiyya, saboda babu wanda yasan mu mutane ne, kinga kuwa babu mai taimakonmu, Najma ta fashe da kuka irin na dabbobi kafin tace "Yah Majeed mun shiga uku, Baaba Lami ta cutar da rayuwarmu, wayo Allah" Majeed yace "inasha Allah zata ga sakaiyya fiye da abinda ta aikata mana" cikin Muryar kuka Najma tace "yah Majeed nidai na gaji da cin dusa da harawa dan Allah kazo mu gudu ko zamu sami abinci mai kyau muci" Majeed ya girgiza mata kai alamar a'a, kafin ya fara magana "Najma kiyi hakuri ki rungumi ƙaddara idan Allah ya taimakemu sai waɗannan mutanen su gane muma kamar su muke" Da wannan kalamin yai galabar kwantar mata da hankali. Waye Majeed? Wacece Najma? PLATEAU Jos Ɓukur park Akwai wani danƙareren gida mai kyau da tsari, amma mamallakan gidan basa zama a Nigeria sai ƙasar Egypt, Alhaji Abdullahi shine mahaifin su Majeed da Najma, Hajiya Salima itace mahaifiyarsu, shekarar Majeed 28yrs shekarar Najma 18yrs sun taso cikin gata da nuna kulawa, kasancewar mahaifin nasu yana da tarin arziƙi mai yawa, basu cika rayuwa a Nigeria ba, a Egypt sukayi karatu dukkansu, WATA RANA Sun dawo hutu, dukkansu har da iyayen, suna zaune a parlor, Dad yace "Majeed, ya kamata ka fara kasuwanci bawai ka dogara da karatu kaɗai ba, bance maka bazaka ribata da ilimin ka ba, amma yana kyau ka kasance mai hanyoyi da yawa" Dad yai maganar yana kallon Majeed, Kan Majeed a sunkuye cike da girmamawa yake cewa Dad ɗin, hakan ma yayi Dad Nagode ina alfahari da kasancewarka mahaifina, Allah ya albarkaci dukiyarka Dady" Dady yayi murmishi kana yace "Nagode da adu'oinka a gareni ɗan albarka" Najma ta kwaɓe fuska kafin tace "Dad nifa?" Dady da Momcy sukayi dariya, Momcy tace "ai ke yarinya ce" Majeed yace "wannan rawar kanta ma yafi ƙarfin ta, Washe gari 12:pm anty Asabe tayi sallama, cikin farin ciki Momcy ta tarbe ta, kasancewar a parlor ta samu Momcy tana shan Black tea, bayan Momcy ta tsiyayo mata, suka gaisa Anty Asabe tace "Alhajin ya fita ne?, Momcy tace "eh ya je anguwa Najma ta bishi daga nan zai sauketa a gurin wankin kai" anty Asabe ta taɓe baki tare da cewa "ya kamata ace Najma ta fitar da gwani duba da girman da tayi sosai" Momcy ta jinjina kai kana tace "anty Asabe ai Najma ƙaramar yarinya ce, dudu du ma guda nawa take?" Anty Asabe ta gwalo idanu kafin tace "ai kuwa tunda kun ɗauki rayuwar yahudawa dole ki faɗi haka" Momcy tayi dariya tare da cewa "ɗazu ma dadyn yake yiwa Majeed faɗa akan rashin sana'a, yace zai buɗe masa babban shago, Najma dai sai ta gama karatu, Anty Asabe ta zaro idanu, ita kam Momcy ma bata san tanayi ba, saboda idanunta suka kan wayar dake hannunta, anty Asabe ta miƙe cike da takaicin labarin su Majeed da Momcy ta bata, ta tsani taga Dad yayiwa wasu alkairi bayan ita, kasancewarta ƴar uwarsa uwa ɗaya uba ɗaya, ta kasance itace gaba dashi, bata ƙaunar Momcy da yaranta, shiyasa ta ɗauki alwashin sai ta haukatasu..." Afuwan please yau dai kunga pegin babu yawa, da naso in bari gobe sai nayi muku mai yawa, masoyan Na KASA JUREWA suka ce a turo musu haka, ayi haƙuri Please 👏 Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ Page 51-52 Bayan sun gama waya da Zayden ta wani lumshe fararen idanuwanta, tare da yin murmishi mai sauti, "gaskiya duk wanda ya faɗa soyayya zai samu farin ciki, amma ake ƙoƙarin a hanata, Wlhi yin waya da Zayden ko ta halin ƙaƙa ne sai ta yi" Duk wannan surutan a zuciyarta takeyi, lokaci guda ta rikice akan bawan Allahan nan, gabaki ɗaya ta kasa control ɗin kanta, babban burin ta a halin yanzu shine ta sake yin tozali dashi. Tayi nisa a tunani, Umaimah ta sake kiran sunanta, a karo na biyu, da sauri ta buɗe ido tana cewa "anty ta dawo ne?" Umaimah ta taɓe baki, kafin tace "wace anty wancan dai Sarkin nacin ne ya dawo wai kizo, nifa na fara zargin sonki yakeyi" Talatu ta zaro idanu kana ta sauko daga saman bed ɗin tana cewa "Umaimah yah Arman bazai yi soyayya dani ba, taɓɓ ki kalleshi ɗan gayu ina ni, ina shi?" Tai maganar tana kama haɓa. "Uhm kije dai kiji ko meye" Sai da Talatu ta kashe wayar, kana ta mayar da ita cikin kwalinta kafin ta ɗauki siririn mayafi kana ta fice, A parlor ta sameshi kamar ɗazu, yana zaune yana danna wayarsa, "sannu da dawowa yah Arman" ta faɗa tana yi masa murmishi, "Masha Allah, tsarki ya tabbata ga Ubangiji da yayi wannan Kyakkyawar halittar" ya faɗa lokacin da ya ɗora idanuwansa a kanta, "Zauna" yah Arman yace yana yi mata nuni da saman couch, zama tayi kana ta sunkuyar da kanta ƙasa, sannan ta fara tunanin ko tayi wani laifinne, sbda ita ba shi take kallo ba, kanta a sunkuye yake, shi kuma idanunsa a kanta yake, shi kadai yake magana da zuciyarsa "anya zan iya jure ɗawainiya da soyayyar Aysha, kodai in sanar mata ne?, idan har na sanar mata zata yimin wata fassarar, gara in bari idan ta mallaki hankalin kanta, saboda a yanzu kam Aysha batasan meye SO ba". Jin shirun yayi yawa, yasa tayi gyaran murya gami da cewa "yah Arman ko kana buƙatar wani abunne?" "Ah..ah..a'a" Maganar ta fito masa ba tare da yaso durbur burjewa ba, tana zaunen har yayi mata hoto bata sani ba, sai da ya gama ikonsa kana yace ta wuce" ta tashi ta bar gurin, dama abinda take jira taji daga bakinsa kenan, ƙarfe 5:pm anty Tasneem ta dawo daga gidan biki, lokacin Umaimah da Talatu suna kitchen suna yin abinci, ko da ta shigo babu kowa a parlor TV ma a kashe yake, ta fara ƙwala musu kira, Umaimah ce ta fito, Talatu na markaɗa kayan miya, sannu da dawowa Umaimah tayi mata, kafin tace "Aysha ma na kitchen" "Anty Tasneem na dariya tace "wato yau girkin ƴan mata zamu ci" Umaimah ma dariyar tayi kana ta koma kitchen. Not. Afuwan, yanzu zan daina kiran Talatu da sunanta na ƙauye, zan dinga kiranta da sunanta na asali wato, Aysha. Bayan anty Tasneem ta cire mayafinta, ta fito zuwa kitchen, lokacin Aysha na zuba farar shinkafa da wake a kula mai kyau, Umaimah kuma tana zuba miyar Stew a ƙaramar kula, anty Tasneem na shigowa ƙamahin miyar ya yi masa iso, cike da murmishi tace "Aysha wannan miya nasan ba iya ƙamshinta ba, dole sai tayi daɗi" suka kwashe da dariya dukkansu, Ayshar na yiwa anty Tasneem sannu da dawowa, ciro latas Umaimah tayi a fridge tare da tumatur da dafaffen ƙwai, ta zauna a kujera kana ta zuba a mazubi ta fara yankawa, anty Tasneem kam komawa ciki tayi dan ta watsa ruwa sbda anyi rana sosai, lokacin da suka kammala girkin har an fito sallahar magriba, Umaimah ta kai dinning ta jeresu, kana ta dawo tace "Aysha babu ɗan wani juice ne?,kinsan anty Tasneem sai tayi magana, tunda an saba yi" Aysha tace "Umaimah dare da yayi, yanzu wane irin juice kike gani za'ayi a wannan time ɗin?" Umaimah tace "ko watermelon juice da milk kawai" Umaimah ce ta haɗa juice ɗin, kana ta jefa ice block a ciki,kana ta zuba a jug mai kyau, shima aka kaishi can dinning" Sai da akayi sallahar isha'i dukkansu sukayi, lokacin da anty Tasneem ta fito parlor su Umaimah suna ɗakinsu, ta ƙwala musu kira suka hallara a dining kana table kana aka fara hidimar bawa ciki haƙƙinsa. Umaimah ce ta sa musu shinkafa da miyar kifi, ko wanne da plate ɗinsa, Bayan sun kammala cin abincin Aysha ta kwashe takai kitchen kana ta wanke sannan ta kifesu, Parlor suka koma suka ɗan taɓa hira, anty Tasneem tace "zata wuce ɗaki sai da safe" Suma ɗakin suka wuce, inda Umaimah ta haye gado, wayarta ce ta fara ringing ta ɗaga tare da maƙale murya suka fara hira ita da saurayinta, sosai Aysha ta nutsu tana sake karantar kalamai daga gurin Umaimah, sun daɗe suna waya, daga ƙarshe sukayi sallama har tana wani yiwa wayar kiss, Aysha ta sheƙe da dariya, Umaimah ta harareta, "Aysha Wlhi ga dukkan alamu idan kikayi zurfi a cikin soyayya zakice mu yara ne, dariya kawai tayi kana taje, kunna TV kafin ta haye bed, wayarta ta ɗauko kana ta kunna, kamar jira yake sai ga kiransa nan, babu ƙara saboda wayar a silent take, Aslmu alaikum my Omri (My lifetime) Babu wanda zai iya bayyanar da yadda zuciya ke ji idan ta kamu da so. Na mallaka miki zuciyata domin ki leƙa cikinta, ki ga irin yadda na kamu da son ki!, Wadannan kalaman da ya gaya mata, sai ta fara jin ta a wata duniyar ba wannan ba, sosai ta kamu da son Zayden saboda shi gwanine gurin iya tsara kalami, My Omri please kice wani abu, idan har kika hukuntani da rashin jin sautin muryarki bazanji daɗi ba, my Omri please" yai maganar yana sanyaya muryarsa, "I love You" tana faɗa ta katse kiran, saboda taji kunyar kanta, kalmar da tunda tasan meye a boko bata taɓa furtawa ba, a bakinta, amma ga shi yau itace take gayawa wani wanda take jin zata iya rayuwa dashi duk tsanani duk wuya, Umaimah kam mutuwar zaune tayi, sai kuma ta tuntsure da dariya, tana cigaba da kallon Aysha, in one time ta fashe da kuka, ita kanta bata san kukan me takeyi ba, sannan kuma bata da muradin Umaimah ta tambayeta wani abu dangane da kukan, gaba ɗaya ta kashe wayar tana jin ƙirjinta na bugawa Dum..dum..dum, Daga can ɓangaren Zayden, yana kwance a haɗaɗɗiyar doguwar kujera mai zaman mutum uku, miƙewa yayi da sauri fuskarsa yalwace murmishi ya fara rawa yana juyi cikin farin ciki, ya rasa a wane yanayi yake ciki, saboda tsabar farinciki ya fice daga room ɗinsa kai tsaye ya nufi side ɗin Umma, suna zaune a parlor ita da Abba, Zayden ya shigo cikin zunuɗi, tare da sallama, ya zauna kusa da Umma yanata murmishi, Umma dai ta kasa haƙuri tace "Zayd lafiya naga sai fara'a kakeyi kamar wanda aka yiwa kyauta?" Anzo dai dai inda yakeso, dan dama yanason ayi masa magana, da sauri yace "umma Wlhi budurwata ce tace tana sona, umma na jima ina jiran wannan ranar" A sukwane ya silale yabar ɗakin, saboda ya mance Abba na zaune can nesa dasu, Sosai kunya ta ƙamashi, a ƙasan zuciyarsa kuma yaji daɗin hakan, saboda Abba zai san da cewar yana neman aure. Sai da tayi kuka mai isarta kafin ta share hawaye, Umaimah tace "wow wannan soyayyar ta birgeni, kenan irin anyi zurfi a cikin soyayyar nan ne ko?" Ta kwashe da dariya. Aysha ta kasa ce mata komai, sai ma kwanciya da tayi barci ya ɗauke ta, itama Umaimah ganin babu abokiyar hira yasa tayi barci. KEFFI Ido biyu sukayi da Hajiya Zaliha, Saudart tayi mata kallon up and down kafin tace "waye ke?" Sosai tambayar ta ƙonawa Hajiya Zaliha rai, cikin fusata tace "ni uwarki ce, munafuka kawai wawuya wacce bata san muhimmancin rayuwarta ba" Saudart ta zaro idanu gami da cewa "kinga mama ina jin nauyinki, ki fitar min daga gida kar in yi miki abinda har ki mutu bazaki mance dashi ba" Hajiya Zaliha ta bugi ƙirjin Saudart kana tace "dan ubanki kiyi min abinda ubanki be yiwa uwarki ba ma kinji", sosai munannan kalaman Hajiya Zaliha da ta dinga yiwa Saudart suka tsorata ta, tabbas bata iya faɗa ba, ko musayar yawu da mutane, hakan yasa mayar da maganar ya zamo mata baƙon abu, hayaniyar ce ta tashi alhaji daga barci, dama yasan za'a rina, wai an saci zanin mahaukaciya, ya fito da sauri tare da wucewa ta gefen Saudart, rai a ɓace yace "Zaliha mai ya kawo ki, mai kikazo yi, Ban sallameki ba?" In one time ya jero mata waɗannan tambayoyin, Sosai tambayoyin da yayi mata suka ƙona mata zuciya, ji tayi kamar ya watso mata ruwan zafi, musamman da yake shirin zubar mata da girma a gaban ƴar cikinta..?, A hassale tace "wato ma tambaya kakeyi mai ya kawoni ko?, to nazo kiranka ne, kazo mu koma gida, Wlhi tallahi idan har baka zo mun tafi ba, bazaka ƙarasa barci cikin ƙoshin lafiya ba" Beyi mamakin jin kalaman da ta furta ba, sai dai ya nuna mata ɓacin ransa fiye da inda bata tsammani, "Zaliha kizo ki wuce gida kokuma Wlhi ranki ya ɓaci" Hajiya Zaliha tayi shewa gami da rangaɗa guɗa, cikin ɗaga murya tace "kafin ka ɓata min rai barin ɓata maka, tayi kukan kura ta janyo Saudart tare da zabga mata mari haɗi da dukanta ko ta ina, Saudart ta fashe da kuka tare da cewa "Wlhi sai na rama sai dai duk abinda zai faru ya faru, tana kuka ta cakumo wuyan rigar Hajiya zaliha ta fara kai mata haushi, guri-yayi guri, sbda sun kicime da faɗa abin babu kayan gani, Alhji ya kamo hannun Hajiya Zaliha, ta fizge tana yi masa "Allah ya isa ita ya cuceta ya gama da ita, yayi mata kishiya, ai sai da ta gaya masa inhar ya raɓu wata mace bayan ita Wlhi sai ta rusa masa farincikinsa" duk waɗannan maganganun ta dinga jera masa tana kuka, Saudart kam tayi galabar dukan Hajiya Zaliha, sbda har bakinta ya fashe ta gefe, ga ƙumbar farcen Saudart Mai tsayi, duk ta yaƙushe ta a fuska, duk da haka bawai ta saduda bane, yunkurin sake takalo Saudart ɗin suci gaba tayi, daga ƙarshe dai Alhaji yace "tunda ni ban kai in baki umarni kibi ba, ya kamo hannun Saudart suka shige ciki, da sauri ya buga ƙofar tare da yi mata key, Mamaki Alhaji ya bata, saboda bata taɓa tsammanin zai yi mata hakan ba, "wai ma tana ina ne har ya figi hannun wannan yarinyar ya wuce?" ta tambayi kanta, tayi kururuwar tayi abin dai babu sauƙi saboda babu wanda ya kulata, tunda mai gadi yayi musu bayani, ko wanne ya samawa kansa lafiya. Ɗakin da ya kawota yafi wancan nata kayan alatu, sai dai itama nata ɗakin yana da kyau dai-dai gwargwado, a saman kujera mai zaman mutum biyu ya zaunar da ita, "Habibty dan Allah kiyi hakuri" kafin ya kai ga sake furta wata maganar ta miƙe da sauri tana shirin guduwa, ya kamo hannunta tare da janyota ta faɗo jikinsa, "me kikeso" yai maganar yana rungume da ita, "ka sakeni" tai maganar cikin suɓutar baki, sbda tun a dama danne zuciyarta takeyi, tabbas ko kaɗan baiji daɗin wannan maganar da tayi ba, sai ya basar da abin da ta faɗa, tare da cewa "bazan iya sakinki ba, saboda bazan jure rayuwa babu ke ba, "innalillahi wa inna ilahir raji'un, so kakeyi wannan matar ta kasheni ne?" tai maganar tana fashewa da kuka, tafin hannunsa ya sanya a fuskarta yana share mata hawaye, kuka take yi sosai kai, ni mom Islam nace UHM Saudart taji cinya mai laushi tayi luff a jikin Alhaji, domin ta tsorata da munanan kalaman Hajiya Zaliha a kanta, har yanzu tana kukan taki yin shiru, yayi lallashin har ya gaji, "Ba wata mai jiki bace, shiyasa bai wani ji nauyin sake gyara mata kwanciya a jikinsa ba, cikin sanyin murya yace "Habibty ki zaɓi duk ƙasar da kikaga tayi miki nayi miki alƙawari zamu tafi a wannan satin" Tunani ta farayi, ya kamata tayi amfani da wannan damar, taje ta gano inda ƴar uwarta take, cikin Muryar kuka tace "SINGAPORE" yai murmishi tare da cewa "Habibty baki da matsala, duk inda kikeson zuwa a faɗin duniyar nan zaki tafi, inasha Allah nan da 5days zamu bar Nigeria, kafin nan na gama komai na shirin tafiyar, Yau ce rana ta farko da taji Alhaji ya birgeta, tunda ya amsa mata zuwa inda takeso, "Habibty..," ya kira sunanta, "na'am.." ta amsa, "Haɗamin ruwan wanka Please" yai maganar yana zame ɗankwalin kanta, tsintar kanta tayi da kasa yi masa musu, ta sauka a jikinsa a hankali, lokacin ana gaf da kiran sallahar asbha, kai tsaye toilet ɗin dake ɗakinsa ta wuce, tsayawa kallo tayi, saboda ko nata toilet ɗin bata shiga ba, shiyasa wannan ya kiɗimata, wasu na'urori ta gani wanda bata taɓa ganinsu ba, duk da ita ɗin ƴar boko ce amma wasu abubuwan sun shige mata duhu, ganinsa tayi ɗaure da towel ya tsaya a bakin ƙofar toilet ɗin yana kallonta, cikin sa'a ta haɗa masa ruwan wankan a bahon wanka, zame towel ɗin da yayi ne yasa ta kawar da idanunta daga gareshi, ya lura da hakan, sai yayi murmishi, "Habibty ke bazakiyi wankan bane?" Alhaji ya tambayeta, "Uhm ai gari be waye ba, kwanciya zanyi" Ya girgiza kai bai ce komai ba, koda ya ƙara sa shigowa toilet ɗin, ta taho zata wuce ta gefensa, a hankali ya kamota tare da rungumeta, kafin yace "ina buƙatar muyi wankan tare" ta kasa yi masa musu, saboda cikar burinta, amma bata amsa masa a fili ba, kanta a sunkuye, sbda kallon jikinsa yayiwa idanuwanta nauyi, tana tsaye kamar gunki ya rabata da duka kayan jikinta, kana ya kamo hannunta suka shiga a tare, wani sassanyar ƙamshi ke fita a ruwan wankan, yanayin ɗumin ruwan ya sanyata lumshe idanu, shiko yayi hakanne ko zai samu damar yin wasa da ita, domin ya kawar mata da ɓacin ran da take ciki, sbda yasan wacece Zaliha sbda tun auren saurayi da budurwa suke tare, cikin siyasa wanda itama bata gane ba, ya ɗan runtse idanunsa tare da cewa "ya Allah, kasancewarta mai tausayi da raunin zuciya yasa ta ce "lafiya?" ya fara mutsike idanu kai kace wani ƙaramin yaro, sai ta tsinci kanta da son ta hure masa idon, a hankali ta ɗan matso duk da a kunya ce take, kuma fuskarta sam babu walwalah, ta ɗan matsa kusa dashi kadan, kana ta kai bakinta gurin idanunsa ta fara hurewa, a hankali, in one time ya fara jin tsigar jikinsa na tashi, a hankali cikin siyasa ya sake kusanto da ita kusa dashi, ta gane hakan, sai ta sake matsawa, duk da bata sonshi, tana yi masa kallon adali saboda zaɓin da ya bata, kiraye-kirayen sallahar asbha da aka farayi ne, ya sata miƙewa da sauri tana cewa "zanje in sa kaya" "Zo ki yi wanka mana, ai bakiyi wankan ba" Da gudu ta fice, sbda inda taga yana ƙarewa halittar jikinta kallo, sanin babu kowa a gidan, kuma tana ganin idan ya fito komai yana iya faruwa, ai ta ruga ɗakinta da gudu, tasa key, jingina tayi a jikin ƙofar tana sauke numfashi.. A ɓangaren Hajiya Zaliha, tunda Alhji ya rufe mata ƙofa, tai ƙwafa tare da wucewa ɗakin da ƙawarta ke kwance, cike da masifa take tashinta, bayan ta buɗe ido tace "ki taso ai bamu ga ta zama ba, Wlhi tallahi sai na wulaƙanta yarinyar nan, sai ta gwammace da bata zo gidan mijina ba" da wannan alwashin tayiwa motarta key, mai gadin ma masifa ce ta addabesa ya buɗe get ɗin yana yi musu a sauka lafiya. KEFFI MOM AND Dad🤗 Bayan biki. Dady ya tsunduma siyasa gadan-gadan, a halin yanzu hankalin momy ya kwanta sosai, saboda maƙudan kuɗaɗen da take juyawa bugu da ƙari, kanta har wani girma yake daɗa yi idan har taga posting ɗin Dad madia, sai dai muce Allah ya bada Sa'a, Dad ya zamo ganinsa ba kamar da ba, ita kanta bata cika ganinsa ba, washe garin bikin suka koma sabon gidansu dake nan Abuja, A.Y.A, Masha Allah gida yayi kyau sosai, abin da yake bawa dangin momy na nesa takaici shine.. Idan har suka zo Abuja gidansu momy, sai anyi ta yi musu bincike, sometimes ma ace wai tana tare da baƙi, har ya zamo momy bata harka da talakawa sai masu kuɗi, koda ko a danginta ne, Wata ranar Saturday, ranar suna zaune a gurin hutawa ita da Dad, tulin kuɗaɗe ne a gabansa, wanda ni mom Islam da na gansu sai da na firgita, Dad ya kira asalin sunan momy wato Zainab, a iya tsawon zamansu Dad bai taɓa kiran sunanta ba sai yau, hakan yasa ta bada attention sosai ga maganar tasa, "Zainab inaso ki sani, rayuwar da zamu cigaba da yi da wacce mukayi a baya, tanada banbanci, saboda yanzu jama'a muke nema ta ko ina, domin mu samu mu cimma manufarmu, kuɗi ba shine zai bani mulki ba, yawan ƙuri'u sune samun mulki, abinda nakeso ki fahimta anan shine, wadannan kuɗaɗen na ware su ne, saboda al'umma, dole mu nemesu, abu na farko mun tattauna akan abubuwan da talakawa sukafi so, inasha Allah zamuyi ƙoƙari gurin ganin munyi musu, na farko zan shiga ƙauyakunmu inga gyaran da ya dace ayi, sannan zan baki baki naki kema nasan zakiyi ƙoƙari sosai" ya kai ƙarshen maganar yana warewa momy nata kuɗin, "Insha Allah Habiby zamuyi nasara da izinin Ubangiji" Momy ta faɗa sabda ta ƙarfafa masa guwaiwa. Ringing ɗin da wayarsa tayi ne yasa shi miƙewa yana ce mata, tayi abinda ya dace, yabar gurin. Tun yanzu an zuba masa police domin kariya, Tunani momy ta farayi, ashe dama sai da al'umma ake samun mulki, a ƙasa zuciyarta kuma tace "tabbas dole sai da al'umma, Bayan ta koma ɗakinta ta fara kiran ƙawayenta a waya da danginta, Allah sarki batayi tunanin zasu amsa gaiyyatar da tayi musu ba, sai gashi sun amsa mata, Wani hali da momy ta tsiro dashi tunda Dad ya fara neman takara shine... Ta watsar da dangin mahaifinta dana mahaifiyarta ya zamo iya mahaifiyarta da yayunta da ƙannenta kawai dasu take mu'amala, yau ga ranarsu tazo, Bayan one week A ranar da ƴan uwanta da ƙawayen da tayi masu buɗaɗɗen ido kwannan suma sun hallara, aka shirya party kai kace biki akeyi, harda raguna da saniya aka yanka sabda gidan ya cika sosai, Momy ta rarrabawa ko wacce dubu hamsin hamsin, kana ta ware wanda za'a rabawa mutane, A store ɗin da Dady yake ajiyar kayan abinci, aka je aka ɗibo shinkafa buhu 1k masara 1k wake 1k sai sabulu da omo, sai da ta tabbatar da an rarraba sbda har video aka dinga yiwa masu rabawar, nanfa gari ya ɗauka, sai Alhaji Aliyu..sai Alhaji Aliyu, aka dinga mammana hotonsa, duk inda ka girfta hotonsa zaka gani.., Yana fita kai tsaye gurin abokinsa ya nufa, abokinnasa shima ya taɓa riƙe muƙamin shugabanci, Bayan sun gaisa, Dad yake gaya masa, yayi duk abinda ya sashi, yanzu mataki na biyu yakeson su je, abokin nasa yayi murmishi, kana yace na tabbatar da gaske kakeyi, yanzu abinda za kayi, zaka ware kuɗaɗe masu tsoka zan kaika gurin wani bokanmu wanda aikinsa kamar yankan wuƙa ne, amma fa sai ka sake hannu" Dad ya sheƙe da dariya tare da cewa "indai kudi ne akwai su, bana tunanin a duniya idan magana ta kuɗi ce, babu abinda zai gagareni, abokin nasa yai na'am da maganarsa kai tsaye suka shiga jirgi suka wuce Lagos, bayan sun sauka, kai tsaye hotel suka kama, mai tsadar gaske, sai da suka gama shiryawa, da duk wasu maganganun da suka dace su gayawa bokan domin samun nasara, Bayan anyi sallahar azhar, sun fito daga masallaci kai tsaye suka wuce jeji inda boka yake, Sunyi tafiya mai nisa, dan har Dad yana cewa ai da sunzo gurin da mota shikam ya gaji, abokin nasa yace "amma ai akwai biyar bukata sosai, da wannan kalamin ya kwantarwa da Dady hankali, ya jure har suka iso gurin boka. Wani irin kururuwa sukaji daga dosowarsu gurin, can kuma suka ji wata mahaukaciyar dariya tare da wani irin sauti marar daɗin ji, da sauri Dad ya toshe kunnuwansa tare da firgita, abin ya bawa Dad tsoro da mamaki, suna tsaye sukaga boka ya faɗo a gabansu yayi shiga marar kyan gani, cikin hargagi mai sauti yace "nasan da zuwanku meke tafe daku?" Abokin Dad yayiwa boka bayani, boka yace ya amince zai yi aiki, saboda Dad yanada magauta sosai, akwai mutanen da basa son suga ya hau mulki dan haka zai taimaka masa, Dad yayi murmishi sbda hankalinsa ya kwanta da maganar da boka yayi, "Akwai wasu sharuɗa da zan gindaya maka idan har ka yisu to ka gama zamowa shugaban ƙasa" bakin Dad na rawa yace na...a...a..amince," boka yace "na farko idan har kukayi taraiyya da iyalinka inaso ka kawomin abinda ya zuba a zanin gadon da kukayi, na biyu kuma muna buƙatar jinin jarirai guda bakwai, idan har kayi wadannan ka dace" Boka na rufe baki Dad yace "zan iya kawo spam ɗin, amma jariran bazan iya kawosu ba" boka yace "akwai hanya amma dole zaka bada trillions, Dad yace babu matsala, A take a gurin Dad yayiwa boka transfer, hhh nasan zakuyi dariya ko? to boka harda system yake da. Kuɗaɗe na shigowa, boka ya ɗago wani abu a jarka, tare da miƙawa Dad kana yace "an kawo mana jinin jarirai yanzu, wannan jinin da kake gani shine, sharaɗinsa karka bari ko da matarka ce ta san ka fito tsakar gida, idan ka fito wanka zakayi dashi, sannan kasha sau uku, ragowar aikin ka bar mana, amma fa bazakayi sallah ba, har sai ranar da ka gama aikin, ƙa'idar gama aikin kwana bakwai, Dady ya karba yana cewa "ya amince," daga nan sukayi musayar number waya da boka, kana sukayi masa sai anjima, boka yace "kar su wani damu mulki zai samu" Ransu fess suka bar jeji suna farincikin, kai tsaye suka wuce hotel, da niyar a ranar zasu koma gida. Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ * Page 53-54 Tunda motar ta fara tafiya, Gudidi take gyangyaɗi har suka iso Kaduna, A television Garej driver yayi parking, har mutanen dake motar suka gama sauka bata farka ba, yaron motar yashigo cikin motar kana ya daka mata tsawa, a firgice ta farka, tare da lalubar ƙuɗinta da ta ƙullesu a hannun zani, ajiyar zuciya ta sauke, tare da kallon cikin motar taga babu kowa, da sauri itama ta fice kana ta tsaya a tashar tana kalle-kalle, ko wacce mace tazo wucewa da mayafi ko hijabi, hakan yasa ta kalli kanta, taga mayafin da tayi ɗammara dashi bashi da wani girma, haka ta yafa shi, kana ta fara tafiya. NA HIGA UKU🤣 Talatu ta faɗa tana ɗora hannu a kai, sai yanzu ta tuno ai tayi babban kuskure, a fili tace "ai da na sani inje gurin me hyagon nan in karɓo lambarsu, yanzu kam yauhe zan gane gidansu" Sosai ta shiga tashin hankali, saboda itakam bata san ina zata dosa ba, tabbas tayi ganganci yanzu ya zatayi?, Ta daɗe a tsaye a gurin, ga wata uwar yunwa dake addabarta, babbar damuwarta bai wuce inda zatayi tayiwa masu mashin kwatancen gidansu anty Jamila ba, Wani mai mashin ya zo kusa da ita, kafin yace "Hajiya tafiya ne?" ta ƙyalkyale da dariya tare da cewa "lallai mai mahin ɗinnan ka ganni ƴar yarinya dani kace min Hajiya?" maganar da tayi, yasa shi yin dariya, kana yace "ina za'a kaiki?" Gyara tsayuwa tayi, kana tace "dan Allah kasan gidansu Hajiya mama, tanada ƙanwa Jamila, ita Hajiya maman tanada yaro miskili marar mutunci, ka ganeta?" Mai mashin yace "ke a garinnan bafa mutum ɗaya bane, baki ganin al'umma ta ko ina, ai inaga ko a anguwar nan baza'a rasa Hajiya mama ba, ki hau sai in kaiki inda zaki, sai muyi tambaya, ko kin riƙe sunan anguwar ne?" Ta girgiza kai. Yace "hau mu tafi" a zuciyarsa ko cewa yake bazai yi tsayuwar banza ba, banda rashin mutunci ta kamo hanya ba tare da tasan inda zataje ba" ta hau yaja mashin suka wuce, a Zaria road ya ajiyeta, suka dinga tambaya kowa suka tambaya yace bai san wata Hajiya mama ba, daga ƙarshe ta sake hawa mashin tace ya kaita wata anguwar, ko musu beyi mata ba, duk inda sukaje sai ace musu basu santa ba, tace ya kaita anguwar masu kuɗi ko za'a dace, ya kaita Uganda, can wata anguwa, Gudidi ta sauka a mashin taje bakin get na wani gida ta dinga nocking aka ƙi budewa, ta sake zuwa wani, koda tayi magana dariya ma yaran suka dinga yi mata, dawo gurin mai mashin kana tace "mai mahin dan Allah ka koma dani inda ka ɗauko Ni" mai mashin ya cire baƙin gilashin dake idonsa kafin yace "na rantse da Allah anan zan barki" Gudidi ta turo baki gami da cewa "na higa uku, ai ba anan ka sameni ba, da zaka ce zaka barni anan" Ya galla mata harara tare da cewa "ki bani dubu uku in wuce, nama yi miki adalci saboda baki samu gidan da zakije ba" ta zaro idanu kana tace "amma ko baka da adalci, saboda cuta da mugunta kace in baka kudi, ban ma samu gidan da zani ba, yo ashe ma tsoronka nakeji" tayi maganar tana riƙe ƙugu, tana girgiza. Sakkowa yayi tare da kafe mashin ɗin, kana ya zaro belt ɗin wandonsa cikeda masifa yake cewa "Wlhi ko ki bani kuɗina ko fatar jikinki ta ji jiki" sosai Gudidi ta tsorata, saboda ba da wasa yake maganar ba, wani gida ta hango ana motsi da get alamun za'a buɗe tayi redi ana buɗe get ɗin ta arce da gudu, ta shige cikin gidan, mai gadi na tambayar ta daga ina take waye ya biyota, inaa, ta kasa bashi amsa sai kutsawa ciki da tayi ta cigaba da gudu, kasancewar kafin akai ɗakunan gidan da ƴar tafiya, wata ƙofa ta gani a bude, ta faɗa ciki tana sauke numfashi, zaro ido tayi lokacin da taga wani saurayi da budurwa suna kwance zigidir lokaci ɗaya jikinta ya hau karkarwa, ta kasa gaba ta kasa baya, a hankali ta fara ja da baya har ta samu ta fice a ɗakin, ta sake shiga wani ɗakin, babban parlor ta gani mai kyau, babu kowa a ciki sai ƙarar TV, kallon ƙofar tayi taga key a jiki, da sauri ta murɗa key ɗin kana ta zare, a gidan su anty Jamila taga hakan. Acan bakin get anata masifa da mai gadi da mai mashin, ya tubure sai mai gadi ya biyasa kudinsa, tunda har ya bari yarinyar ta shige, da mai gadi ya gaji da bawa mai mashin haƙuri yaja get ya rufe, mai mashin yayi kiran duniya mai gadi yaƙi budewa, Dole yaja mashin ya tafi, aiko sai da yayi Allah ya isa. Tsuru-tsuru tayi a parlon mutane, sai yanzu ma tsorata, tunani ta farayi idan har ta fita a wannan gida ina zata dosa, Wata mata ta fito daga wani ɗaki, a ƙalla matar zatayi shekaru arba'in a duniya, tana sanye da atamfa mai ratsin green and light pink, anyi mata ɗinkin doguwar riga, sai da ta gama ƙare wa Gudidi kallo, kafin tace "yarinya daga ina kike" Gudidi kam tayi nisa a tunani bata san anayi mata magana ba, har sai da matar ta taɓa mata kafaɗa, firgit ta firgita tare da juyowa, zuciyarta cike da tsoro tace "Hajiya dan Allah kiyi hakuri Wallashi zanyi miki aikatau" Hajiyar ta kalli Gudidi kana tace "aiki kuma, keɗin daga ina kike?" Gudidi tayi shiru bata ce komai ba, matar ta fita ta barta a gurin ta zubawa TV ido.kamar zata shige ciki, Kai tsaye ta wuce kitchen ta ɗibo mata jollof ɗin couscous wanda yaji kifi dasu carrot, a gaban Gudidi ta ajiye, kana ta buɗe fridge ta ɗauko mata zoɓo da ruwa ta ajiye mata, ba tare da ɓata lokaci ba, Gudidi ta ajiye cokalin a gefe tasa hannu kana ta fara ci, kamar wacce tayi sati bata ga abinci ba, Matar na zaune tana kallon Gudidi, sosai gudidin ta bata tausayi, sai girgiza kai takeyi, bayan ta gama cin abincin ta ture plate ɗin gefe, ta ɗauki gorar zoɓo ta shanye, ta ɗauki ruwan leda shima ta shanye, tare da yin gyatsa mai sautiii, "Hajiya dan Allah zan iya kwanciya?" Hajiyar ta gyaɗa mata kai, alamar eh ta kwanta, da gudu ta haye saman kujera 3sitter kana ta kwanta, lokaci ɗaya barci ya ɗauketa, Hajiya dai ta kasa tashi daga gurin Gudidi, ta jima a zaune a saman kujera mai zaman mutum ɗaya, tana ƙare mata kallo tare da tarin tambayoyi da tunani iri-iri,kwance a zuciyarta. Innalillahi wa inna ilahir raji'un, Ruqaiyya ta ambata kana ta fara ƙoƙarin janyo bedsheet tana rufe jikinta, Sabeer sai wani ƙwaƙumeta yakeyi, ita kuma ta ƙoƙarin suturta jikinta, cikin Muryar firgici tace "Sabeer ka rabu dani Sabeer ka ƙayaleni baka tunanin komai game da yarinyar nan da ta shigo ta fita?" tai maganar ƙirjinta na tsananta bugawa, "sai da nace miki bai kamata muzo gidanku ba, Gara mu haɗu a hotel kikace babu damuwa, kuma ai kince Mom ɗin naki ta fita ko?" Girgiza kai ta farayi tana kuka tana yarfe hannaye, cikin yanayi na damuwa tace "Mom ta dawo saboda na ji maganarta, nifa babbar damuwata yarinyar nan, duk da ban taɓa ganinta ba, amma na tsorata sosai, yanzu duk ba wannan ba, ka tashi kasa kaya ka fice gobe zamu haɗu a club" ta kai ƙarshen maganar tana haɗe hannayenta biyu alamar ban haƙuri, "shikenan, amman kinsan Wlhi kin ja min rai, Ruky bazan iya ƙarashe wunin yau ba tare da keba, dan haka zan tafi, i swear idan baki zo ba, ni zan sake dawowa" Sabeer ya bata amsa yayinda yake sanya rigarsa, "In...i...in...sha...inasha... Allah zan zo" ta faɗa tana miƙewa tsaye, saboda ta zumbula doguwar rigar da ta cire sbda zuwansa, "Ruqaiyya... Ruqaiyya... Ruqaiyya..mom ta fara ƙwala mata kira, sai da ta tabbatar da Sabeer ya fice kana ta amsa tana mutsike idanunta alamun daga barci ta tashi, lokacin da ta shiga parlon Mom ta sami Gudidi tana kwance tana barci, acan gefe kuma Mom ce tana daddana waya, Ruqaiyya ta ƙaraso jiki a sanyaye, ta durƙusa a gaban Mom kana tace "Mom gani" tana maganar tana sake mutsika idanu, Mom tace "dama inason zanje anguwa dan Allah ki kularmin da gida, karki fita ko ina" Ruqaiyya ta gyaɗa kai tana cewa "to" sai kuma ta sake kai kallonta ga Gudidi kafin tace "Mom wannan kuma wacece, a tsorace tayi maganar sbda gudun kar Gudidin ta tona mata asiri, Mom tace "barinje in dawo zanyi miki bayani, amma idan ta tashi ki bata ruwa tayi wanka" mom na gama maganar ta wuce bedroom ɗin ta, mayafi da waya ta ɗauka sai key car kana tayi musu sai ta dawo. Bayan fitar Mom Ruqaiyya ta fara roƙon Allah, yasa Gudidi ta tashi daga barci kafin Mom ta dawo, sabda idan har Mom ta dawo bazata samu damar yin magana da ita ba. Kai tsaye bedroom ɗin Mom ta wuce ta fara gyara bed kana ta shiga toilet tayi wankan tsarki, kana ta wanke ta share ko ina, ta dawo parlor ta goge kujeru sannan ta haɗa kayan wanke-wanke tayi, bayan ta gama ta kunna A.C kana ta fesa room freshener, ko ina ya ɗauki ƙamshi mai daɗi, A hankali sanyin A,C ke shigarta, ta fara tattare ƙafafuwa alamun sanyi takeji, sai kuma ta buɗe idanu tare da tashi zaune, tana sake ƙare wa parlorn kallo, Ruqaiyya ta shigo hannunta riƙe da tray na indomie sai ƙamshi ke fita, tunda sukayi ido biyu da Gudidi ta runtse idanunta tare da toshe baki, in one time jikin Ruqaiyya ya fara kyarma tasan asirinta zai tonu, amma sai ta wayance da yin murmishi tace "Baƙuwarmu kin tashi ne" Gudidi ta cire hannu a baki, sai ta fara ganin kamar ba ita ta gani da wani saurayi tsirara ba, gyaɗawa Ruqaiyya kai tayi, Ruqayya ta taso daga inda take zaune tace "Baƙuwarmu dan Allah inason in tambayeki" Gudidi tace "to" Ruqaiyya tace "lokacin da kika shigo gidannan baki ga wata budurwa da wani saurayi a ɗaki ba?" cikin sauri kamar wacce aka zabura Gudidi tace "tabbas na gansu tsirara aihuwar uwarsu da ubansu" sai da Ruqaiyya ta zaro idanu kafin ta sake ce mata, "kinasan me nakeso dake?" Gudidi tace "a'a" Ruqaiyya tace "inason ki yi shiru da bakinki Wlhi tallahi idan har naji kin gayawa wani sai na kasheki, sosai tsoro da firgici ya shiga zuciyar Gudidi, da sauri ta yayibo ɗan siririn mayafinta, ta fara shirin guduwa, saboda dama ance ana yawan kashe mutane a binni, hamdala Ruqaiyya tayi, saboda tayi nasarar tsoratar da ita, sbda ko a yanayin ta ma tasan ta tsorata sosai, "ki tashi kije kiyi wanka, zan baki kayana kala goma sai ki dinga sawa, amma kafin nan daga ina kike?" Gudidi ta riga ta firgita sosai tace "ni ƴar uwar Hajiyar gidannan ne, na dangin NoNo" Ruqaiyya kam bata gane wannan Hausar ba, ta ce "jekiyi wankan kawai" Ta miƙe ko ina nata kyarma yake, saboda a duk tunaninta Tana shiga banɗaki Ruqaiyya zata kasheta, ko da Ruqaiyyan ta nuna mata toilet ta shiga sai da tasa saƙata, kana tayi wankan a gurguje, bayan ta fito, taci karo da tsadaddun kaya wanda Ruqaiyya ta ajiye mata, sai dai duk masu gidan sa nono ne, itakam da babu komai a ƙirjinta, wata doguwar riga ƴar kanti tasa, tayi mata yawa, saboda Ruqaiyya tanada tsayi kuma shekarunsu ba ɗaya ba, sabda Ruqaiyya zatayi 23yrs, Ruqaiyya na fitowa tayi murmishi, kana ta ƙara so ta sanya maɗaurin rigar ta ɗaure mata, hakan ya taimaka mata gurin rage tsayin rigar, ta kawo mata man shafawa ta shafa, sannan tace "zan shiga bedroom ɗin Mom zanyi waya, duk wanda ya shigo kice bana nan, amma idan Mom ce kimin magana" Gudidi ta amsa mata da cewa "to" bayan shigar Ruqaiyya, sai da Gudidi ta tabbatar da Ruqaiyya ta rufe ƙofar, sannan ta fara shirye-shiryen guduwa, saboda tana ganin Ruqaiyya zata iya kasheta. Acan bedroom ɗin Mom, Sabeer ne ya dameta da kira, wai sai dai tazo Gidansa kokuma su haɗu a hotel shi bazan iya jure rashinta ba, haƙuri ta dinga bashi, yace sai dai suyi video call idan ta yarda, dole ta yarda tunda tana tsananin sonsa, ya sata ta cire komai na jikinta ta kafe wayar inda zai dinga kallon komai nata, sunata baɗalarsu, shima hakan yayi, yasata tayi wannan ya sata tayi wancan daga ƙarshe dai ta kwanta tana mayarda numfashi, dama da biyu yayi hakan yasan dole sai ta buƙaceshi, tana sauke wani fitinannen nishi tana cewa "Sabeer NA KASA JUREWA bazan iya jurewa ba, Please kazo da mota ka ɗaukeni Please my Sabeer" ransa fess dama abinda yake jira kenan, kasancewarsa mai wayo da dabara, ba wani jimawa sai gashi a ƙofar gidansu, ya kirata a waya, tace masa gata nan fitowa, sai da ta sake yin wanka kana ta sauya kaya, sannan ta fito, "ina kuma yarinyar nan ta shiga?" Ruqaiyya ta tambayi kanta tana ɗaura ɗankwali, ta fito ta zagaye ko ina bata ganta ba, ta tambayi mai gadi yace shima bai ganta ba, hankalinta a tashe ta dinga zagaye anguwarsu, tana dawowa ne ta hango motar Sabeer, ƙara sawa gurinsa tayi, ba tare da tunanin komai ba, yaja mota sukayi gaba... LAYLA Rai a ɓace ta ƙarasa shigowa gidan, da kuka ta shiga ɗakin mamanta, mama na zaune tana ninke kaya, Layla ta sameta, cikin Muryar kuka take cewa "mama zan ajiye aiki wallhi bazan iya ba, mama bazan iya JUREWA ba" Maman bata fahimci komai ba, ta matsar da kayan da take ninkewa cikin yanayi na damuwa tace "Layla meke faruwa? Dan Allah kar in sake ji kince zaki bar aiki" Hawaye na bin kumatun Layla tace "mama na kamu da soyayyar wanda bai san inayi ba, mama na furta masa yana ƙoƙarin hukuntani, Wlhi har wulaƙanci yayimin, mama bakiga korar karen da yayimin ba, ƙarshe cewa yayi ya tsaneni" Mama ta zaro ido, kana tace "kina nufin yace karki sake zuwa gurin aiki "Layla na kuka tace "eh" maman tace "inko haka ne ai bamu ga ta zama ba, Wlhi tallahi sai inda man mu ya ƙare, amma fa kinsan malam mai yanzu-yanzu aikinsa akwai tsada abinda nakeso dake yanzu, kiyi hakuri ki bar min komai a hannuna tunda yace "abinda zeyi kenan kawai ki ƙyaleshi, ni zan ji da komai" mama ta kai ƙarshen maganar tana kwashe kayan ba tare da ta ƙara sa ninkewa ba ta kaisu uwar ɗaka, ta ɗauko hijabi tana cewa "yanzu nawa ne a gurinki?" Layla tace "dubu biyar, amma ai yau za'ayi mana albashi, mu jira zuwa anjima mama" Maman ta ajiye hijabin, ta shiga kitchen kana tace mata "idan kuɗin ya shigo kiyimin magana" Kai tsaye ta wuce ɗakinta tare da tunanin idan har bata mallaki Ma'aruf, ba zuciyarta tana iya fashewa, tana tsaka da tunani ƙarar alert ya shigo wayarta, ihu ta kurma tare da duba alert ɗin, ware idanu tayi tana cewa "Allah na gode maka, zan mallaki wannan haɗaɗɗen gayen ko ta halin ya ya" da gudu ta nufi inda mama take, cikin farin ciki tace mama kuɗi sun shigo 100k yanzu ya za'ayi?" Mama tace "jeki ciro dubu talatin, kinsan ance komai ayishi da zafi zafi yafi, ke ƴar nan idan har kika auri wannan mutumin ba ni kaɗai ba, har dangina sun warke da nera, mama ta janyo hijabi ta fice tana kiran Layla, a tare suka tafi, Layla na cire kuɗin a POS ta miƙawa mama 40k ta riƙe 10k dama 50k ta ciro ya zamo tanada 15k a hannunta, kai tsaye mama ta wuce bakin titi, nan ta wuce baban Layla a majalisa, mashin ta hau ta gaya masa anguwar da zai kaita, bayan sun iso ta sauka, kana ta sake hawa wani mashin ɗin da zai kaita ƙauyen da take son zuwa, daga gefen hanya mai mashin ɗin ya ajiyeta, ta bashi kudinsa kana ta ci gaba da tafiya, tayi tafiya mai nisan gaske har haɗa gumi takeyi, tana tafe tana ta saƙar inda bikin Layla zai kasance idan har tai nasarar samun Ma'aruf, Tana isowa gurin wata tsangaya ta tsaya tare da ɗagawa malamin hannu, sbda yana tare da almajirai, Malamin na ganinta ya washe haƙora, saboda yanayi mata aiki sosai tana kawo masa mutane, aikin mallakar baban Layla ma ita tayi masa, Tashi yayi daga inda yake zaune, kana yace suci gaba da karatu, iso yayi mata zuwa ɗakin da yake karɓar baƙi, bayan mama ta zauna suka gaisa, ta ce masa "dan Allah ya taimaketa yarinyarta tana kwance babu lafiya ta kamu da soyayyar wanda take yiwa aiki a Company ɗinsa, sun rasa gane kanta" malam yayi murmishi kafin yace "Hajiya wannan duk mai sauƙi ne, wato matsalar shi wanda takeso shine... Bayi da ra'ayin soyayya, sannan bai sanya mace a lissafinsa ba, amma idan har tace zata iya zama dashi a haka, zanyi mata aiki mai ƙarfi wanda zan janyo hankalinsa ya karkato gareta" Mama tayi shiru, kafin tace "malam bari in kirata kar ayi abun da ka" Malam yace "babu network anan, ki fita can waje zakiga wani ƙaton dutse anan muke samun network" Mama ta fita tare da hawa saman Dutse kana ta fara lalubar number Layla, Layla na ganin kiran mama tai saurin ɗagawa, cikin farin ciki take cewa "mama an dace ko?" Mama tace "Layla kina jina?" Layla ta amsa da "eh, " Tayi mata dukan bayanan da malam yayi mata, kana tace "kin amince ayi aikin?" Layla tace "eh na amince" Mama ta katse kiran ta koma gurin malam, tace ayi aiki kawai, malam yace "yanzu ma kuwa, tambayar sunan wanda Layla takeso malam yayi, mama tace "Ma'aruf" Malam ya zuba wani irin ruwa a ƙwarya kana ya fara ƙwalawa Ma'aruf kira da ƙarfi, sai ga Ma'aruf a cikin wannan ruwan ya baiyyana, gashi a zaune a office yana shan coffee, malamin ya fara wasu surkulle wanda ni kaina ba riƙe su nayi ba, daga ƙarshe ya ɗibi ruwan a gora ya miƙawa mama, kana yace a kaiwa Layla tayi wanka dashi babu sabulu, sannan ga wannan powder idan zataje Company ta shafa, ko wani saurayi ya ganta babu damuwa ai da sunan wanda takeso akayi aikin" mama tace "to malam mun gode sai dai baka faɗi abinda za'a baka ba?" Malam yayi dariya, kana yace "kuɗin aikinku dubu talatin da biyar" mama ta ƙirgo ta miƙa masa, kana tayi masa sallama, ta fito. Cike da fatan nasara ta ƙara so bakin titi inda zata samu abin hawa, mai mashin na zuwa ta hau suka wuce anguwarsu, kasancewar idan daga nan zaka tafi ana samun mashin direct zuwa unguwarsu, Har ƙofar gida mai mashin ya sauketa, ta shige gida zuciyarta fal farinciki, lokacin anata kiraye-kirayen sallahar magriba, sai da tayi sallah kana ta zauna bawa Layla labari, har suna tafawa saboda farinciki, ta miƙawa Layla ruwan maganin da Powder tayi mata bayani, kana tace "bata son mahaifinta ya sani, cikin sirri sukayi abin, har baba ya shigo bayan an idar da Sallah, ya tambayi mama ina taje, tace masa gidan wata ƙawarta, bai sake cewa komai ba. Washe gari Layla ta ɗau alwashin bazata je aiki ba, zata gwada ta gani maganin yana aiki, kwanan ta biyu babu wanda yai cigiyarta a gurin aikinsu, sosai ta fara damuwa saboda gani takeyi maganin ma baya aiki, ƙarfe 10:am ta kwanta barci mai cike da mafarki mai daɗin gaske, wayarta ta fara ruri, tsaki taja saboda mafarkin masoyinta takeyi gashi wanda yake kira ya katseta, da sauri ta ɗaga kiran cikin tausasa murya tace "Sir Barka da safiya da fatan kana cikin ƙoshin lafiya" ya Subhanallah ji yayi kaf duniya babu Muryar da takai ta Layla daɗi, bayan sun gaisa shine har da ce mata wai yayi missing ɗinta, sannan yana son tazo office idan bai ga kyakkyawar fuskarta ba bazai iya yin aikin komai ba, sosai ta dinga furta masa kalamai masu tsayawa a zuciya cikin sanyin murya wacce ta sake Ratsa zuciyarsa da zallar soyayyarta, Bayan sun gama waya, shine har da ce mata I love you, da wasu hote things. Tana ajiye waya ta shirya cikin sauri tare da baɗa powder har taso tayi mata yawa, Koda taje gurin kayanta ta jima tana zabar kayan da zai dace da shigar da takeson yi, saboda yau ranace ta musamman a gareta, wata baƙar doguwar riga ta ciro wacce akayi mata tattara ta gaba, anyi mata ado sosai da pink and golden ɗin zare, kana an yalwata ta da stone masu walwali, ga wasu tutoci a zagayen jikin rigar, mayafin rigar tayi rolling dashi kana taje gaban mirror ta ƙare wa kanta kallo, ko ba'a gaya mata ba, ta sani tayi kyau sosai, tasa pink lipstick tare da fesa turaruka masu ƙamashi. Hand bag ɗinta ta ɗauka kana ta rataya, sannan ta ɗauki farin mayafi ta ninkeshi a kafaɗarta, ta fito parlor sai zuba ƙamshi takeyi, Mama ta kalleta cike da ƙauna irin ta ɗa da uwa, tayi murmishi kafin tace "har na hangoki a gidan Ma'aruf, suka kwashe da dariya, Layla tace "mama inasha Allah, adu'arki ai karɓaɓɓiya ce a gurin Ubangiji". Mama tayi mata Allah ya kiyaye ta fice zuwa company. Afuwan kuyi hakuri baku samu update da wuri ba, Wlhi nayi baƙi ne, sannan ina jiran shar'hi, wanda suke son shiga group ɗin da nake posting suyimin magana WhatsApp 08141799224 Mom Islam ce...🤙 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam_ _SANARWA_ Aslamu alaikum masoya makaranta littafin NA KASA JUREWA, kuyi haƙuri da tsaikon da ake samu gurin posting, jiya na samu matsala da WhatsApp, yau kuma yarinyata ta tashi babu lafiya, alhmdulilah jiki yayi sauƙi, akwai wata sanarwa da naga ya dace in yiwa masu bibiyar labarin, idan har na kai page 50 zan dinga posting ƙarfe 12:pm insha Allah, sannan inayi muku albishir da cewar, daga yanzu zaku dinga samunsa akan lokaci da izinin Ubangiji, masu Arewabook posting ɗinku special ne. Page 55-56 Washe gari sunada makaranta dan haka ta shirya da wuri, anty Tasneem da Umaimah ne suka ƙara sa aikin gidan, tana fitowa harabar gidan ta hango motar yah Arman, mamaki ne ya kamata sai ta ci gaba da tafiya, har ta iso inda motar tasa take, "yah Arman ina kwana" ta gaishe shi tana ɗan sunkuyawa, "lafiya lau ƙanwata da fatan kin tashi lafiya" ta gyaɗa masa kai, tare da buɗe gidan gaba ta shige, bayan ta rufe murfin motar, yayiwa mai gadi horn suka fice, tunda suka fara tafiya take ta kalle-kalle, shi ko idanunsa suna kanta, duk wani motsi nata akan idanunsa takeyi, ikon Allah ne kaɗai ya kaisu makarantar, domin kuwa bai mayar da hankali ga tuƙinsa ba, mai gadin makarantar nasu na ganin mota ta taho, ya miƙe da sauri yana buɗe get, har cikin makarantar yah Arman ya shigar da ita, bayan ta fito yace "Aysha.." ta amsa da cewa "na'am.." Kamar ba zai yi magana ba, sai kuma yace "kinzo da kuɗi ne?" "Eh yaya" ta faɗa tana kama hanyar tafiya zuwa ajinsu, tunda ta fara tafiya ya zuba mata idanu, har ta ɓacewa ganinsa, sannan ya ja motar kana ya fice daga cikin makarantar. Da sallama ta shiga class ɗin, wasu ƴan mata guda biyu suka amsa mata fuska cike da fara'a, suna ce mata Aysha Barka da zuwa" duk da bata wani daɗe da shiga makarantar ba, ta fara sabo da ƴan matan ajinsu, sosai ta sake wayewa idanunta suka sake buɗewa, sabda ƴan matan ajin nasu duk wasu sun girme mata wasu kuma ta girmesu, alhmdulilah karatunta yana tafiya inda ya kamata, tunda wasu ma gurinta suke zuwa su tambayeta abinda basu ganeba, Ko da aka fita break ƴan ajin nasu basu fita ba, kasancewar suna meeting akan inda zasu yi birthday ɗin ɗaya daga cikin ɗaliban mai suna Laurat, ko wacce tana faɗar abinda zata kawo, dai-dai ƙarfinta, Aysha tayi murmishi kafin tace "nikam zan zo ayi aiki tare dani, idan har na samu abin kawowa zan kawo" Nan fa suka kaure da ihun murna, suna class har aka dawo break, a ranar malamai huɗu ne, suka shigar musu aji, kuma alhmdulilah duk wani malami da ya shiga ajinsu yana alfahari da basirarsu saboda suna ƙoƙari sosai, bayan sunyi sallahar azhar suka koma aji, yau kam da wuri aka tashesu dan basukai 6:pm ba, saboda ankai wata Malama Hospital, Ta rasa inda za'ayi ta koma gida, ga shi tsakanin makarantar da anguwarsu akwai nisa sosai, shawarar taje office ko akwai mafita ne ya faɗo mata, bayan tayi sallama shugaban makarantar ya amsa kafin yace "yarinya lafiya?" Aysha tayi rau-rau da idanu kafin tace "Dama number wayar dreban gidanmu ko ta yayana nake nema.." Shugaban makarantar ya buɗe wani babban littafi wanda suke ajiye number saboda irin haka, kasancewar ita bata jima a makarantar ba, yasa ya gane sunan yah Arman, ya ɗau number tare da kiransa, ringing ɗaya wayar yah Arman tayi kana ya ɗaga, bayan sun gaisa shugaban makarantar yace "dama mun tashi ɗalibai ne, sakamakon wata Malama babu lafiya an wuce da ita asibiti, Yah Arman yace "okay ta jirani gani nan zuwa" Kallon tulin file's ɗin dake gabansa yayi, saboda ya fara cikewa kenan aka kirashi, shi kuma bayajin zai iya haƙura ta hau mashin ɗin wani ko adaidaita, yana tsaka da tunanin tafiya makaranta, PA ɗinsa ta sake shigowa a karo na biyu, "Sir dama nazo in gaya maka ne, ya kamata a cike takardunnan a yau saboda yin hakan yanada muhimmanci sosai" "Naji..." Shine amsa da ya bata, koda tayi masa godiya ta fita, tsaki yaja mtswww, tare da tashi tsaye, ya ɗauki key car ɗinsa, cikin sauri dan baya buƙatar wani dakatar dashi, ya shiga mota kana ya fice da a guje, yayi gudu sosai kafin ya iso makarantar, a waje yayi parking motarsa kana ya fito ya shiga cikin makarantar, tana zaune ita da ƙawarta, Laurat kasancewar itama bata da number kowa na gidansu sannan bata je office ta tambaya ba, sukan ɗanyi fira jefi-jefi kafin Yah Arman ɗin ya iso, yana isowa inda suke Laurat ta gaishe sa, kafin Aysha ta gaishe sa itama, amsa musu yayi a lokaci ɗaya, tare da cewa "Aysha wacece wannan?" Aysha tayi murmishi kafin tace "yah Arman ƴar ajinmu ce" "Me yasa bata tafi gida ba" Laurat ta karɓe da cewa "drivern mu ne bai zo ba" Yah Arman yace "okay muje sai in saukeki a hanya" Laurat tace "ai sai na rigaku sauka ma" Suka wuce zuwa mota, Yah Arman da Aysha suna gaba, Laurat tana baya, sunyi tafiya ba mai nisa sosai ba, suka iso ƙofar get ɗin gidansu Laurat, kasancewar gidan yana bakin hanya, tayi musu godiya kana ta fita tare da ɗagawa Aysha hannu tana murmishi, Sunyi tafiya mai nisa kana ya waigo ya kalleta sannan yace "Aysha ana karatun kuwa?" Ta gyaɗa masa kai, Cikin yanayi na bada umarni yace "karki kuskura wani namiji ya fara wata magana dake, a school ko a hanya ke ko a ina ne, wlhi idan har kika fara soyayya Aysha kin cuci kanki, sbda inaso kiyi karatu sosai ki zamo wa iyayenki abin alfahari" Aysha tace "insha Allah yah Arman, Nagode sosai" Koda suka iso ƙofar gidan anty Tasneem, bai shiga ba, ya ajiyeta a bakin get, tayi masa Allah ya kiyaye hanya, kana ya wuce. Kafin ta kai ga shiga gidan, sai da ta daɗe a tsaye tana tuno faɗan da Yah Arman yayi mata, lokaci ɗaya zuciyarta ta kasu gida biyu, ɗaya tana ce mata, tabbas Aysha kinyi ganganci, ɗayar kuma tana ce mata "inda kika fara samun farinciki bai kamata kiyi wasa da damarki ba, ga shi Zayden yana mugun sonki kawai ki mance da batunsa, Ko wacce shawara ta yanke oho, kai tsaye ta wuce cikin gidan tare da yin sallama, sai da ta gaishe da mai gadi kana ta shige ciki. A parlor ta samesu da Anty Tasneem da Umaimah suna zaune a saman kujera suna hira, sannu tayi musu kana itama tayiwa kanta mazauni tana cewa "wash na gaji" Umaimah tasa dariya tare da cewa "haka muma muka sha fama da wannan zirga-zirgar" Aysha ta turo baki gami da cewa "anty bakiga na dawo da wuri ba?" Anty Tasneem tace "wlhi kinga tambayar tana bakina, amman dai lafiya ko?" Aysha tace "ai wata Malama ce babu lafiya" Sukayi mata adu'ar samun lafiya, Umaimah tace "barin taimaka in kawo miki abinci, Aysha ta washe haƙora tana dariya. SINGAPORE Buland island Wani haɗaɗɗan ɗaki Reed ya shigar da Thabit, cikin kakkausar murya yake gaya masa ɗakin sirrinsa ne, saboda kaf duniya bashi da kamarsa, ɗaki ne wanda aka gina shi da zinare, ko ina walwali yakeyi, sai dai shima ɗakin a tsafe yake sosai, a saman wata kujera mai zaman mutum biyu suka zauna, abin mamaki, a hankali kujerar ta fara tafiya har ta kaisu ga wani rami mai kyau, ramin an sarrafashi da gwala-gwalai, sannan komai na cikinsa gold ne, Oga Reed ya kalli Thabit kafin yace "wannan guri da kake ganinsa, idan har mutum ya shiga ba tare da amincewata ba, gawarsa za'a gani, sannan waɗannan gwala-gwalai da ka gansu mallakina ne, yau ma za'a sake kawomin wasu a cikin dare" Thabit ya jinjina kai, kafin yace "baka da matsala dani shugabana ni mai biyayya ne ga duk wasu abubuwan da ka sakani zanyi maka" Oga Reed yai murmishi kafin yace "yayi dai-dai, yanzu ya kamata mu koma ɗakin da buka baro, sbda inason mu tattauna wasu muhimman abubuwa" Thabit ya jinjina wa Oga Reed kai tare da binsa suka koma ɗakin da suka baro a da, Thabit ya ɗauki school bag ɗin da ya shiga gurin Oga Reed da ita, zuge zip ɗin baya yayi kana ya ciro wani ƙaton mangwaro jajir dashi, sai dai jan da yayi bai hanashi yin tauri ba, Thabit ya miƙawa Oga Reed, Oga Reed ya miƙa hannu tare da cewa "Me ya kawo mangwaro cikin shirin da muke son aiwatarwa?" Thabit yai murmishi kafin ya juya bayan mangwaron kana ya sanya hannu ya tura ɗan yatsansa sai ga shi ya ciro sabon memory card, ya miƙawa Oga Reed, Kana yace "wannan memory card ɗin da kake ganinsa akwai abubuwan da zasu amfani tafiyar da zamuyi kawai ka tsaya ka kalleshi daga farko har ƙarshe, Da sauri Oga Reed ya janyo system ɗinsa kana ya jona memory card ɗin, ya buɗe, videos ya gani sunkai kala uku, ya kunna na farko, sosai videon ya ja hankalinsa, sakamakon tare wasu jiragen ruwa da akeyi, abin takaicin ma, nasa ne, jiragen ruwan sunkai su biyar, amma duk an riƙesu, wasu a cike da ƴan mata, wasu kuma an cika shi da miyagun kwayoyi, wani an cika shi da magunguna masu cutarwa, wasu kuma an cikosu da ma'adanai na ƙarshen shine wanda aka cika shi da wasu manyan kwalaye ko meye a ciki oho.., Kafin Oga Reed ya kai ga kallon video na biyu, hankalinsa in yayi dubu ya tashi, rai a ɓace ya miƙe tare da kashe kallon, kana ya juya ga Thabit sannan ya marairaice idanu, ya sani idan har waɗannan jiragen ruwan suka salwanta, tabbas kashinsa ya bushe har gida za'azo a ƙamashi, sboda bashi da tarin ƴan matan da zai biyasu dashi, a yau yau ɗin nan ya ƙuduri aniyar ɗaukar ƙwaƙwaran mataki akan wannan ɓarna da ake shirin yi masa, Yace "ɗan uwa Thabit Please I need your help, kaima zaka more duniya idan har ka taimakamin wannan lamari bai faru ba, Thabit yace " Oga baka da matsala dani, dama kuɗi na fito nema saboda talauci ya isheni tabbas idan na zauna baƙinciki zai kasheni" sosai hankalin Oga Reed ya kwanta, ya matso kusa da Thabit kana yace "yanzu me kake ganin ya kamata muyi?" Thabit yai shiru da alamu yana nazari ne, ya daɗe bai cewa oh Reed komai ba, daga ƙarshe dai yai gyaran murya kafin yace "Oga kuɗi zaka fitar masu yawa, saboda mu siye manya manyan masu ruwa da tsaki a ƙasarnan, ta inda ko me zaka shigo dashi babu mai yi maka magana, ya kasance duk wata kana biyansu lafiya lau fa" Oga Reed yace "tabbas na daɗe ina tunanin hakan amma kasan me?, ya za'ayi su fahimceni?" Thabit yace "karka damu zasu fahimta" Cikin ƙoƙari irin na Thabit ya fara ƙoƙarin gwada number Prime minister, abin mamaki shine oga Reed yace "Thabit ya akayi ka samu numbersa kai tsaye?" Thabit yayi murmishi gami da cewa, idan har kanason dukiya dole ka yi faɗi tashi gurin ganin ka cimma manufarka" Oga Reed ya jinjina kai tare da cewa, amma kana ganin Prime minister zai iya gyara komai?" Thabit yace "eh amma fa sai ka saki kuɗaɗe" Iya Reed ya gyara zama kafin yace "indai kudi ne babu matsala nidai fatana komai ya tafi dai-dai kar a samu matsala". Daga nan suka fara shirya yanda komai zai tafiyar musu dai-dai, Agogon sanarwa ne ya buga daga ɓangaren hagu, Reed ya kai dubansa ga agogon kafin yai tsaki, tare da cewa "shagali za'ayi bana jin zan iya aiwatar da komai saboda wlhi ina cikin wani hali, bana jin daɗin yanayin da nake ciki a yau" Ya kai ƙarshen maganar yana miƙewa tsaye kana ya fara zagaye ɗakin, Thabit ya miƙe tsaye shima, kana ya tako har kusa dashi sannan ya dafa kafaɗarsa, cikin ƙarfafa masa guwaiwa yace "Oga Reed ka kwantar da hankalinka, waɗannan ƴan mata da ka tara, kamar inda kace idan an tashi siyar dasu akwai kuɗi sosai, bai kamata mu saka musu fargaba, ni Thabit zan jagiranci shagalin ina fatan zaka goyamin baya" oga Reed yayi murmishi kafin yace "gaskiya Thabit bani da kamarka, ina alfahari da kasancewar mu tare, fatan alheri abokina" Thabit ya koma ya zauna tare da fara latsa wayarsa, Acan ɓangaren su Misha, ita da Neria suna zaune a parlor ko waccensu da glass cup a hannunta table ɗin dake gabansu an jereshi da faifan wainar ƙwai da chips na dankali da Biryani, hankali kwance suke cin abincin, kasancewar lokacin bai wuce 7:pm ba, cikin yanayi na jin daɗi da annashuwa Misha tace "Neria ya kamata ki tashi mu shiga boutique mu zaɓi kayan da zamu sa, kinsan time yana tafiya fa" Wacce Misha ta kira da Neria, wato ƙanwarta uwa ɗaya uba ɗaya da bata sani ba, tace "anty Misha Please muje ki zaba min" suka tashi kai tsaye suka wuce gurin zaɓar kaya, akwai wani tsari da gidan nasu yake da, duk wanda zai karɓi kaya sai an bashi wani kati, sai ya wuce gurin karbar kayan, kasancewar gurin akwai kasuwanni kuma duka domin waɗannan ƴan matan, sannan duk wani motsi na kowa yana tafin hannun OGA Reed, hakan yasa babu wanda yake yunkurin cutar dashi, CCTV tsaf zai nuno kowa. Ƙarfe 8:pm ilahirin ƴan matan dake cikin wannan gida suka fito, ko wacce da kalar adon da tayi, amman duk cikinsu babu wacce ta sanya rigar da ta kawo mata gwaiwa, daga iya cinya ne, sai wacce da kaɗan ta wuce mazaunanta, cikin taku na isa da sarauta kai kace wani Sarki yake takowa, tun da ya fara idanun ƴan matan dake estate ɗin ya dawo kana Thabit dake takowa cikin hall ɗin, yana sanye da kaya irin na sarakai, tabbas duk wani mai fahimta ya fansa yasan shi ɗin musulmi ne, domin kuwa bai yi kama da kalar kafirai ba, Yana tafe securities na biye dashi har ya ƙaraso cikin hall ɗin, aka fara yi masa tafi, Kai tsaye ya wuce kyakkyawar kujerar da aka tanadar masa, bayan ya gama jawabai akan ko wacce budurwa tayi shagalinta iya son ranta babu mai takura musu, daga ƙarshe aka sake kida ko wacce ta tafi gurin shaye-shaye, wasu kuma suna can tare da samari ana holewa, Misha ce kwance saman ƙirjin wani saurayi, wanda shima yana ɗaya daga cikin mutanen gidan, ba wai iya mata suke ɗaukowa ba, harda maza, saboda su dinga taraiyya da matan, sosai. Nocking aka farayi da ƙarfi, saurayin ya miƙe tare da cewa "Sir Thabit yana magana da Misha" da sauri ta miƙe a zabure tare da yayibar kayanta ta sanya, tana cewa "bansan laifin da na aikata ba, i know babban abokin OGA ne, ta mike tsaye tare da ɗaukar handbag ɗinta kana ta fice. Sauri-sauri gudu-gudu takeyi har ta iso sashen da Thabit yake, nocking tayi jiki na karkarwa, "Yes come in" ya faɗa kana ya mayar da hankali kan wayarsa, jiki a sanyaye ta murɗa handle na ƙofar kana ta buɗe, tare da shigowa ta tsaya a bakin ƙofa, "Barka da dare" ta faɗa cikin harshensu, amsawa yayi da yauwa Barka, tare da ce mata ta ƙarasa, har yanzu jikinta bai daina ɓari ba, ta ƙaraso tare da tsugunawa, cikin girmamawa tace "gani" tashi ki zauna" ya mayar mata da maganar da turanci, ta tashi zaune har yanzu zuciyarta na ci gaba da tsinkewa, in Cold voice yace "kece Misha?" Ta gyaɗa masa kai, ƙwarai ya lura da da yanayin rashin nutsuwar da take ciki, a hankali ya matso inda take kafin yace "yaushe rabonki da iyayenki?" Sosai maganar ta juyar mata da ƙwaƙwalwa, saboda a iya tsawon zamanta a nan babu wanda ya taɓa yi mata wannan tambayar sai shi, bata da wannan amsar, sannan ko tayi yunkurin aikata wani abun sai taji rayuwar gurin yana sake shiga ranta, a hankali ya furta, "Rabonki da iyayenki tun ranar da mahaifiyarki ta haifeki, ke ba ƴar Nigeria bace, kana ke ba Christian bace, amman inason wannan maganar ta zamo sirri tsakanina dake, ni nan da kike gani hhhh, yayi dariya mai sauti... KEFFI Ikon Allah ne kawai ya kai Hajiya zaliha gidanta, saboda tsananin ɓacin ran da take ciki ko kaucewa gargada batayi, ko da ta iso bakin get na gidanta, wani mahaukacin horn ta yi, wanda yasa mai gadi buɗe get ɗin a tsorace, yana ganin Hajiyar ce ya ɗaga mata hannu, idanunta sun rufe ko ganinsa ma batayi ba.., ba a inda ake ajiye mota ta ajiye motar ta ba, tsabar zafin zuciya, tace "Hadiza yau kam naga tashin hankali, Hadiza ta hau tafa hannu gami da cewa "wlhi idan har baki tashi a tsaye ba, narantse miki da Allah indai miji ne kinaji kina gani zai fi ƙarfinki, yo ke a zamanin yanzu waye yake zama haka?" Hajiya Zaliha tace "hmm ke a tunaninki ban je gurin malamai bane? Wlhi cemin sukayi wai wannan auren baza a fasa shi ba, idan na dage zan iya mutuwa" Hadiza tayi tsaki kafin tace "kedai Hajiya Zaliha wlhi kin bani kunya, wato da ban shigo gidanki ba, bazaki gayamin an miki kishiya ba, Hajiya Zaliha tayi tagumi, gami da cewa "hmm abunne ya isheni shiyasa babu wanda na gaiyyata, "ga shi nan ai tana neman hallakaki, wlhi idan baki tashi tsaye ba, wannan tsinanniyar yarinyar sai ta ƙwace miki Alhaji, Hadiza tayi maganar cike da masifa, Hajiya Zaliha tace "to yanzu meye abin yi?" Hadiza tace "abinyi karki damu na ɗauki nauyin komai da komai, kedai kawai ki amince dani" Hajiya Zaliha tace "ƙawata ai maganar amincewa ma ba sai kin tambayeni ba, saboda na daɗe da amincewa dake" nan dai suka fara tattauna ta ina zasu fara, Hadiza tace "tasha kuruminta ba sai ta biyota ba, insha Allah zata san inda zata yi akan Alhaji ya saki Saudart, suna tsaka da magana sai ga sallamar ƴarta auta wato Salma, tun daga corridor suke jiyo gunjin kuka, har ta ƙara so parlorn kuka take yi, cikin sarƙewar murya take cewa "Momy wato Dady ya ƙi ji sai da yayi aure nan?, Nan fa suka fitae koke-koke kai kace gidan mutuwa, Salma tace "wallahi momy nima ina cikin wata masifar, wai Imran na neman aure, har waya yakeyi da budurwarsa a gabansa, ke duniya maza basu da tabbas wallahi momy zan kashe aurena Gara in mutu ko in dawo gida da dai inga Imran ya ƙara aure wlhi, tai maganar tana sake fashewa da matsanancin kuka, Hadiza tace "ƴata ki kwantar da hankalinki akwai mafita da izinin Ubangiji indai maganar aure ne, kamar an fasa shi, yanzu dai ki gayamin rabasu kikeso ayi kokuma kar ya sake marmarin ƙara kula ƴa mace a duniya?" Salma tace "anty Hadiza ko a lahira ma bana son ya kula ko wacce mace" Anty Hadiza ta miƙe tsaye, tare da yiwa Hajiya Zaliha alkawarin raba auren Alhaji da Saudart, bayan tafiyar ta, Salma ta matso kusa da Hajiya Zaliha, ta sata a gaba tana rusa kuka, cikin jin haushin ƙara mata wata damuwar da tayi tace "Salma ki gode wa Allah ma bai yi auren ba, ni da dadynku yai auren fa, karki manta ƴar cikinsa ya aure, wacce bata wuce sa'arki ba" Hajiya Zaliha tasa kuka itama. Ko gida Anty Hadiza bata wuce ba, kai tsaye ta wuce gurin bokanta, bayan sun gaisa tace masa, akwai wani ana ce masa Alhaji Salisu Alherin Allah yayi sabon aure, sunan amaryar Saudart, tanason a raba auren har abada, sannan akwai wata ita kuma sunanta Salma mijinta yana neman auren ƴarta Hindu, tana son duk gurin malaman duniyar da zasuje kar suyi galaba akan hana auren, saboda Hindu tana son Imran sosai, boka ya ake ciki?" boka ya yi wasu surutai kana ya kwashe da dariya, kafin yace "akan maganar shi wannan Alhjin zanyi iya bakin ƙoƙarina gurin ganin an ruguza musu farinciki, sannan ita kuma Hindu ai wannan auren babu fashi, sai dai zata fuskanci ƙalu bale daga gurin Salma" anty Hadiza tace "duk wannan ba damuwata bane, indai ta shiga babu damuwa na shiryawa koma meye" daga nan ta ajiye masa 2 hundred.k kana ta bar gurin, boka ya kwashe da wata iriyar dariya mai sauti... Abuja A hankali tayi parking motarta a inda aka tanada na cikin company ɗin, kai tsaye office ɗin Ma'aruf ta wuce cike da yauƙi, nocking tayi ya bata izinin shiga, ta shige ranta fess, sallama tayi ya amsa kana ta ƙara sa ciki, yayi mata alama da hannunsa akan ta zauna, tunda ta shigo ya fara jin wani abu ga me da ita, shi kansa ya kasa fassarawa kansa shin me yake ji ne?" Bayan ta zauna tace "good morning my Honey" kasancewarsa miskili bata wani fahimci fara'arsa ko akasin hakan ba, "ya amsa mata da morning to o, tai murmishi kafin tace "wow Masha Allah honey kayi kyau sosai, dama dai daga gida sai mota, saboda bana son ƴan mata su gama kallemin kai" juyi yayi a saman kujerar kana ya lumshe idanunsa, wani sihirtaccen murmishi ya baiyana fuskarsa, kafin ya lashi pink lip ɗinsa na ƙasa, kana yace "da fatan dai kin tahomin da abinci" Yah Subhanallah yafa birgeta, sai ta ji ta tamkar a wata duniya take, ko hira Mai tsayi basu taɓa yi a tsakaninsu ba, yau shi ne har da tambayar abinci?" Ta yi murmishi kafin tace "honey idan kana da buƙata ko nan da ina ne wlhi zan je in dafa maka, an sorry honey I love you wlhi" tayi maganar hawaye sun fara zubowa a idanunta, sosai yake kallon ƙwayar idanunta saboda tabbas ya hango tsagwaron soyayyar da takeyi masa, sai dai birgesa takeyi babu ƙaunarta a cikin zuciyarsa, Murmishi yayi kafin yace Love You too, tayi ƴar dariya tana rufe fuska, kana ta tashi tana cewa "barin je inyi maka girki mai daɗi, yace "oky" Matsalarta dashi sam baya iya yin magana Mai tsayi ko hira, Haka dai ta wuce kai tsaye kasuwa tayi siyayyar kayan abinci, sboda tana son ta dafa masa jollof ɗin couscous da vegetables, daga kasuwa ta wuce gidan ƙawarta, bayan sun gaisa tace "kinga ba zama bane ya kawoni, sir Ma'aruf ne ya ce inyi masa girki shiyasa kika ganni yanzu, kai tsaye ta shige kitchen ta ɗora abinci, kasancewar bashi da wuyar dahiwa yasa nan da nan ta kammala girkin sai ƙamshi ke tashi, ƙawar Tata, ta bata sabuwa kula ta zuba a ciki, kana ta bata kunun aya wanda tayi mai daɗi, wanda yaji kwakwa da dabino da peakmilk, aka zuba a kyakkyawan jug, ta sanya su a wani basket mai kyau sosai. A tukunya ta barwa matar gidan kana ta fito tace mata sauri takeyi, daga nan ta dawo company, yayi mamakin ganinta a wannan lokacin, sboda yayi tunanin zata ɗau lokaci mai yawa kafin ta kammala girkin, ko da ta shigo faɗaɗa fara'arta tayi kafin tace "your food is ready" shima murmishin yayi kafin yace "godiya nake, ya kamata ki wuce office I think akwai aiyuka acan" uhm..uhm gaskiya bazan iya zuwa ba har sai na baka abincin nan a baki" suka haɗa ido, tare da sakarwa junansu murmishi, cikin nutsuwa ta buɗe foodflaks ɗin tare da ɗaukar plate da spoon ta saka, kana ta ajiye a gabansa, cikin salon so take aikin kana ta fara bashi a baki, a hankali ya buɗe bakinsa tare da lumshe idanunsa, lokacin da yake tauna abincin, yana jin wani irin daɗi yana ratsa shi, "gaskiya kin iya girki Masha Allah, wato duk mijin da ya aureki ya more, wlhi" Murmishin yaƙe tayi saboda wannan kalmar sam batayi mata daɗi ba, sai tace "ai kaine mijin" cikin suɓutar baki da tunanin me zai bata amsa, Murmishi yayi yana amsar abincin, ta ƙara ɗibo abincin zata bashi kenan abokinsa Muhammad ya turo ƙofar bakinsa ɗauke da sallama hangame baki...! Afuwan inasha Allah idan nakai page 50 da zarar mun fara 51 zaku samu more typing. Mom Islam ce, 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋           _Mom Islam_ Page 57-58 Bayan ta gyara bedroom ɗin nata, ta koma ɗakin Alhji Abdullahi, yana kwance kamar inda ta barshi ɗazu, ya miƙe samɓal sai ta ga ya ƙara yi mata tsayi sosai, a hankali ta isa gareshi tare da kai tafin hannunta gurin hancinsa, yanayin da jikinta ya bata, sam ta kasa gasgata hakan, ta sake kai hannu a karo na biyu, a tsorace tace "baya numfashi?" ta fashe da kuka, saboda bata yarda da abinda zuciyarta ke gaya mata ba, da sauri ta koma ɗakinta, kana ta ɗauki wayarta ta danna number anty Asabe, bata ma san anty Asabe ta kirawo ba, murya babu daɗin saurare tace "Salima ya akayi?" Cikin Muryar kuka Hajiya Salima tace "Anty Asabe dan Allah kizo, dan Allah" takai ƙarshen maganar tana sakin kuka mai sauti, Daga can ɓangaren anty Asabe sauri ta farayi, adu'ar da takeyi bai wuce ta ji ance nata Alhaji Abdullahi ya mutu ba, a fili tace "baya motsi meye amfaninsa" ta fito harabar gidan sboda dama ita kaɗai ce a gidan sai yaron ƙanwarta da ta rasu ta bari tun yana jariri ga shi yanzu ya zama saurayi a halin yanzu shekarunsa 27yrs a duniya, "Driver yi sauri kazo ka kaini gidan yayana, tai maganar cikin yanayi na nuna damuwa kai kace har a zuciya, bayan ta shiga mota driver ya tada mota suka fice, kasancewar mai gadi ya buɗe get tun kafin shigarta mota. Driver na gudu tana yi masa masifa akan ya ƙara gudu ita kam taga yana driving sai kace wani mace, daga ƙarshe ma cewa tayi ya fito a motar ya dawo backside ta yarda ita zatayi driving, abin ya matuƙar bashi mamaki matuƙa, saboda driving ɗin ma bata iya ba, shi yake koya mata, masifarta ta hanata koya, Ikon Allah ne ya kawosu gidan Alhaji, gida ya cika maƙil da mutane, saboda Hajiya Salima ta sanarwa da maƙota, sai koke-koke akeyi, tun da taga ƙofar gidan an cika, tai saurin fitowa daga mota ba tare da ta gama tsayawa ba, wata irin kururuwa takeyi marar daɗin ji, har ta isa ɗakin da alhajin yake, Hajiya Salima da maƙotansu da ƴan uwanta wanda suke kusa, mama dai har yanzu bata iso ba, sosai take ta gunjin kuka babu kauƙautawa, mutane sai bata haƙuri sukeyi, cikin Muryar kuka tace "Allah sarki Yaseen da Yusra, ko a wane hali suke ciki oho, Hajiya Salima kam idanunta sun kumbura sosai, tsabar kuka, da jimamin yaranta, ta rasa su, daga shi har ƴaƴansa, sosai takejin rayuwar duniyar ma ta fitar mata a kai, Bayan anyi masa wanka kana aka yi masa sutura, daga nan aka kaisa gidansa na gaskiya. Alhmdllh Alhaji Abdullahi ya samu yabo daga bakunan al'umma, babu mai faɗar wani mugun abu sai alkairansa, yayi tashen arziƙi wanda har yanzu ma yana kai, sai kuma yabar duniya, ya gina manya manyan masallatai da makarantun islamiyya duk kyauta, kana yana yawan kaiwa gidan marayu ziyara duk lokacin da yake free, hakan yasa ya samu babbar shaida anan duniya. Ana kaisa aka fara hada-hadar ɗora abinci, anty Asabe kam kai tsaye ɗakinsa ta wuce, ganin key a ƙofar ɗakin yasa ta kulle ƙofar ba tare da sanin kowa ba, a tunaninta Hajiya Salima ta iya zuwa ta kwashe dukiya ta barta a banza.. KEFFI yau ta kasance sunday, washe garin biki kenan, sam hankalinta ya gaza kwanciya, gani takeyi kamar Hajiya Zaliha zata iya dawowa, duk da alhajin yana gida, zaune take a saman gado, tana sanye da shadda fara sol anyi mata stone work ɗinkin Abuja Bubu, tayi ɗauri mai kyau wanda ya daɗa ƙawata kwalliyar tata, Masha Allah. Danne-danne takeyi a wayarta, bata tunanin kiran iyayenta, saboda sune suka yi sanadiyar rusa mata farinciki, tunda akayi bikin bata kirasu ba, sboda ta ajiye simcard ɗin ta a ƙasa, a hankali Alhajin ya murɗa handle na ƙofar kana yai sallama tare da ƙarasowa cikin shiga ta alfarma, yana sanye da shadda milk color sleek sai sheƙi takeyi, a hannu ya riƙo babbar rigar tasa, ta amsa sallamar tare da sunkuyar da kanta, "Habibty gaskiya kinyi kyau" yai maganar yana ƙarasowa inda take, bata ɗago kanta ba, bare ta nuna ta ji abinda ya faɗa, zamansa a kusa da ita ne yasa ta ɗago fararen idanuwanta tare da ɗora su a nata, yai amfani da hakan wajen rungumeta, cikin Muryar tarairaya yace "Habibty nasan kina jin yunwa, idan har drinks ɗin da suke gidannan basuyi miki ba, ki tashi muje restaurant muci abinci" Tabbas zaman kaɗaici ya dameta, duk da alhajin yana wuni a gida, amma bata wani sakewa suyi hira, ita har yanzu bataji tana sonsa ba, sai dai ta gano yana tsananin sonta sosai, tana son ta koyawa zuciyarta sonsa ya zatayi?" Amsar ta maƙale mata a ƙasan maƙoshinta, Rungumeta yayi sosai, kana ya ɗan sunƙuyo da fuskarsa gurin tata fuskar kafin yace "Habibty mai kikace game da fitar?" "Uhm to" Saudart ta amsa masa, saboda bata da zaɓi, Ta zame a jikinsa tare da buɗe drowa ta ɗauki mayafi, ta ɗauko sabon takalminta da Hand bag, da wayarta, wacce babu simcard a ciki, kana ta fito parlor, har yanzu yana mamakin Saudart, duk irin soyayyar da yake nuna mata har yanzu ta kasa fahimtarsa, mai yasa take yi masa haka?" murmishi kawai yayi, kana ya fita a bedroom ɗin nata, kai tsaye ya wuce bedroom ɗinsa, car key da ATM ya ɗauka, kana ya sanya takalmi cover shoe sannan ya fito parlor, tana zaune a ɗaya daga cikin kujerun da suka ƙawata parlorn, tayi nisa a tunani sosai, "Habibty tashi mu tafi.." jin bata ce komai ba, sannan bata motsa ba, yasa shi ɗan risinawa a gabanta bai kai ƙasa ba, yace "Habibty nace tashi mu tafi" Firgit ta miƙe saboda tayi zurfi cikin tunanin nata, drivernsu na ganin fitowarsu ya fara shirin shiga mota, alhajin ya dakatar dashi tare da cewa "kayi zamanka yanzu zamu dawo" Driver yayi musu Allah ya tsare, bayan an buɗe musu get securities ɗin suka buɗewa Alhji Murfin mota gurin zaman driver, already Alhji ya buɗe wa Saudart kusa dashi, kai tsaye yayiwa motar key suka bar anguwar, Driving yakeyi time to time yana kallon fuskar Saudart, cikin rashin sa'a go slow ya haɗu, wata ƙawar Salma ta hango Saudart dake zaune cikin motar Alhji, abin ya bawa ƙawar Salma mamaki, dan bata san yayi aure ba, sbda har hannunsa ya ɗora a saman Saudart, kana ya zuba mata idanu, da sauri ƙawar Salman ta danna number Salma, ringing ɗaya ta ɗaga, tare da cewa "Aminiya ya akayi ne?" "Ke na rantse da Allah idanuna sun ganemin wani abu, Salma Dad ɗinki tare da wata kyakkyawar budurwa har yana kissing ɗinta a mota gashi go slow ya haɗamu, nikam basu gama isata kallo ba" Salma ta miƙe a zabure, kana ta kalli mahaifiyarta, kafin tace "momy wlhi tallahi Dady ya gama damu, ashe ma yawo yakeyi da amaryar tasa, yanzu fa ƙawata ta kirani" Salma tayi maganar tana fashewa da kuka, tare da ɗora hannu a kai, Hajiya Zaliha tace "shikenan, wlhi shikenan, mun kaɗe, daga mu har ganyenmu, Hajiya Zaliha tace "barin kira Hadiza inji ya akayi da maganar zuwa gurin malamin da tace zatace " Salma ta dauki wayar Hajiya Zaliha ta kira lambar anty Hadiza, sai da tayi ringing sau uku ana uku Kafin ta ɗaga "Hajiya ina hanyar zuwa gidanki, yanzu" Hajiya Zaliha tace "Allah ya kawo ki ina jiranki akwai wata, bura ubar sabuwa" Hajiya Hadiza tace "shafamin ya akayi?" Sai kin zo ɗin kawai ina jiranki" Hajiya Zaliha tai maganar tana share ƙwalla. Suna cikin jajanta lamarin alhaji, anty Hadiza na shigowa parlor kai tsaye bedroom ɗin Hajiya Zaliha ta wuce, saboda basa parlor, tura ƙofar da zatayi ta samu sunata kuka dukkansu, da sauri ta ƙarisa tare da neman gurin zama, kafin tace "Hajiya kekuwa baki jira zuwan ba, kike sake tada hankalinki?" Cikin muryar kuka Salma tace "anty Hadiza Dady ne ya cucemu, wannan wane irin tozarci ne, da ƴar cikinsa fa yake yawo" anty Hadiza tayi salati tare da cewa "oh ni Hadiza naga abinda ya isheni" sai kuma tace "amma dai ku kwantar da hankalinku, saboda wlhi nasa ayiwa Alhaji aikin mantau, ta inda bazai sake tuno da waccar karuwar ba, a tarihin rayuwarsa, inaso dukkanku ku cire damuwar Alhaji domin kuwa wasan yazo ƙarshe... Salma na share hawaye tace "anty Hadiza nifa maganar mijina?" Anty Hadiza tayi murmishi tare da cewa "baki da matsala Salma, ke da kishiya har abada.. Salma tayi tafi cike da farin ciki, har tana zuwa ta rungume anty Hadiza. K.D Kwanci  tashi babu wuya a gurin ubangiji yau satin su Majeed da Najma ɗaya a gidansu Yaseen da Yusra kullum yana  fita aiki sai ta ɗora abinci cikin tukunya ta kaiwa dabbobin nan, suna mugun jin daɗi sosai, Ranar ta kasance Monday tushen aiki, dama duk ranar Monday baya dawowa da wuri, tana zaune a parlor taji mararta na murɗawa, a hankali ta zube ƙasa daga saman kujerar tare da runtse idanuwanta, da alamu tana jin zafi sosai, da ƙyar ta janyo wayarta ta danna number Yaseen yana ganin kiranta ya ajiye aikin da yake yi ya ɗaga tare da cewa "my life yakike" saukar numfarfashi da yaji ne ya tabbatar masa da babu lafiya, bai sallami mutanen dake gabansa ba, bare ya kalli wanda suka zauna a harabar Company ɗin, suna roƙonsa, kai tsaye mota ya shiga hankalinsa a tashe, driving yakeyi kamar zai tashi sama saboda tsananin firgici da yake ciki, Ikon Allah ne kawai ya kawo shi gida, lokacin ta galabaita sosai, tana durƙushe a gurin, Cikin hanzari ya ɗagata cak kana ya kaita mota, sannan ya dawo bedroom ɗinta ya ɗauki jakar kayan baby, kana ya shiga mota suka fice, ko takan baba mai gadi bebi ba, ya dinga sharara gudu a titi, har suka iso PLATEAU hospital, kai tsaye aka wuce da ita emergency room, manya manyan likitoci ne suka taru a kanta suna bata taimakon gaggawa, yayinda Majeed yake waje yana ta zirga zirga, ko wacce likita ko doctor suka fito basa sauraren sa, hakan ba ƙaramin ɗaga masa hankali yayi ba, cikin sauri ya lalubi number mahaifiyar Yusra ya kirata, tana ɗagawa ya sanar mata da Yusra na hospital, mahaifiyar Tata, tace "gata nan zuwa" Tun ƙarfe 12:pm suke hospital ɗin har ƙarfe 2pm bai ji wani cikakken bayani ba, sai yanzu da wani doctor ya gaiyyacesa zuwa office ɗinsa, bayan sun gaisa yace "matarka aihuwa zatayi, gashi har yanzu shiru, sannan bata da wani power a jikinta ina tunanin zamuyi mata Cs idan har ka amince, ga takarda kasa mana hannu, damuwarsa bai wuce ya ga Yursa cikin ƙoshin lafiya ba, da sauri yasa hannun tare da ɗaga hannu yana roƙon Ubangiji, kai tsaye aka wuce da ita ɗakin tiyata domin kuwa bata cikin haiyyacinta, bata san waye a kanta ba, Bayan an shigar da ita, doctor's suka fara hada hadar fara aiki, lokaci ɗaya ta wani daƙarƙare ta zafga ƙara tare da riƙe ƙarfen gadon da take kwance, sai ga baby ya faɗo, likitocin sai hamdala sukeyi, sakamakon tausaya mata da sukeyi, Da sauri wata likita ta fita ta samu Yaseen dake zaune a saman benci fuskarta ɗauke da murmishi tace "sir matarka ta aihu" kafin ya buɗe baki tayi gaba, Yaseen kam wani daɗi ne ya lulluɓeshi sakamakon wannan albishir da wannan likita tayi masa, da sauri ya wuce masallaci ya kabbara sallah tare da sake miƙa godiyar sa ga Allah, lokacin da ya fito daga masallaci, Momcy tana parking mota ita da kakar Yusra ta gurin mahaifiyarta, ko gaisawa basuyi ba, suka hau tambayar jikin Yusra, yayi musu albishir da aihuwarta, suma su Momcy ba'a barsu sun shiga ba, sai bayan wasu lokuta kana aka basu damar shiga, dukkansu suka shiga ko wannensu fuskarsa ɗauke da fara'a, yaro ne Kyakkyawa mai kama da mahaifinsa, ga shi jajir dashi, an nannaɗeshi cikin kayan sanyi masu kyau sosai, Yusra kam tana da barci saboda drip ne ma a hannunta shiyasa akace kar suyi hayaniya, kaka sai cewa take yi "Masha Allah yaro kamar babansa" shikuma Yaseen yanata sunkuyar da kai, ko da Momcy ta karɓi yaron ta ji wani soyayyar jaririn na shigar mata rai, a hankali ta dinga tofa masa adu'oi daga ƙarshe ta miƙawa Yaseen, shima yayi masa adu'a, tabbas bai gaji da ganin ɗansa ba, haka dai ya danne ya sake miƙawa kaka, tare da kallon Momcy yace "Momcy ki faɗa min abubuwan da ake da buƙata, Momcy ta lissafa masa ya fice, suna yi masa Allah ya kiyaye hanya, Acan gidan Yaseen dabbobi sunyi kuka har sunji ba daɗi, tsabar yunwa Barin ma su Majeed da Najma abin sai wanda ya ganni, saboda durƙushewa sukayi gefe guda sunata kuka, Shinan Yaseen yama mance da maganar abincin dabbobi, har aka kwana aka wuni, da yamma da ya tuna ya sa aka kai musu, yana daga Hospital ɗin yayi waya da wani tsoho akan ya zo ya kwashe dabbobin yakai su kasuwa, abar masa saniya guda biyu su za'a yanka, hakan ko akayi, su Najma sunyi kuka sosai, koba komai sun fara sabawa da nan ɗin, yanzu basu san inda za'a kaisu ba, gaskiya suna cikin wani hali, Kai tsaye aka wuce dasu kasuwar dabbobi, inda tsohon ya zauna yake karantar yanayin ko wacce dabba, tsohon ya kasance mafarauci ne, sannan yana da sani akan wasu abubuwan, tunda idanunsa a buɗe suke, ji a jikinsa da yayi ne ma, yasa yake ta kallon dabbobin, ko da idanunsa suka sauka akan su Najma da sauri ya sake ƙura musu idanu, ya girgiza kai tare da ɗauko wani kaskon wuta kana ya zuba wani abu hayaƙi ya tashi, sannan ya matso kusa da su ya ɗibi wani ruwa mai warin gaskiya ya watsa musu, kafin ya sake ɗibo wani garin magani ya kaɗa a ruwa ya basu suka sha, sannan yayi kabbara Allahu Akbar... Allahu Akbar.... Allahu Akbar, sau uku, abin mamaki sai ga Majeed da Najma sun baiyyana cikin kayan da suka fito dashi daga gidan tun watanni takwas da suka wuce, dukkansu a durƙushe suke, sai da tsohon ya sake ɗibo wani man shafawa ya shafa musu a guwaiwar hannu da ƙafa da wuyansu, kafin ya umarcesu da su miƙe tsaye, suka miƙe tare da fara rarraba idanu, dukkansu sai suka fashe da kuka a tare, tsohon ya ɗaga musu hannu kana yace "godewa Allah ya kamata kuyi, bai kamata kuna kuka ba, ya ƙwalawa yarinyarsa kira wacce bata wuce sa'ar Najma ba, sannan ya ƙwalawa yaronsa wanda Majeed ma zai girme masa kamar da shekara ɗaya, yace "a basu ruwan wanka da abinci, shi namjin ya bawa Majeed kaya, ita kuma macen ta bawa Najma kaya, suka amsa da cewa "to"... KANO ana gobe birthday party ɗin Laurat, Aysha ta gayawa anty Tasneem da Umaimah, bata hanata zuwa ba, hasali ma har tambayarta tayi mai zata kai wa ƙawar Tata a matsayin gift, Aysha tayi shiruuu, sboda bata sam mai ya dace ta kai mata ba, anty Tasneem tace "gobe idan Allah ya kaimu sai in baki abinda zaki kai mata, "Umaimah zakije koh?" Aysha ta tambayeta, "Eh man zuwa sosai ma" Umaimah ta bata amsa, wunin ranar dai sunata tsara irin shigar da zasuyi, kai kace sune masu yin birthday ɗin,  yau kusan kwananta uku bata kunna wayarta ba, Umaimah tayi tayi akan ta kunna saboda kar Zayden yayita tunanin ko bata cikin ƙoshin lafiya amma fur taƙi sai yau, kamar jira yake yi, ta kunna wayar, aiko sai ga kiransa tare da text message, kiran nasa ta ɗaga, cikin sanyaya murya, "amincin Allah ya tabbata ga masoyiyata abin alfaharina, ina fatan dai kwana biyu lafiya?" "Uhm lafiya lau" "Mai yasa wayarki bata shiga," "Haka kawai" "Kinason ki azabtar dani ne?" Ta fashe masa da kuka mai sauti, da sauri ya kalli wayar dake hannunsa kana ya kara a kunnensa kafin yace "Please beauty ki gayamin meke faruwa?" "Zayd ina sonka, bani da damar da zan iya furta maka hakan" Ta katse kiran tare da ajiye wayar, dariya ta farayi ga hawaye na, zuba, ta share hawayen, tare da kallon gefenta taga babu kowa, hamdala tayi kana ta tashi ta shiga toilet ta ɗauro alwalah kana ta shimfiɗa sallahya sannan ta kabbara sallahar magriba, tana cikin yin Sallah sai ga Umaimah ta shigo, da alamu daga can parlorn ta ɗauro alwalah, itama ta kabbara sallah, bayan sun idar sunyi addu'oinsu, Aysha ta kalli Umaimah, kafin tace "kinsan me?" Umaimah ta girgiza kai, Aysha tace "wlhi har tunanin ranar da zan koma gidan Hajiya nakeyi, babbar damuwata yah Ma'aruf, bashi da mutunci ko kaɗan" Umaimah tace "uhm na taɓa ganinsa sau ɗaya a wata hira da akayi dashi a TV, wlhi bana fata in ganshi a zahiri, saboda Guy ɗin akwai kwarjini sosai, ga shi Ubangiji ya haɗa masa komai duka, ance ɗan adam tara yake bai cika goma ba, nikam a ganina wannan bawan Allahan ya cika ɗari ma, ga kyau ga kuɗi ga izza wow amma fa tsoronsa nakeji" Aysha tayi murmishi kana tace "wato Umaimah, babbar damuwata komawa gidan, kamar dai yadda na gaya miki, dalilin da yasa na fara tunani, hamm uncle Junaid ya kusa dawowa kinga anty Tasneem bazata barmu a gidannan ba, i swear" Umaimah tace "faɗi ki ƙara barinma kekam da zaki sace zuciyar duk wani lafiyayyen namijin da yayi tozali dake" Aysha ta zaro idanu tare da cewa "wlhi sharri dai babu kyau" Umaimah tace "wlhi gaskiya nake gaya miki lokaci ɗaya kika wani cika, ƙila baki ga hips ɗinki bane ko?  One Month nazo gidannan lokacin ma ƙirgen dangin da kika farayi ƙanana ne, ga shi yanzu har ana saka bra, uwa uba 3 weeks ago kika fara period, hmm ai dole ki fara tunanin makomarki, amma ya maganar makarantar ki fa?" Uhm Umaimah, alhmdulilah insha Allah na koma Abuja zan ci gaba, amma nafison mai haɗe da islamiyya" Umaimah tace "ai karatun addini yanada kyau sosai, haɗuwarmu zatayi wuya sai dai a waya, wlhi zan gargaɗeki karki kuskura ki nunawa wani wayarnan, idan ba haka ba, wlh sai kin shiga tashin hankali" Aysha tace "hauka nakeyi Umaimah?" Aysha ta faɗa tana riƙe baki, Sunsha hira a daren, bayan an kira sallahar isha'i sunyi suka kwanta, wayar Umaimah ta fara ringing, tana dubawa taga Zayden, ta zaro idanu, tare da cewa "Aysha ga masoyinki ya kira, tayi kamar bazata karɓi wayar ba, ta miƙa hannu ta karba tare da karawa a kunnenta, "aslmu alaikum" Tayi sallama, "Wlkslm" Zayden ya amsa, daga jin muryarsa ma ta nuna yanayin damuwar da yake ciki, Kafin yace "beauty dan Allah ina son in roƙeƙi wata alfarma, sannan inason ki gayamin iya gaskiyarki saboda bana son ƙarya.." In Cold voice tace "ina jinka" "Aysha kina sona, tsakaninki da Allah?" "Tayi shiru, kafin tace "eh sosai ma" Yace "good" Ya sake cewa "Aysha bana son idan muna magana ki dinga katse min kira" Cikin sanyin murya tace "bazan sake ba" A karo na uku ya sake cewa "yanzu meye yake damunki?" Ta marairaice murya tare da cewa "babu komai" "Yaushe zamu haɗu" Kai tsaye tace masa "ko gobe" Yace "a ina zamu haɗu?" Ta jujjuya idanu kafin tace "zan kiraka, ƙawata ce zatayi birthday" Yace "okay, Allah ya kaimu" Tunda ya katse wayar Aysha, tunani iri-iri ya dameshi, sakamakon sonta da yake neman zautar dashi, duk inda ya zauna sai ya yi maganarta har cikin danginsa da abokansa, shi kasansa ya kasa misalta son da yake yi mata, wanda bai taɓa yiwa wata mace a faɗin duniya ba" Itama a nata ɓangaren haka ne, soyayyar Zayd ta fara nisa a zuciyarta. Har Umaimah tayi barci tana rungume da wayarta... Washe gari Tun bayan da sukayi sallahar asbha suka fara aikace-aikace, daga nan sukayi wanka, already dama babu school sboda malamar su anyi wa wata Malama cs headmastern su shima yana Hospital, A gurguje sukayi breakfast sukuma masu aikin sukayi moping, Ƙarfe 9:am abinci ya kammalu aka jere a dinning, sai da suka shirya tsaf, cikin Abaya baƙaƙe, sunyi matuƙar kyau, saboda abayar ta amsa sunanta, duba da ƙyaleƙyalen dake jikinta, duk wanda ya kallesu tabbas sai ya sake kallo, saboda har wani walwali takeyi sukayi rolling veil ɗin a kansu, ba wani abinci mai yawa sukaci ba, tsabar ɗoki da murna, anty Tasneem ta kawowa Aysha wata haɗaɗɗiyar sarƙa mai zobe, da turare mai tsada harda su ribom masu kyau, Masha Allah sunyi kyau sosai, Aysha tayi godiya tare da cewa "anty bakice munyi kyau ba" Anty Tasneem tace "wlhi kunyi kyau sosai, sukayi hoto, Tare da yi mata sallama, kasancewar ko wacce ta fito da hand bag ɗinta, anty Tasneem ta miƙawa Umaimah 10k tace ko zasuyi siyi wani abun, sukayi mata godiya kana suka wuce. Kai tsaye parking space suka nufa, sukayi wa driver kwatancen anguwar da zai kaisu, suka shiga backside yayiwa motar key bayan an buɗe masa get. Cikin ikon Allah suka iso anguwarsu Laurat har ƙofar gida ya kaisu, suka gaya masa time ɗin da zai dawo ya ɗauke su, ya wuce. Nocking sukayi a get na gidan, mai gadi ya leƙo tare da cewa "sannunku daga ina?" Umaimah tace "nan ne gidansu Laurat?" Da sauri mai gadi ya gyaɗa kai gami da cewa "eh nan ne, amma daga ina kuke, kuyi hakuri wannan tambayar da nakeyi muku tana ɗaya daga cikin sharuɗan shiga wannan gidan" Aysha tace "babu komai, ta buɗe hand bag ɗinta kana ta ciro wata ƴar takarda sannan ta miƙa wa Umaimah, tace ta kira mata lambar, ringing ɗaya Laurat ta ɗaga tare da cewa waye?" Aysha tace "gamu a ƙofar gidanku" Cike da murna Laurat ta katse kiran tare da fitowa harabar gidan tana yiwa mai gadi magana akan ya buɗe musu get, bayan ya buɗe musu suka shigo, wow, hmm masu karatu gidan fa Masha Allah komai yayi, hatta motoci biyar ɗin dake jere a gurin ajiyar motoci duk na yayi ne masu tsadar gaske, Laurat tana sanye da gown irin ƴar kanti, kanta yasha gyara sai sheƙi yake yi Masha Allah, daga nan tayi musu iso zuwa cikin gidan, babu kowa a gidan, saboda an ɗaga birthday ɗin, sakamakon Dad ɗin ta yace ta bari sai next week, Aysha kuma bata sani ba shiyasa suka zo, kai tsaye ɗakinta ta kaisu, ɗakine babba kai kace ɗakin wata macen, Masha Allah ɗakin yayi kyau, bayan sun shiga suka zauna a wasu ƙawatattun kujeru, Laurat ta fita zuwa kitchen, ta kawo musu sakwara da miyar egusi, da kunun gyaɗa mai ɗumi wanda ya ji coconut da milk, Bayan ta ajiye musu a saman table ta koma ta zauna, kafin suka fara gaisawa, nan take gaya musu ai an ɗaga birthday ɗin, Aysha ta ciro kayan da Anty Tasneem ta bata ta miƙa mata, sosai Laurat tayi farinciki da wannan tsaraba, saboda a halin yanzu sun shaƙu da Aysha sosai, Basu wani ci abincin sosai ba, Laurat ta ƙurawa Aysha idanu, A'isha dai da ta gaji da kallon da Laurat keyi mata tace "ke ya dai lafiya?" Laurat ta sauya mood zuwa na damuwa, kafin tace "Ƙawar Aysha Please sunanki fa?" Umaimah tayi murmishi kafin tace "sunana Umaimah, ni ƴar uwarta ce" Laurat tace "alhmdulilah" "Dan Allah Umaimah ki taimakeni akan manufata Please ku fahimceni dan Allah" Sosai ta jefasu cikin alhini duk da basu ji me take son cewa ba, Laurat ta sakko ƙasa tare da durƙusa guwaiwoyinta ƙasa, ta haɗe hannayenta kafin tace "dan Allah Aysha kiyimin wata alfarma dan Allah" Aysha tace "Laurat wace irin alfarma ce hakan, da har kika durƙusa min?" Laurat ta shiga gallery na wayarta ta nuno wani kyakkyawan hoto, wanda wani matashi ne a jikin hoton, shi ɗin ba fari bane, baƙi ne, sannan baƙinsa ba mai muni bane, yanada gashin baki mai kyau, sannan ya gyare sumar kansa, ta nunawa Umaimah, kafin tace kinsan wannan?" Umaimah ta gyaɗa kai, tare da cewa "wannan ai yayi ambassador a ƙasar waje, kuma har yanzu ana damawa dashi dan na gaban goshi ne, ga kuɗi kamar zai kasheshi" dukkansu basu san me take nufi ba, tace "kuyimin alƙawarin duk abinda nace zaku amince" a tunaninsu wata maganar ko neman shawara takeyi, cikin haɗin baki suka amsa da cewa "zamu amince" "Laurat tace "Aysha dan Allah ki auri Dad ɗina, shine a jikin hotonnan, ni kaɗai nake zaune a gidannan sai masu aiki, sannan shi bai cika zama a Nigeria ba, sannan yana dawowa Nigeria baya cin abincin waje ko na masu aiki nice nakeyi masa, tun bayan rasuwar mahaifiyata, tana aihuwata ta rasu, wlhi tallahi Aysha baki da matsala da Dad, ƴan uwansa sunyi masa maganar aure har sun gaji dan Allah ki taimakeni" Laurat ta ƙarshe maganar tana, sake cewa "karki manta keda Umaimah kunyi min alƙawari, sannan Ubangiji yana girmama alƙawari" Kuka take yi sosai, yayinda Aysha ta daskare a gurin, Umaimah kam ta kasa koda motsa bakinta ne, tsabar firgici, saboda basuyi tunani ko tsammanin jin waɗannan zafafan kalaman daga bakin Laurat ba, ta sake fashewa da kuka tana cewa "Please nasan zaki iya kinada hankali nutsuwa tausayi da duk wani hali na gari da namiji ya kamata ya samu gurin mace, Please say something...! Tofa, 2days nayi talauci, rashin data yasa banyi muku posting ba, kuyi hakuri dan Allah. Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋           _Mom Islam_ Page 59-60 Bayan ta gyara bedroom ɗin nata, ta koma ɗakin Alhji Abdullahi, yana kwance kamar inda ta barshi ɗazu, ya miƙe samɓal sai ta ga ya ƙara yi mata tsayi sosai, a hankali ta isa gareshi tare da kai tafin hannunta gurin hancinsa, yanayin da jikinta ya bata, sam ta kasa gasgata hakan, ta sake kai hannu a karo na biyu, a tsorace tace "baya numfashi?" ta fashe da kuka, saboda bata yarda da abinda zuciyarta ke gaya mata ba, da sauri ta koma ɗakinta, kana ta ɗauki wayarta ta danna number anty Asabe, bata ma san anty Asabe ta kirawo ba, murya babu daɗin saurare tace "Salima ya akayi?" Cikin Muryar kuka Hajiya Salima tace "Anty Asabe dan Allah kizo, dan Allah" takai ƙarshen maganar tana sakin kuka mai sauti, Daga can ɓangaren anty Asabe sauri ta farayi, adu'ar da takeyi bai wuce ta ji ance nata Alhaji Abdullahi ya mutu ba, a fili tace "baya motsi meye amfaninsa" ta fito harabar gidan sboda dama ita kaɗai ce a gidan sai yaron ƙanwarta da ta rasu ta bari tun yana jariri ga shi yanzu ya zama saurayi a halin yanzu shekarunsa 27yrs a duniya, "Driver yi sauri kazo ka kaini gidan yayana, tai maganar cikin yanayi na nuna damuwa kai kace har a zuciya, bayan ta shiga mota driver ya tada mota suka fice, kasancewar mai gadi ya buɗe get tun kafin shigarta mota. Driver na gudu tana yi masa masifa akan ya ƙara gudu ita kam taga yana driving sai kace wani mace, daga ƙarshe ma cewa tayi ya fito a motar ya dawo backside ta yarda ita zatayi driving, abin ya matuƙar bashi mamaki matuƙa, saboda driving ɗin ma bata iya ba, shi yake koya mata, masifarta ta hanata koya, Ikon Allah ne ya kawosu gidan Alhaji, gida ya cika maƙil da mutane, saboda Hajiya Salima ta sanarwa da maƙota, sai koke-koke akeyi, tun da taga ƙofar gidan an cika, tai saurin fitowa daga mota ba tare da ta gama tsayawa ba, wata irin kururuwa takeyi marar daɗin ji, har ta isa ɗakin da alhajin yake, Hajiya Salima da maƙotansu da ƴan uwanta wanda suke kusa, mama dai har yanzu bata iso ba, sosai take ta gunjin kuka babu kauƙautawa, mutane sai bata haƙuri sukeyi, cikin Muryar kuka tace "Allah sarki Yaseen da Yusra, ko a wane hali suke ciki oho, Hajiya Salima kam idanunta sun kumbura sosai, tsabar kuka, da jimamin yaranta, ta rasa su, daga shi har ƴaƴansa, sosai takejin rayuwar duniyar ma ta fitar mata a kai, Bayan anyi masa wanka kana aka yi masa sutura, daga nan aka kaisa gidansa na gaskiya. Alhmdllh Alhaji Abdullahi ya samu yabo daga bakunan al'umma, babu mai faɗar wani mugun abu sai alkairansa, yayi tashen arziƙi wanda har yanzu ma yana kai, sai kuma yabar duniya, ya gina manya manyan masallatai da makarantun islamiyya duk kyauta, kana yana yawan kaiwa gidan marayu ziyara duk lokacin da yake free, hakan yasa ya samu babbar shaida anan duniya. Ana kaisa aka fara hada-hadar ɗora abinci, anty Asabe kam kai tsaye ɗakinsa ta wuce, ganin key a ƙofar ɗakin yasa ta kulle ƙofar ba tare da sanin kowa ba, a tunaninta Hajiya Salima ta iya zuwa ta kwashe dukiya ta barta a banza.. KEFFI yau ta kasance sunday, washe garin biki kenan, sam hankalinta ya gaza kwanciya, gani takeyi kamar Hajiya Zaliha zata iya dawowa, duk da alhajin yana gida, zaune take a saman gado, tana sanye da shadda fara sol anyi mata stone work ɗinkin Abuja Bubu, tayi ɗauri mai kyau wanda ya daɗa ƙawata kwalliyar tata, Masha Allah. Danne-danne takeyi a wayarta, bata tunanin kiran iyayenta, saboda sune suka yi sanadiyar rusa mata farinciki, tunda akayi bikin bata kirasu ba, sboda ta ajiye simcard ɗin ta a ƙasa, a hankali Alhajin ya murɗa handle na ƙofar kana yai sallama tare da ƙarasowa cikin shiga ta alfarma, yana sanye da shadda milk color sleek sai sheƙi takeyi, a hannu ya riƙo babbar rigar tasa, ta amsa sallamar tare da sunkuyar da kanta, "Habibty gaskiya kinyi kyau" yai maganar yana ƙarasowa inda take, bata ɗago kanta ba, bare ta nuna ta ji abinda ya faɗa, zamansa a kusa da ita ne yasa ta ɗago fararen idanuwanta tare da ɗora su a nata, yai amfani da hakan wajen rungumeta, cikin Muryar tarairaya yace "Habibty nasan kina jin yunwa, idan har drinks ɗin da suke gidannan basuyi miki ba, ki tashi muje restaurant muci abinci" Tabbas zaman kaɗaici ya dameta, duk da alhajin yana wuni a gida, amma bata wani sakewa suyi hira, ita har yanzu bataji tana sonsa ba, sai dai ta gano yana tsananin sonta sosai, tana son ta koyawa zuciyarta sonsa ya zatayi?" Amsar ta maƙale mata a ƙasan maƙoshinta, Rungumeta yayi sosai, kana ya ɗan sunƙuyo da fuskarsa gurin tata fuskar kafin yace "Habibty mai kikace game da fitar?" "Uhm to" Saudart ta amsa masa, saboda bata da zaɓi, Ta zame a jikinsa tare da buɗe drowa ta ɗauki mayafi, ta ɗauko sabon takalminta da Hand bag, da wayarta, wacce babu simcard a ciki, kana ta fito parlor, har yanzu yana mamakin Saudart, duk irin soyayyar da yake nuna mata har yanzu ta kasa fahimtarsa, mai yasa take yi masa haka?" murmishi kawai yayi, kana ya fita a bedroom ɗin nata, kai tsaye ya wuce bedroom ɗinsa, car key da ATM ya ɗauka, kana ya sanya takalmi cover shoe sannan ya fito parlor, tana zaune a ɗaya daga cikin kujerun da suka ƙawata parlorn, tayi nisa a tunani sosai, "Habibty tashi mu tafi.." jin bata ce komai ba, sannan bata motsa ba, yasa shi ɗan risinawa a gabanta bai kai ƙasa ba, yace "Habibty nace tashi mu tafi" Firgit ta miƙe saboda tayi zurfi cikin tunanin nata, drivernsu na ganin fitowarsu ya fara shirin shiga mota, alhajin ya dakatar dashi tare da cewa "kayi zamanka yanzu zamu dawo" Driver yayi musu Allah ya tsare, bayan an buɗe musu get securities ɗin suka buɗewa Alhji Murfin mota gurin zaman driver, already Alhji ya buɗe wa Saudart kusa dashi, kai tsaye yayiwa motar key suka bar anguwar, Driving yakeyi time to time yana kallon fuskar Saudart, cikin rashin sa'a go slow ya haɗu, wata ƙawar Salma ta hango Saudart dake zaune cikin motar Alhji, abin ya bawa ƙawar Salma mamaki, dan bata san yayi aure ba, sbda har hannunsa ya ɗora a saman Saudart, kana ya zuba mata idanu, da sauri ƙawar Salman ta danna number Salma, ringing ɗaya ta ɗaga, tare da cewa "Aminiya ya akayi ne?" "Ke na rantse da Allah idanuna sun ganemin wani abu, Salma Dad ɗinki tare da wata kyakkyawar budurwa har yana kissing ɗinta a mota gashi go slow ya haɗamu, nikam basu gama isata kallo ba" Salma ta miƙe a zabure, kana ta kalli mahaifiyarta, kafin tace "momy wlhi tallahi Dady ya gama damu, ashe ma yawo yakeyi da amaryar tasa, yanzu fa ƙawata ta kirani" Salma tayi maganar tana fashewa da kuka, tare da ɗora hannu a kai, Hajiya Zaliha tace "shikenan, wlhi shikenan, mun kaɗe, daga mu har ganyenmu, Hajiya Zaliha tace "barin kira Hadiza inji ya akayi da maganar zuwa gurin malamin da tace zatace " Salma ta dauki wayar Hajiya Zaliha ta kira lambar anty Hadiza, sai da tayi ringing sau uku ana uku Kafin ta ɗaga "Hajiya ina hanyar zuwa gidanki, yanzu" Hajiya Zaliha tace "Allah ya kawo ki ina jiranki akwai wata, bura ubar sabuwa" Hajiya Hadiza tace "shafamin ya akayi?" Sai kin zo ɗin kawai ina jiranki" Hajiya Zaliha tai maganar tana share ƙwalla. Suna cikin jajanta lamarin alhaji, anty Hadiza na shigowa parlor kai tsaye bedroom ɗin Hajiya Zaliha ta wuce, saboda basa parlor, tura ƙofar da zatayi ta samu sunata kuka dukkansu, da sauri ta ƙarisa tare da neman gurin zama, kafin tace "Hajiya kekuwa baki jira zuwan ba, kike sake tada hankalinki?" Cikin muryar kuka Salma tace "anty Hadiza Dady ne ya cucemu, wannan wane irin tozarci ne, da ƴar cikinsa fa yake yawo" anty Hadiza tayi salati tare da cewa "oh ni Hadiza naga abinda ya isheni" sai kuma tace "amma dai ku kwantar da hankalinku, saboda wlhi nasa ayiwa Alhaji aikin mantau, ta inda bazai sake tuno da waccar karuwar ba, a tarihin rayuwarsa, inaso dukkanku ku cire damuwar Alhaji domin kuwa wasan yazo ƙarshe... Salma na share hawaye tace "anty Hadiza nifa maganar mijina?" Anty Hadiza tayi murmishi tare da cewa "baki da matsala Salma, ke da kishiya har abada.. Salma tayi tafi cike da farin ciki, har tana zuwa ta rungume anty Hadiza. K.D Kwanci  tashi babu wuya a gurin ubangiji yau satin su Majeed da Najma ɗaya a gidansu Yaseen da Yusra kullum yana  fita aiki sai ta ɗora abinci cikin tukunya ta kaiwa dabbobin nan, suna mugun jin daɗi sosai, Ranar ta kasance Monday tushen aiki, dama duk ranar Monday baya dawowa da wuri, tana zaune a parlor taji mararta na murɗawa, a hankali ta zube ƙasa daga saman kujerar tare da runtse idanuwanta, da alamu tana jin zafi sosai, da ƙyar ta janyo wayarta ta danna number Yaseen yana ganin kiranta ya ajiye aikin da yake yi ya ɗaga tare da cewa "my life yakike" saukar numfarfashi da yaji ne ya tabbatar masa da babu lafiya, bai sallami mutanen dake gabansa ba, bare ya kalli wanda suka zauna a harabar Company ɗin, suna roƙonsa, kai tsaye mota ya shiga hankalinsa a tashe, driving yakeyi kamar zai tashi sama saboda tsananin firgici da yake ciki, Ikon Allah ne kawai ya kawo shi gida, lokacin ta galabaita sosai, tana durƙushe a gurin, Cikin hanzari ya ɗagata cak kana ya kaita mota, sannan ya dawo bedroom ɗinta ya ɗauki jakar kayan baby, kana ya shiga mota suka fice, ko takan baba mai gadi bebi ba, ya dinga sharara gudu a titi, har suka iso PLATEAU hospital, kai tsaye aka wuce da ita emergency room, manya manyan likitoci ne suka taru a kanta suna bata taimakon gaggawa, yayinda Majeed yake waje yana ta zirga zirga, ko wacce likita ko doctor suka fito basa sauraren sa, hakan ba ƙaramin ɗaga masa hankali yayi ba, cikin sauri ya lalubi number mahaifiyar Yusra ya kirata, tana ɗagawa ya sanar mata da Yusra na hospital, mahaifiyar Tata, tace "gata nan zuwa" Tun ƙarfe 12:pm suke hospital ɗin har ƙarfe 2pm bai ji wani cikakken bayani ba, sai yanzu da wani doctor ya gaiyyacesa zuwa office ɗinsa, bayan sun gaisa yace "matarka aihuwa zatayi, gashi har yanzu shiru, sannan bata da wani power a jikinta ina tunanin zamuyi mata Cs idan har ka amince, ga takarda kasa mana hannu, damuwarsa bai wuce ya ga Yursa cikin ƙoshin lafiya ba, da sauri yasa hannun tare da ɗaga hannu yana roƙon Ubangiji, kai tsaye aka wuce da ita ɗakin tiyata domin kuwa bata cikin haiyyacinta, bata san waye a kanta ba, Bayan an shigar da ita, doctor's suka fara hada hadar fara aiki, lokaci ɗaya ta wani daƙarƙare ta zafga ƙara tare da riƙe ƙarfen gadon da take kwance, sai ga baby ya faɗo, likitocin sai hamdala sukeyi, sakamakon tausaya mata da sukeyi, Da sauri wata likita ta fita ta samu Yaseen dake zaune a saman benci fuskarta ɗauke da murmishi tace "sir matarka ta aihu" kafin ya buɗe baki tayi gaba, Yaseen kam wani daɗi ne ya lulluɓeshi sakamakon wannan albishir da wannan likita tayi masa, da sauri ya wuce masallaci ya kabbara sallah tare da sake miƙa godiyar sa ga Allah, lokacin da ya fito daga masallaci, Momcy tana parking mota ita da kakar Yusra ta gurin mahaifiyarta, ko gaisawa basuyi ba, suka hau tambayar jikin Yusra, yayi musu albishir da aihuwarta, suma su Momcy ba'a barsu sun shiga ba, sai bayan wasu lokuta kana aka basu damar shiga, dukkansu suka shiga ko wannensu fuskarsa ɗauke da fara'a, yaro ne Kyakkyawa mai kama da mahaifinsa, ga shi jajir dashi, an nannaɗeshi cikin kayan sanyi masu kyau sosai, Yusra kam tana da barci saboda drip ne ma a hannunta shiyasa akace kar suyi hayaniya, kaka sai cewa take yi "Masha Allah yaro kamar babansa" shikuma Yaseen yanata sunkuyar da kai, ko da Momcy ta karɓi yaron ta ji wani soyayyar jaririn na shigar mata rai, a hankali ta dinga tofa masa adu'oi daga ƙarshe ta miƙawa Yaseen, shima yayi masa adu'a, tabbas bai gaji da ganin ɗansa ba, haka dai ya danne ya sake miƙawa kaka, tare da kallon Momcy yace "Momcy ki faɗa min abubuwan da ake da buƙata, Momcy ta lissafa masa ya fice, suna yi masa Allah ya kiyaye hanya, Acan gidan Yaseen dabbobi sunyi kuka har sunji ba daɗi, tsabar yunwa Barin ma su Majeed da Najma abin sai wanda ya ganni, saboda durƙushewa sukayi gefe guda sunata kuka, Shinan Yaseen yama mance da maganar abincin dabbobi, har aka kwana aka wuni, da yamma da ya tuna ya sa aka kai musu, yana daga Hospital ɗin yayi waya da wani tsoho akan ya zo ya kwashe dabbobin yakai su kasuwa, abar masa saniya guda biyu su za'a yanka, hakan ko akayi, su Najma sunyi kuka sosai, koba komai sun fara sabawa da nan ɗin, yanzu basu san inda za'a kaisu ba, gaskiya suna cikin wani hali, Kai tsaye aka wuce dasu kasuwar dabbobi, inda tsohon ya zauna yake karantar yanayin ko wacce dabba, tsohon ya kasance mafarauci ne, sannan yana da sani akan wasu abubuwan, tunda idanunsa a buɗe suke, ji a jikinsa da yayi ne ma, yasa yake ta kallon dabbobin, ko da idanunsa suka sauka akan su Najma da sauri ya sake ƙura musu idanu, ya girgiza kai tare da ɗauko wani kaskon wuta kana ya zuba wani abu hayaƙi ya tashi, sannan ya matso kusa da su ya ɗibi wani ruwa mai warin gaskiya ya watsa musu, kafin ya sake ɗibo wani garin magani ya kaɗa a ruwa ya basu suka sha, sannan yayi kabbara Allahu Akbar... Allahu Akbar.... Allahu Akbar, sau uku, abin mamaki sai ga Majeed da Najma sun baiyyana cikin kayan da suka fito dashi daga gidan tun watanni takwas da suka wuce, dukkansu a durƙushe suke, sai da tsohon ya sake ɗibo wani man shafawa ya shafa musu a guwaiwar hannu da ƙafa da wuyansu, kafin ya umarcesu da su miƙe tsaye, suka miƙe tare da fara rarraba idanu, dukkansu sai suka fashe da kuka a tare, tsohon ya ɗaga musu hannu kana yace "godewa Allah ya kamata kuyi, bai kamata kuna kuka ba, ya ƙwalawa yarinyarsa kira wacce bata wuce sa'ar Najma ba, sannan ya ƙwalawa yaronsa wanda Majeed ma zai girme masa kamar da shekara ɗaya, yace "a basu ruwan wanka da abinci, shi namjin ya bawa Majeed kaya, ita kuma macen ta bawa Najma kaya, suka amsa da cewa "to"... KANO ana gobe birthday party ɗin Laurat, Aysha ta gayawa anty Tasneem da Umaimah, bata hanata zuwa ba, hasali ma har tambayarta tayi mai zata kai wa ƙawar Tata a matsayin gift, Aysha tayi shiruuu, sboda bata sam mai ya dace ta kai mata ba, anty Tasneem tace "gobe idan Allah ya kaimu sai in baki abinda zaki kai mata, "Umaimah zakije koh?" Aysha ta tambayeta, "Eh man zuwa sosai ma" Umaimah ta bata amsa, wunin ranar dai sunata tsara irin shigar da zasuyi, kai kace sune masu yin birthday ɗin,  yau kusan kwananta uku bata kunna wayarta ba, Umaimah tayi tayi akan ta kunna saboda kar Zayden yayita tunanin ko bata cikin ƙoshin lafiya amma fur taƙi sai yau, kamar jira yake yi, ta kunna wayar, aiko sai ga kiransa tare da text message, kiran nasa ta ɗaga, cikin sanyaya murya, "amincin Allah ya tabbata ga masoyiyata abin alfaharina, ina fatan dai kwana biyu lafiya?" "Uhm lafiya lau" "Mai yasa wayarki bata shiga," "Haka kawai" "Kinason ki azabtar dani ne?" Ta fashe masa da kuka mai sauti, da sauri ya kalli wayar dake hannunsa kana ya kara a kunnensa kafin yace "Please beauty ki gayamin meke faruwa?" "Zayd ina sonka, bani da damar da zan iya furta maka hakan" Ta katse kiran tare da ajiye wayar, dariya ta farayi ga hawaye na, zuba, ta share hawayen, tare da kallon gefenta taga babu kowa, hamdala tayi kana ta tashi ta shiga toilet ta ɗauro alwalah kana ta shimfiɗa sallahya sannan ta kabbara sallahar magriba, tana cikin yin Sallah sai ga Umaimah ta shigo, da alamu daga can parlorn ta ɗauro alwalah, itama ta kabbara sallah, bayan sun idar sunyi addu'oinsu, Aysha ta kalli Umaimah, kafin tace "kinsan me?" Umaimah ta girgiza kai, Aysha tace "wlhi har tunanin ranar da zan koma gidan Hajiya nakeyi, babbar damuwata yah Ma'aruf, bashi da mutunci ko kaɗan" Umaimah tace "uhm na taɓa ganinsa sau ɗaya a wata hira da akayi dashi a TV, wlhi bana fata in ganshi a zahiri, saboda Guy ɗin akwai kwarjini sosai, ga shi Ubangiji ya haɗa masa komai duka, ance ɗan adam tara yake bai cika goma ba, nikam a ganina wannan bawan Allahan ya cika ɗari ma, ga kyau ga kuɗi ga izza wow amma fa tsoronsa nakeji" Aysha tayi murmishi kana tace "wato Umaimah, babbar damuwata komawa gidan, kamar dai yadda na gaya miki, dalilin da yasa na fara tunani, hamm uncle Junaid ya kusa dawowa kinga anty Tasneem bazata barmu a gidannan ba, i swear" Umaimah tace "faɗi ki ƙara barinma kekam da zaki sace zuciyar duk wani lafiyayyen namijin da yayi tozali dake" Aysha ta zaro idanu tare da cewa "wlhi sharri dai babu kyau" Umaimah tace "wlhi gaskiya nake gaya miki lokaci ɗaya kika wani cika, ƙila baki ga hips ɗinki bane ko?  One Month nazo gidannan lokacin ma ƙirgen dangin da kika farayi ƙanana ne, ga shi yanzu har ana saka bra, uwa uba 3 weeks ago kika fara period, hmm ai dole ki fara tunanin makomarki, amma ya maganar makarantar ki fa?" Uhm Umaimah, alhmdulilah insha Allah na koma Abuja zan ci gaba, amma nafison mai haɗe da islamiyya" Umaimah tace "ai karatun addini yanada kyau sosai, haɗuwarmu zatayi wuya sai dai a waya, wlhi zan gargaɗeki karki kuskura ki nunawa wani wayarnan, idan ba haka ba, wlh sai kin shiga tashin hankali" Aysha tace "hauka nakeyi Umaimah?" Aysha ta faɗa tana riƙe baki, Sunsha hira a daren, bayan an kira sallahar isha'i sunyi suka kwanta, wayar Umaimah ta fara ringing, tana dubawa taga Zayden, ta zaro idanu, tare da cewa "Aysha ga masoyinki ya kira, tayi kamar bazata karɓi wayar ba, ta miƙa hannu ta karba tare da karawa a kunnenta, "aslmu alaikum" Tayi sallama, "Wlkslm" Zayden ya amsa, daga jin muryarsa ma ta nuna yanayin damuwar da yake ciki, Kafin yace "beauty dan Allah ina son in roƙeƙi wata alfarma, sannan inason ki gayamin iya gaskiyarki saboda bana son ƙarya.." In Cold voice tace "ina jinka" "Aysha kina sona, tsakaninki da Allah?" "Tayi shiru, kafin tace "eh sosai ma" Yace "good" Ya sake cewa "Aysha bana son idan muna magana ki dinga katse min kira" Cikin sanyin murya tace "bazan sake ba" A karo na uku ya sake cewa "yanzu meye yake damunki?" Ta marairaice murya tare da cewa "babu komai" "Yaushe zamu haɗu" Kai tsaye tace masa "ko gobe" Yace "a ina zamu haɗu?" Ta jujjuya idanu kafin tace "zan kiraka, ƙawata ce zatayi birthday" Yace "okay, Allah ya kaimu" Tunda ya katse wayar Aysha, tunani iri-iri ya dameshi, sakamakon sonta da yake neman zautar dashi, duk inda ya zauna sai ya yi maganarta har cikin danginsa da abokansa, shi kasansa ya kasa misalta son da yake yi mata, wanda bai taɓa yiwa wata mace a faɗin duniya ba" Itama a nata ɓangaren haka ne, soyayyar Zayd ta fara nisa a zuciyarta. Har Umaimah tayi barci tana rungume da wayarta... Washe gari Tun bayan da sukayi sallahar asbha suka fara aikace-aikace, daga nan sukayi wanka, already dama babu school sboda malamar su anyi wa wata Malama cs headmastern su shima yana Hospital, A gurguje sukayi breakfast sukuma masu aikin sukayi moping, Ƙarfe 9:am abinci ya kammalu aka jere a dinning, sai da suka shirya tsaf, cikin Abaya baƙaƙe, sunyi matuƙar kyau, saboda abayar ta amsa sunanta, duba da ƙyaleƙyalen dake jikinta, duk wanda ya kallesu tabbas sai ya sake kallo, saboda har wani walwali takeyi sukayi rolling veil ɗin a kansu, ba wani abinci mai yawa sukaci ba, tsabar ɗoki da murna, anty Tasneem ta kawowa Aysha wata haɗaɗɗiyar sarƙa mai zobe, da turare mai tsada harda su ribom masu kyau, Masha Allah sunyi kyau sosai, Aysha tayi godiya tare da cewa "anty bakice munyi kyau ba" Anty Tasneem tace "wlhi kunyi kyau sosai, sukayi hoto, Tare da yi mata sallama, kasancewar ko wacce ta fito da hand bag ɗinta, anty Tasneem ta miƙawa Umaimah 10k tace ko zasuyi siyi wani abun, sukayi mata godiya kana suka wuce. Kai tsaye parking space suka nufa, sukayi wa driver kwatancen anguwar da zai kaisu, suka shiga backside yayiwa motar key bayan an buɗe masa get. Cikin ikon Allah suka iso anguwarsu Laurat har ƙofar gida ya kaisu, suka gaya masa time ɗin da zai dawo ya ɗauke su, ya wuce. Nocking sukayi a get na gidan, mai gadi ya leƙo tare da cewa "sannunku daga ina?" Umaimah tace "nan ne gidansu Laurat?" Da sauri mai gadi ya gyaɗa kai gami da cewa "eh nan ne, amma daga ina kuke, kuyi hakuri wannan tambayar da nakeyi muku tana ɗaya daga cikin sharuɗan shiga wannan gidan" Aysha tace "babu komai, ta buɗe hand bag ɗinta kana ta ciro wata ƴar takarda sannan ta miƙa wa Umaimah, tace ta kira mata lambar, ringing ɗaya Laurat ta ɗaga tare da cewa waye?" Aysha tace "gamu a ƙofar gidanku" Cike da murna Laurat ta katse kiran tare da fitowa harabar gidan tana yiwa mai gadi magana akan ya buɗe musu get, bayan ya buɗe musu suka shigo, wow, hmm masu karatu gidan fa Masha Allah komai yayi, hatta motoci biyar ɗin dake jere a gurin ajiyar motoci duk na yayi ne masu tsadar gaske, Laurat tana sanye da gown irin ƴar kanti, kanta yasha gyara sai sheƙi yake yi Masha Allah, daga nan tayi musu iso zuwa cikin gidan, babu kowa a gidan, saboda an ɗaga birthday ɗin, sakamakon Dad ɗin ta yace ta bari sai next week, Aysha kuma bata sani ba shiyasa suka zo, kai tsaye ɗakinta ta kaisu, ɗakine babba kai kace ɗakin wata macen, Masha Allah ɗakin yayi kyau, bayan sun shiga suka zauna a wasu ƙawatattun kujeru, Laurat ta fita zuwa kitchen, ta kawo musu sakwara da miyar egusi, da kunun gyaɗa mai ɗumi wanda ya ji coconut da milk, Bayan ta ajiye musu a saman table ta koma ta zauna, kafin suka fara gaisawa, nan take gaya musu ai an ɗaga birthday ɗin, Aysha ta ciro kayan da Anty Tasneem ta bata ta miƙa mata, sosai Laurat tayi farinciki da wannan tsaraba, saboda a halin yanzu sun shaƙu da Aysha sosai, Basu wani ci abincin sosai ba, Laurat ta ƙurawa Aysha idanu, A'isha dai da ta gaji da kallon da Laurat keyi mata tace "ke ya dai lafiya?" Laurat ta sauya mood zuwa na damuwa, kafin tace "Ƙawar Aysha Please sunanki fa?" Umaimah tayi murmishi kafin tace "sunana Umaimah, ni ƴar uwarta ce" Laurat tace "alhmdulilah" "Dan Allah Umaimah ki taimakeni akan manufata Please ku fahimceni dan Allah" Sosai ta jefasu cikin alhini duk da basu ji me take son cewa ba, Laurat ta sakko ƙasa tare da durƙusa guwaiwoyinta ƙasa, ta haɗe hannayenta kafin tace "dan Allah Aysha kiyimin wata alfarma dan Allah" Aysha tace "Laurat wace irin alfarma ce hakan, da har kika durƙusa min?" Laurat ta shiga gallery na wayarta ta nuno wani kyakkyawan hoto, wanda wani matashi ne a jikin hoton, shi ɗin ba fari bane, baƙi ne, sannan baƙinsa ba mai muni bane, yanada gashin baki mai kyau, sannan ya gyare sumar kansa, ta nunawa Umaimah, kafin tace kinsan wannan?" Umaimah ta gyaɗa kai, tare da cewa "wannan ai yayi ambassador a ƙasar waje, kuma har yanzu ana damawa dashi dan na gaban goshi ne, ga kuɗi kamar zai kasheshi" dukkansu basu san me take nufi ba, tace "kuyimin alƙawarin duk abinda nace zaku amince" a tunaninsu wata maganar ko neman shawara takeyi, cikin haɗin baki suka amsa da cewa "zamu amince" "Laurat tace "Aysha dan Allah ki auri Dad ɗina, shine a jikin hotonnan, ni kaɗai nake zaune a gidannan sai masu aiki, sannan shi bai cika zama a Nigeria ba, sannan yana dawowa Nigeria baya cin abincin waje ko na masu aiki nice nakeyi masa, tun bayan rasuwar mahaifiyata, tana aihuwata ta rasu, wlhi tallahi Aysha baki da matsala da Dad, ƴan uwansa sunyi masa maganar aure har sun gaji dan Allah ki taimakeni" Laurat ta ƙarshe maganar tana, sake cewa "karki manta keda Umaimah kunyi min alƙawari, sannan Ubangiji yana girmama alƙawari" Kuka take yi sosai, yayinda Aysha ta daskare a gurin, Umaimah kam ta kasa koda motsa bakinta ne, tsabar firgici, saboda basuyi tunani ko tsammanin jin waɗannan zafafan kalaman daga bakin Laurat ba, ta sake fashewa da kuka tana cewa "Please nasan zaki iya kinada hankali nutsuwa tausayi da duk wani hali na gari da namiji ya kamata ya samu gurin mace, Please say something...! Tofa, 2days nayi talauci, rashin data yasa banyi muku posting ba, kuyi hakuri dan Allah. Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋           Mom Islam Page 61-62 "Innalillahi wa inna ilahir raji'un" Hajiya Lubabatu ta ambata, cikin yanayi na damuwa, kana ta ci gaba da tafiya tana jimamin Gudidi, babbar damuwarta ina zataje..sannan da su wa zata hadu...a wane hali zata kasance?" Har ta iso gurin get ɗin gidanta tana ci gaba da tunaninta,  nocking tayi mai gadi ya buɗe mata, kana yayi mata sannu da dawowa ta amsa tana shigewa ciki, tun kafin ta kai ga shiga cikin gidan ta fara ƙwalawa Rukaiyya kira, amma shiru, kamar babu kowa a gidan, sosai ranta ya ɓaci ta shiga ɗakinta tare da duba ko ina babu Rukaiyya babu alamarta, wasu kaya ta gani a saman kujera sunkai kala tara, duk na Rukaiyyan ne, ta nemi guri kana ta zauna tare da tunani iri-iri kwance a zuciyarta. Hotel Tun ƙarfe 10:am Rukaiyya ta bi Sabeer ga shi yanzu har ƙarfe 4:pm bata dawo ba, hankalin Hajiya Lubabatu ya tashi sosai, saboda bata san Rukaiyya tana yawace-yawace ba, Astagfirullah innalillahi wa inna ilahir raji'un, dan girman Allah iyayena mata mu kula, tabbas duk wanda Ubangiji ya azurta da aihuwar ƴa mace, tofa bata da kwanciyar hankali har sai ta ganta a ɗakin mijinta, bawai dan kinada budurwar ƴa ki sake mata komai ba, wlhi tallahi mu kula, ranar lahira sai Ubangiji ya tambayemu, akan tarbiyya, Suna kwance a saman bed ya rungumeta, ga dukkan alamu babu kaya a jikinsu, hankali kwance suke barcin, Ruqaiyya ce ta fara farkawa, da sauri ta sauko daga gadon tare da wucewa toilet tayi wanka ta tsarkake jikinta, kafin tazo ta fara tashin Sabeer, a hankali ya buɗe idanu tare da cewa "Ruky karki damu fa.." "Wane irin kar in damu har ƙarfe biyar da rabi tayi, ka kalli agogon dake jikin bango ka gani mana, idan momy tazo ai na shiga uku wlhi sai ta kusa kasheni" Ruqaiyya ta faɗa tana yayibo ƙaton hijabinta da hand bag ɗinta, da sauri ya tashi, cikin sauri shima ya shiga toilet ɗin, tare da yin wanka kana ya fito, ko mai bai shafa ba, ya sanya kaya yayi mata rakiya suka fito har harabar hotel ɗin, "ban gane ba mai kake nufi?" Ruky tayi masa magana saboda ta fahimce bazai mayar da ita gida ba, "kinga kiyi hakuri Wlhi barci nakeji sosai, kinga a irin wannan condition ɗin bai kamata inyi driving ba, sai mu samu matsala" Ya ƙarashe maganar yana ɗaga mata gira, "Uhm Sabeer ni zaka wulaƙanta, a lokacin da ka buƙaci jikina ɗaukoni kayi har nan, bayan ka biya buƙatarka sai ka watsar dani ko?, kana nufin sai gobe kuma idan ka sake jin wani jarabar sai ka nemeni?" Tayi maganar tana zubar da hawaye, kafin ya buɗe baki yace mata wani abu, har ta buɗe get ta fice da gudu, tana kuka, tafiya take tana cewa "tabbas Allah ba azzalumin kowa bane, na cutar da kaina wayo Allah, bansan mai yasa Sabeer ya lalatamin rayuwa irin haka ba, innalillahi wa inna ilahir raji'un, ta dinga mai-maitawa tana kuka, sai da ta gaji da tafiya, kafin ta tsari mai adai-daita ya kawo ta har ƙofar gida, koda ta fara buga get ɗin kamar zata cireshi tsabar bugu, saboda gabaki ɗaya bata cikin nutsuwarta, mai gadi ya taso zai yi masifa ya ga itace ai yayi gum da bakinsa, da gudu ta shiga gidan tana ci gaba da kuka, har ta shigo parlon momynta tana cigaba da gunjin kuka, Momyn ta fito da sauri kana ta kalli Rukaiyya tare da cewa "Rukaiyya ina kikaje me kuma ya faru?" Bakinta ta toshe da tafin hannunta tana kuka, Cikin daka tsawa tace "ina kikaje?" Muryarta na sarƙewa tace "mo..mo...momy, na...na...naje, islamiyya ne, shine malaminmu ya ce ya koremu" Momy ta nemi guri ta zauna, kafin tace "amma ai baki gayamin zakije ba" Tana shesheƙar kuka tace "momy Ummu ce tazo bayan fitarki tace wai yau akwai islamiyya, kai tsaye momy tace "toh shikenan" "Mai ya haɗaki da Yarinyar nan, na ganta a can kusa da bakin titi, ko da na tambayeta, na nemeta na rasa ta gudu?" Zaro idanu Rukaiyya tayi, kafin tayi yunkurin bata momy amsa, cikin rashin tsammani amai ya taho mata wanda ita kanta bata san da zuwan aman ba, "innalillahi Rukaiyya dama baki da lafiya ne"? Ta jefo mata tambaya, tana miƙewa da sauri ta kawo ruwa a cup kana ta shafa mata a fuska, sannan ta riƙe hannunta suka shiga toilet, ta wanke baki, acan toilet ɗin ma tayi amai sosai, lokaci ɗaya jikinta ya fara karkarwa, cikin sauri momy ta ɗauko mata rigar sanyi, tare da cewa "Rukaiyya mai yake damunki?" "Uhm momy wlhi zazzaɓi ne" Momyn ta fice da sauri tana ƙwalawa mai gadi kira akan ya kira mai mashin, Bai daɗe da fita ba, sai ga shi nan ya shigo tare da mai mashin ɗin, ta riƙe hannun Rukaiyya suka fito harabar gidan, momy ta miƙa mata hijab ta saka, kana ta hau mashin ɗin momy ta hau bayanta suka wuce Hospital, Sai da suka fara ganin likita, akayi wa momy tambaya "tun yaushe ta fara rashin lafiyar?" Momy tace "yau ne ta dinga amai" Doctor yace za'ayi mata test, momy tace babu komai, Bayan an ɗibi jininta aka bata wata roba tayi fitsari a ciki, kana aka ce suje su zauna kafin su jira result sai asan taimakon da ya dace a bata, sun ɗan jima a saman benci a zaune, doctor ya ƙwalawa momy kira, bayan ta zauna yace "tanada aure ne?" Momy tace "bata da aure yarinyar da ko samari bata da su" doctor ya jinjina kai kafin ya fara sosa kansa, saboda ya kasa yi mata bayanin abinda ke faruwa, cikin tuhuma momy tace "doctor lafiya naga bakinka yana ta motsi kamar kana son cewa wani abu?" Doctor ya ajiye pen ɗin dake hannunsa kafin yace "Hajiya idan yarinyar ki ce, tanada cikin wata biyu, idan baki yarda ba zaki iya zuwa wani Hospital ɗin. Tun da ya fara magana momy ta daskare a gurin, lokaci ɗaya jikinta ya fara karkarwa, da sauri ta ce "Doctor ciki fa kace?" Doctor ya sake gyaɗa kai, "Nagode nawa ne kuɗin?" Ya gaya mata ta bashi sannan ta fice da sauri, "Rukaiyya tashi mu je gida" Momy ta faɗa tana kallon Rukaiyyan, kafin ta miƙe, momy ta rigata yin gaba, sboda jikinta babu ƙarfi sosai, momy na fita a hospital ɗin ta iso bakin titi, hankali a tashe, Ruqaiyya na zuwa suka hau mashin suka dawo gida, bayan sun shigo parlorn Ruqaiyya ta nemi guri a 3sitter kana ta kwanta, sboda kasalar da takeji, sai da momy ta wuce ɗakinta tasha kuka mai isarta kafin ta fito parlor, "Ruqaiyya tashi zaune" Momy ta faɗa a taƙaice, Ruqaiyya ta tashi zaune kamar inda momy ta buƙata, "waye yayi miki ciki, ashe dama yawon banza kike zuwa?" Momy ta jefo mata waɗannan tambayoyin, ƙirjinta ne ya bada rass, ta dafe ƙirji kafin tace "haba momy kinfi kowa sanin wacece ƴarki, wlhi bana bin kowa hasali ma ko saurayi bana..." Momy ta gwaɓe mata baki tare da cewa "wlhi tallahi idan har baki gayamin wanda yayi miki ciki ba, sai na kasheki" Da sauri ta zabura, kafin momy tayi wani yunƙuri ta ɗauki wayarta ta gudu, kasancewar get ɗin abuɗe yake, ta fice. Momy ta ɗora hannu a kai tare da kurma ihu, tsananin baƙinciki da takaici yasa ta kasa furta komai, a gurin ta durƙushe tana kuka, a halin yanzu bata san wa zata ta ra da wannan maganar ba, waye zai fahimceta?"...       ***** Har yanzu tana emergency room bata san inda kanta yake ba, shiko yana zaune a office ɗin doctor, kasancewar doctorn abokinsa ne, yayi tagumi cikin wani irin yanayi, sai mai-maita Innalillahi wa inna ilahir raji'un, gabaki ɗaya ya gama rikicewa saboda tunaninsa yarinyar da ya bige bazata rayu ba, mutuwa zatayi, duba da jinin da ya zuba daga jikinta mai yawa sosai, Doctor yace "Prince Murad ka kwantar da hankalinka da izinin Ubangiji komai zai zamo normal" Prince Murad ya miƙe tsaye, sanye da Kayan sarauta, tsantsar cikar kamala da izza gami da ruwan sarauta duk sun yalwatu a jikin Prince Murad, "Allah ya bata lafiya" ya faɗa yana ficewa a office ɗin, doctor ya amsa da amen" Dama dogarensa na daga bakin ƙofa, suna ganin ya fito, suka zube a gurin suna miƙa jinjina, Ransa a ɓace yake, saboda ko kaɗan baya fatan ya ga ya wulaƙanta wani ɗan adam a doron duniya, burinsa kyautatawa al'umma, Kai tsaye haɗaɗɗiyar motarsa ya shiga,  drivernsa  ya rufe murfin motar, ganin haka yasa dogarai suma suka shiga tasu motar, Prince Murad yace kaini "gurin Umma" Kai tsaye suka wuce garin MANDU, har cikin gidan sarki suka shigar da motar, inda sukayi parking a inda aka tanadarwa motoci, bayan an buɗewa Prince Murad murfin mota ya sauko da ƙafarsa ɗaga, kafin ya sake sauko da ɗayar ƙafar, yanayin takunsa kaɗai ya isa ya tabbatar maka da ko shi waye, yana tafe dogarai na biye dashi, ko da yazo shiga babban parlon Sarauniya, tsayawa sukayi daga bakin ƙofa, tafiya yakeyi ko gabansa baya kallo, saboda tsananin ɓacin ran da yake ciki, bai yi tunanin kiranta a waya ba, har ya wuce parlon bai san da cewar Sarauniyar na zaune a parlon ba, hadiman ta suna ganin Prince Murad suka duƙar da kansu ƙasa, "Murad lafiya na ganka cikin wannan yanayin?" Sarauniya ta tambayesa, tana daga kishingiɗe a saman wata kujera mai kama da katifa tsabar taushi, da sauri hadiman suka fice, suna cewa "Allah ya taimakeki Allah ya ƙara Miki lafiya, mun barki lafiya" a hankali ya juyo cike da sarauta, kafin ya zo gabanta ya nemi guri ya zauna a saman Capet, kana yace "Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana Umma na kusa kisan kai, a halin da ake ciki ma, wlhi bansan zata rayu ko bazata rayu ba oho" a ɗan firgice ta tashi zaune tare da gyara zaman alkyabbar dake jikinta, kafin tace "Murad mai kake nufi ban gane ba?" Idanunsa sun kaɗa sunyi jajir yace "Umma muna cikin tafiya a mota, Umar driver ya kaɗe wata yarinya tana can rai a hannun Allah, Umma yanzu idan har yarinyar nan ta mutu ya zamuyi?" Sarauniya tace "Murad ka kwantar da hankalinka, komai fa ikon Allah ne, shi yake raya wanda yaso sannan ya kashe wanda yaso, yanzu dai waye a gurinta?" Kan Murad a duƙe yace "Allah ya taimakeki, Falmata ce a gurinta" Sarauniya ta jinjina kai, sannan tace "ya kamata kaje kayi wanka kaci abinci, saboda kar ulcer ɗinka ya tashi, idan baka manta ba, doctor ya ɗoraka akan magani sannan yace "ba'a son ka ji yunwa komai ƙanƙantar ta?" ya miƙe tare da fita daga sashen mahaifiyar tasa kafin ya wuce sashen sa, wani haɗaɗen ɗaki ya shiga ko ina walwali yakeyi Masha Allah, a kujera one sitter ya zauna, ya fara tuno irin hatsarin da sukayi, yana tsaka da tunani, Ruma ta shigo fuskarta ɗauke da murmishi, ko sallama babu ta yiwa kanta mazauni, kafin tace "yaya Murad lokaci yayi da zamu fito mu faɗawa mai martaba da Umma cewar mun shirya a ɗaura mana aure.." da sauri ya kalleta, kallo yakeyi mata mai cike da zallar tsana, ransa a ɓace yace "tashi ki fita.. ta wani matso kusa dashi tare da cewa "ko kanaso ko bakaso aurena ya zame maka tilas ragowar jiji da kai da taƙama duk zanji dasu, nidai burina..." Kafin takai ƙarshen maganar ya wanka mata mari lafiyayyu masu zafin gaske, wanda yasa ta riƙe kumatunta, tare da ficewa da gudu, tayi sashen Fulani...! Comments and share fisabilillah Mom Islam ce 08141799224 NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋    Book Page 63-64 Kuyi following ɗina Arewabook https://arewabooks.com/u/momislam11                  _Mom Islam_ A hankali ta fara motsa hannayenta, tare da yunkurin tashi zaune, tsananin zafi da raɗaɗi ne sukai mata sallama, saboda duka jikin nata ciwo yakeyi mata, in ka cire goshinta da ya sha ɗauri, "yi haƙuri insha Allah zaki samu lafiya" Wata likita tayi mata magana cikin tausasa harshe, Tabbas tasan lokacin da ta zata tsallaka titi, bayan nan babu abinda zata iya tunawa sai ganinta da tayi a asibiti, meke faruwa da ita?, Kuka ta farayi tare da mutsu mutsu, wanda yasa ta kusa tsige drip ɗin dake hannunta, likitoci biyu ne a ɗakin hakan yasa suka riƙeta sosai, tana ta kuka, tana cewa "nikam na haƙura da rayuwar binni wlhi gara in koma gurin mahaifiyata wayo Allah na zan mutu waiyyo Allah..." Duk waɗannan maganganun da takeyi, a kunnen Prince Murad ta yisu, ba kayan ɗazu bane a jikinsa ya sauya wasu, sai dai a sama akwai wata ƴar riga mai tambarin gidan sarauta a jiki, ga dukkan alamu bayan yayi wanka ne ya dawo Hospital ɗin, cikin takunsa mai ɗaukar hankali ya shigo room ɗin tare da amsa gaisuwar likitocin da sukayi masa, "ya jikin?" Ya tambayeta cikin dakakkiyar muryarsa, Waro idanu tayi, kafin tace "da sauƙi, kana ta mayar da kai ta kwanta, ammafa abin ya bata mamaki, gani takeyi kamar wani ɗan gidan sarauta ne, sboda sunsha zuwa kallon al'adun sarakuna da akeyi a ta wajajen ƙauyukan su, "mai kike da buƙata" Prince Murad ya tambayeta" Duk da raunin dake a goshinta bai hanata yin murmishi ba, a zuciyarta tace "wannan fa wata dama na samu da zanci abinda zuciyata takeso" "Kaza nake son ci wlhi idan da hali kace asa yaji sosai, amma kayi haƙuri idan baka da kuɗi ko kifi ka siyomin" Tayi maganar tana runtse idanu, sabida lokaci zuwa lokaci jikin nata kan ɗan yi mata zafi, "Shi kenan" ya faɗa yana miƙewa kana ya fice, dogarai suka ci gaba da binsa tare da securities, acan harabar asibitin ya hango Falmata tana tsaye tana waya, ga dukkan alamu wayar da takeyi tanada muhimmanci, tabbas yin hakan da tayi ya sosa masa zuciya, an bar mai jinya ita kaɗai, hakan bai dace ba, Bayan komawarsa gida, a harabar gidan, ya tarar da Umma wato mahaifiyarsa matar sarki  tana shirin shiga mota, sai da ta jira ya fito, tayi masa ya mai jiki, kafin tace masa Hospital ɗin zataje sboda ta dubo jikin yarinyar" Prince Murad yace "Allah ya ƙara miki lafiya, godiya nake Ubangiji ya kaiki lafiya ya dawo dake lafiya, Allah ya tsare gabanki da bayanki ummana, sosai take ƙara jin son ɗan nata guda ɗaya tilo wato Murad a cikin ranta, saboda nutsuwarsa da hankalinsa,  yayi mata Allah ya tsare ta shiga mota suka wuce. Har motarsu ta ɓacewa ganinsa yana tsaye a gurin, ya sanya hannu a aljihun rigarsa ya ciro wayarsa, number drivernsa umar ya kira, bayan ya ɗaga yace masa, inason ka koma Hospital yanzu, amma kafin kace, ka siya mata kaji guda uku masu kyau sai ka kai mata, ka haɗa mata da lemun kwalba kokuma dasu fruit" Cike da girmamawa driver Umar yace "an gama ranka ya daɗe, abinda kace shi za'ayi Allah ya ƙara maka lafiya" Ya amsa da Amin. Acan Hospital, tun da Gudidi ta farka bata sa wata Falmata a idanunta ba, tunda bata san ma itace mai jinyarta ba, ko da ta ga, Prince ya fita, ta cuno baki, tare da cewa "mtswww a sawa mutum rai da abu sai ya gama ammanna sannan a yaudarehi" Sallamar da taji anyi tare da turo ƙofar ne yasa ta sake ware idanunta tana ƙare wa Sarauniya kallo, tana cikin shiga ta alfarma wacce duk wanda ya ganta sai yayi sha'awar sake ganinta, sanye take da farin leshi mai adon duwatsu masu sheƙi, ta sanya alkyabba daga sama, ƙarasa shigowa sukayi itada jakadiya, hannun jakadiyar riƙe da wani babban basket mai kyau, ta ƙaraso tare da ajiye wa a can nesa da gadon da Gudidi take kwance, "ina wuninku" Gudidi ta faɗa tana rarraba idanu, Umma ta amsa da "lafiya lau ya ƙarfin jikin?" Gudidi tace "yai sauƙi, amma yunwa nakeji" Umma tayi murmishi tare da cewa "Masha Allah, jakadiya a tambayeta mai takeson ci" Umma ta miƙe tare da fita waje, kira ne ya shigo wayarta, da alamu kiran yanada muhimmanci, "ranka shi daɗe, Barka da wannan lokaci"  Sarki ya amsa da cewa "yauwa ya mai jikin, da sauƙi dai ko?" "Eh da sauƙi ina tunanin zuwa anjima a sallameta, sboda naga jikin nata alhmdulilah" Umma ta tabbatarwa da mai martaba, "Cikin bada umarni yace "idan an sallameta a taho da ita nan, ta huta kafin.." Ya katse kiran. Kai tsaye ta kira Prince, ta sanar masa da umarnin da mai martaba ya bata, shima yayi na'am, sukayi sallama ta katse kiran. Cikin umarnin Umma jakadiya ya bubbuɗewa Gudidi foodflaks, kafin tace "wanne kike son ci?" Waro idanu tayi, cike da nuna ƙauyanci tace "duka ma zanci, amma dai ki fara zubomin farfesu" jakadiya ta ɗauki plate kana ta zubo mata farfesun sannan ta miƙa mata, Ci ta farayi hannu baka hannu ƙwarya, abin har yaso bawa jakadiya tsoro, da sauri ta matsa kusa da gudidi tace "akwai  abin da kike da buƙata ne bayan wannan?" "Eh ai komai ma zanci kedai miƙomin waccan tuwon hinkafar, malmala biyu" Jakadiya ta zaro idanu, dole ta saka mata, tunda umarni aka bata, Kamar inda ta ɗauki alwashin cin duk abinda ke cikin basket ɗin, aiko sai da taci, kaɗan ta rage, sallamar Umar driver ne yasa tai saurin goge bakinta, sbda tayi dumu dumu da manja, bayan ya gaishe da jakadiya ya wuce gurin Gudidi, yayi mata ya jiki, ta amsa kana ya ajiye ledar a saman loka, yace "kaji ne, inji Prince yace a kawo miki" Allah ya taimakeni an cire ruwan baturen da ake ɗura min" ta faɗa tana saukowa ƙasa, sai dai babu takalmi a ƙafarta, hakan bai saka ta damu ba, ta zauna a saman tabarmar dake shimfiɗe a gurin, kafin tace "kai wlhi kunada kirki Nagode sosai, tai maganar tana buɗe ledar jikinta har yana rawa, wasu manya manyan gasassun kaji ta hango, sai ƙamshi sukeyi, a hankali ta haɗiyi miyau, tare da cewa "uhm yasin zagina sukeyi, hikenan sabuwar duniya" ta faɗa tana yagar naman kazar, tunda ta tauna taji ya cika mata baki, ga daɗi ga garɗi, ta wani lumshe idanu, tare da kallon Umar tace "kai wlhi ka yimin hajji da Umrah, dan Allah kace masa na gode" Umar yayi murmishi tare da cewa "karki damu" Jakadiya kam, taga ikon Allah, sboda Gudidi ta fara bata tsoro, duba da yanda take ta zura abinci sai kace ba mutum ba, daga can  harabar asibitin Ummar ta wuce office ɗin doctor, ta lura da Falmata ba zama gurin mai jinya bane ya kawota, saboda ta samu labarin ta koma gida, Ya tabbatar mata da anjima za'a sallameta, already akwai wani ɗaki empty, Umma ta saka a gyara shi, duk da koda yaushe basa wasa da gyara ma'aikatan gidan, daga nan ta dawo ɗakin da aka kwantar da Gudidi, sallama tayi, suka amsa kana ta ƙarasa shigowa, "alhmdulilah ta ambata tare da cewa ,jiki yayi kyau, Masha Allah" Jakadiya tace "ai kuwa, nikam Allah ya taimakeki har gabana yana lugude" Umma tace "name fa?" "Hmm kaf abincin da aka kawo duk ta cinyesu har da kaza Umar ya kawo inji yarima ta kusa cinye guda ɗaya" Umma tayi murmishi, ba tare da tace komai ba. Da sallama doctor ya shigo hannunsa riƙe da takardar sallama, ya miƙa wa umma, cikin girmamawa, ta karɓa tare da cewa "Masha Allah, jakadiya sai a harhaɗa kayan ku taho tare" Umma ta faɗa tana buɗe kofar ɗakin ta fice, tunda ta fita daga ɗakin dogarai su duƙa kwasar gaisuwa, Bayan jakadiya ta kammala tattara kayan, ta bawa Umar ya fita dasu zuwa motarsa, ta riƙe hannun Gudidi da lokacin da ta miƙe take shirin faɗuwa, doctor ya bamu magunguna, kai tsaye suka wuce masarautar MANDU.. SINGAPORE Bayan kwana uku da yin taro, wani allo da oga Reed ya rataye tsafaffe wanda zai dinga yi masa nuni da adadin matan dake period, A yau ya sami mata sama da hamsin, wanda suka kai masa pad ɗinsu, a take a lokacin aka turawa da bokansa, shi kuma ya jira sakamako, acan ɓangaren Thabit ya matsa lamba dan ganin anyi nasara jiragen ruwa sun tsira daga hannun hukuma, cikin sa'a prime minister ya amince da tayin da Thabit yayi masa, cike da farin ciki ya samu Oga Reed ya sanar masa, wani irin hugging yayi masa cike da tsantsar farinciki, a take a lokacin oga Reed ya yiwa  Thabit kyautar wani danƙareren gidansa dake kusa da anguwar tasu, Sosai Thabit yaji daɗi tare da ce masa, ai wannan kaɗan ka gani daga aikin Thabit, nidai fatana in ga ance Jirgi ya iso" Wayoyinsa guda uku duka suka hau ringing, duk ya birkice yama rasa wacce zai ɗaga, wayar dake gabansa ya ɗauka kafin yace "Oga an saki jirginmu gamu a hanya" ɗayar wayar ma haka aka gaya masa, yayi farinciki sosai, ya sake ƙara yiwa Thabit wata kyautar, kafin yace "a cikin ƴan mata nan ya zaɓi guda ɗaya wacce zata dinga ɗebe masa kewa" dama wannan ranar yake jira, aiko yace "toh tare da sake yiwa ita Reed godiya" Tunda Misha ta koma ɗakinta hankalinta sam ya gaza kwanciya, "da gaske yake yi kokuma yaudararta zai yi? itaɗin wacece meye alaƙarta da musulmai, bayan ko hausarsu ma bataji, ta dafe kanta tare da miƙewa tsaye ta fara zagaye ɗakin, Neria dake barci ta jiyo surutan Misha sai kace a mafarki, duk da dai bazata iya maimaitasu ba, saboda sama sama take jiyo maganganun nata, murya irin ta mai barci tace "anty Misha lafiya kuwa, naga sai zirga-zirga kikeyi, kuma ga dukkan alamu bakya cikin kwanciyar hankali, tunda nazo ban taɓa ganinki cikin irin wannan yanayin ba sai yau Please mi ke damunki?" Misha ta furzar da iska mai zafi, tare da sauke ajiyar zuciya, kafin tace "Neria, bansan meye yake damuna ba, bansan meye yake tunkaroni ba, i don't know what to do" Ta tura hannunta da yasha farcen Bature cikin sukar kanta, tare da zubewa saman bed tana tsaki, "Amma ya kamata ki kwanta kiyi barci" Neria ta gaya mata itama tana mayar da kai ta kwanta. Zaune yake a gidan da Oga Reed ya bashi, dalilin zuwansa gidan shine.. A ranar da oga Reed yayi masa kyautar gidan yace ya kamata ya koma, saboda babu wanda yasan ko gidan waye, ta haka ne zasu dinga gano masu yi musu zagon ƙasa, saboda babu wanda yasan Thabit yana yiwa Ita Reed aiki, Washe gari. Tun da asbha yasa aka ɗauko masa Misha, yaso haɗawa da Neria, hakan ba zai yiwu ba, saboda CCTV camera yana nunawa iya Reed komai, dole Misha ya ɗauka, zaune suke a parlor tayi shigarta na arna kamar yadda ta saba, riga iya cinya sai takalmi mai tsini sosai a ƙafarta, wayarsa ta fara ringing, ganin number Umminsa yasa shi ɗauka tare da cewa "Assalamu alaikum ya Ummi.., afuwan wlhi Ummi ina son zuwa anjima zan tura da kuɗin ayiwa Marwa aikin na samu alhmdulilah" Ummin tayi murmishi daga can ɓangaren kafin tace "nidai matar da zaka aura  nakeson ka kawomin, yace...! Ayi haƙuri babu yawa please Mom Islam ce..08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋    Book Page 65-66                  _Mom Islam🍹_ "Ummi zamuyi magana zuwa anjima" Ya katse kiran yana kallon Misha, da itama shi ɗin take kallo, "Naga kamar kinason yin magana?" Thabit ya tambayeta ba tare da ya kalli fuskarta ba, "Waye kai, me kake nema a gurina..?" Ta jefo masa tambayoyi tana mayarda numfashi kamar wacce tayi gudu, Thabit yayi murmishi, kafin yace "ni ba kowa bane face bawan Allah, ban gaya miki wannan maganar dan in cutar dake ba, ki fahimceni taimakonku nazo yi" Da sauri ta miƙe tsaye, tare da cewa "babu wani taimakonmu da ka zo yi, in banda ka wulaƙantamu, ko da yake na fara tunanin kazo ka dulmiyar damu a cikin addininku ne, wanda babu komai a cikinsa in banda takura, shi yasa kake wani cewa wai asalinmu musulmai ne" Sosai ta bashi mamaki, saboda yin maganar kawai takeyi, sai ka ce ba a cikin haiyyacinta take ba, sai da ya bari ta gama surutunta kafin yace "duk abinda zaki faɗa sai dai ki faɗa, saboda taimakonku da nake sonyi ba zan fasa ba, dole in cika alƙawarin da na ɗauka" Ya ƙarashe maganar yana buga table ɗin dake gabansa, "Ka nemo min wine" Kai tsaye yace "musulunci ya haramta mana shan ta" ta wani juya idanu tare da yin bakin ƙofa, tace "ka janye duk alwashin da ka ɗauka a kanmu idan ba haka ba, tabbas zakayi nadama wacce baka taɓa yi ba" tana gama faɗar haka ta buɗe ƙofar ta fice da sauri... Iska mai zafi ya furzar tare da miƙewa tsaye ya fara zagaye ɗakin yana tunani iri-iri, Acan gidan oga Reed, yana zaune a ɗakin da yake ajiyar gwala-gwalai, fuskarsa fal farinciki da annashuwa, sakamakon isowar da jirgin ruwan yayi, har kayan sun shiga kasuwa, CCTV camera yake kallo, sboda tsarinsa ne, sanya ido akan komai da komai, hatta gidan da Thabit yake ciki yayi connecting da CCTV camera, yau ne ma ya fara ganin musayar yawun da Misha tayi da Thabit, Oga Reed yayi murmishi tare da cewa "impossible, wannan mutumin da biyu ya shigo rayuwata, akwai abinda yake nema... Acan ɓangaren Thabit, shikam bai ma san da akwai CCTV camera ba, sai yanzu da ya ɗaga kansa sama, a ɗan firgice ya sake kallon gurin, kafin ya sauke numfashi, shawara ɗaya ya yanke wa zuciyarsa, lokaci ɗaya yasa gidan a kasuwa, ko zai yi waya baya taɓa sakewa yayi a gidan, har ya zamo ma ya siyar da gidan, saboda oga Reed ya damƙa masa takardar gidan a hannunsa, ko da suka gama cikini ya samu abu ya lulluɓe Camera ɗin, a ranar da zai bar gidan kenan, A fili yace "Misha nayi niyyar taimakonku, hakan bai samu ba, amma nasan insha Allah watarana zamu haɗu, ya fice da school back ɗinsa, Kai tsaye ya wuce airport.. Oga Reed yabi ƙididigin camera na gidan Thabit amma ina, duhu kawai yake nuno masa, abin mamaki, ga shi rabonsa da Thabit ɗin yau kwana biyu kenan, tabbas idan beyiwa tufkar hanci ba, zai kaisa ya baro sa, 1:am na dare, yanada ikon shiga ko ina inhar ya kasance mallakinsa ne, dan haka kai tsaye ya fito daga gidansa ba tare da securities ba, cikin zafin rai ya nufi gidan Thabit ɗin, sai dai kash, ko da ya iso bakin get na gidan, ya samu an garƙame gidan da ƙaton kwaɗo, a gigice ya sake kallon babban kwaɗon, kana ya kai kallonsa ga wata takarda da aka manna a jikin get ɗin, "Gidannan ya zamo mallakin gwamnati, Nagode da karamcin da kayimin, dama na fito neman kuɗi ne, ƙanwata ce take Hospital babu lafiya, za'ayi mata tiyata bamu da komai a hannunmu, shiyasa nazo na taimaka maka" Oga Reed ya dunƙule hannu tare da kaiwa get ɗin naushi, cikin takaici yace "har yanzu ban gama yarda da kai ba Thabit, i swear akwai wata a ƙasa..." Washe gari, musamman yasa aka kirawo masa Misha, sosai ta firgita, saboda sai suyi 3monthts basu sanyashi a idanunsu ba, idan ba meeting zasuyi ba, bayan tazo ya dinga yi mata tambaya game da Thabit, babu abinda ta ɓoye masa, ya jinjina kai tare da yi mata godiya kafin yace "Misha, kinada sha'awar komawa wani addini ne?" da sauri ta girgiza kai tare da cewa "bana da" "Okay jeki, duk a tunaninsa maganganun da Thabit yayi mata sunyi tasiri a zuciyarta, Bayan tafiyarta, ya fara tunani iri iri, tare da ɗaukar alwashin sai ya sa an nemo masa Thabit duk inda ya shiga, mutanensa ya tura da motoci, akan subi duk wata hanya da suke ganin zasu sameshi, sai dai kash ya tsere musu, a halin yanzu ma ya sauka a ƙasarsa Egypt. KD ƙauyen ƴan kifi, Bayan sunyi wanka, Inna ta kawo musu ɗumamen tuwo sukaci, Haka suka ci gaba da rayuwa a wannan ƙauyen.. Wata ranar Talata, kwanansu biyar a gidan malam, sai dai babban abinda zai bawa mai karatu mamaki, bai wuce mancewar da su Majeed sukayi akan ko su suwaye ba, bazasu iya tuno asalinsu ba, sai dai ilimin da suke dashi yana nan zaune a brain ɗinsu da kuma sunayensu.. Yau ne malam ya fara tafiya da Majeed gona, sam Majeed bai iya komai ba, Haladu ne ya dinga nuna masa inda zai yi, Acan gida gurin Inna, kasancewar tana yawan fita kasuwa kai kaya kamar su, masara da sauran su hatsi dai, Karima ta kalli Najma ta taɓe baki, kafin tace "ke tashi kiyi wanke-wanke dan wlhi yau tsinke bazan kawar a gidannan ba, kamar inda Karima ta bata Umarni, ta miƙe ta tattara kwanukan kana ta kaisu mawanki ta wankesu tsaf, ta share gidan, Karima ta watso mata kayan wanki tace "ga sunan ki wanke idan ba haka ba in naɗa Miki na jaki" Najma ta waro idanu, dubada wankin yanada yawa sosai, tace "gaskiya sunyi yawa ba zan iya ba, ta miƙe tare da wanka mata mari, cikin zafin rai Najma ta rama, tare da cewa "a girma nasan na girmeki kawai dan kin ganni a gidanku, karki manta duniya da faɗi a duk inda muke ni da yayana Ubangiji zai karemu, tunda bamu san danginmu ba.." Karima ta kwashe da shewa tana ce mata, "wa ya sani ma ko a titi aka haifeku," Sosai maganar ta daki Najma ta runtse idanu, cike da ɓacin rai tace "wlhi ƙarya kikeyi" "Ubanki ne yake ƙarya?" Najma tace "nasan darajar iyayena" "Wato sai dai nawa uban ko" Karima ta faɗa tana cakumo Najma suka kaure da dambe, sosai suke damben, har Inna ta shigo, da gudu ta ƙara so kana ta yarda itacen dake kanta, Karima ta kurma ihu tana cewa "wayo ta watsamin barkono a idanu" Inna ta juya gurin Najma ta wanka mata mari, tare da cukume mata wuyan riga cikin faɗa take cewa "daga alfarma sai ki zaƙe zaki kashe ƴar masu gida, walhi tallahi baki isa ba, shegiya kawai" Najma ta fashe da kuka tana riƙe da kumatunta, zatayi magana Inna ta gwaɓe mata baki, Karima ta cigaba da gurje idanu, taci gaba da cewa "Inna wai dan nace ta yimin wanki shine ta wani cukumeni da faɗa" Inna ta riƙe baki, kafin tace "yo bata isa ta baki wankin bane? ko kina ganin zaki dinga cin abincin gidan ubanta a banza ne?" Najma ta rushe da kuka tana share hawaye, Sai da aka kira sallahar magriba kafin su Malam da Majeed da Haladu suka dawo gida, bayan anyi sallahar isha'i suka zauna cin abinci, daga nan kowanne Ya tafi makwancinsa, Washe gari, bayan su Najma sunyi sallahar asbha, har zata koma ta kwanta, Inna ta tasheta tace taje ta ɗibo ruwa a rijiya basu da ruwa a gida, ta miƙe jikinta yanayi mata ciwo, haka ta ɗauki bokiti Allah yasa ma rijiyar a gidansu take, bayan ta ɗibo ruwan ta ajiye, tare da komawa ɗakinsu ta kwanta a wani fallen zani, gashi inda take kwancen duk tudu da kwari, dayake babu siminti a ƙasa, itako Karima sai kwasar barcinta takeyi cikin kwanciyar hankali, Ƙarfe 7:am Inna ta gama dama koko suka karya, daga nan tace "Najma ta kwashe kofuna ta wanke, babu musu ta wanke, malam ya ƙwala musu kira su biyu, Karima na turo baki ta tafi, tare da harar Najma, bayan sunje yace zai aikesu kasuwa su siyo masa masara saboda yau ba zai samu zuwa ko ina ba, yace su je su sanyo hijabi, kamar inda ya umarcesu hakan sukayi, ɗan babu hali ta hana Najma aron hijabi saboda zata iya fuskantar faɗa daga gurin malam. Bayan sun zo gurinsa sun karɓi kuɗin, dama Karima ce ta karɓi kuɗin, suka fito ƙofar gida, Karima tayi tsaki mtswww... tare da cewa "ni Wlhi na tsani tafiya da baƙauyen mutum, idan munje guri yayita kalle-kalle" Najma dai bata ce komai ba, sun kusa isowa kasuwa, wata galleliyar mota tayi parking a gefensu, sukaci gaba da tafiya Karima nata zaginta, wani yaro ne ya taho da sauri yana cewa "wai wancan mutumin yana magana daku" Karima tace "ki tsaya anan bari inje inji dan nasan kekam sai dai baƙinjini" Harda ƴar rangwaɗa ta ƙarasa gurinsa tare da cewa "sannu da zuwa gani" tana washe haƙora, "Yi haƙuri ƴan mata ba ke nake kira ba, waccar wace kuke tare" Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokareta, ko tsayawa saurarar Najma batayi ba, ta wuce ta da sauri, ita da ta tsaya jiranta, cikin ɗaga murya yace "ƴan mata dan Allah ina magana" Najma ta tafi a hankali, cikin nutsuwarta kafin tace "ina kwana, lafiya lau, da fatan banyi laifi ba" Murmishi tayi masa wanda ya sake ƙawata kyakkwar fuskarta, yace mata tayi masa kwatancen gidansu, zai ga iyayenta, babu musu tayi masa yayi mata godiya, Karima na isa kasuwa ta auni masara ta kamo hanya bata ɗauko masarar ba, tace Najma ta wuce ta ɗauko, duk yana la'akare da abinda Karima take yiwa Najma, hakan yasa ya fara shan jinin jikinsa suɗin ƴan uwa ne kuwa? har suka ɓacewa ganinsa kafin ya fara bin su sannu a hankali... KEFFI Kamar inda boka ya bashi umarni na wanka cikin dare hakan ko akayi, yace momy ta rufe ƙofa shikam a ɗakinsa zai kwana saboda yanada wasu takardu da zai cike, bayan sunyi sallama ya dawo ɗakinsa, yana zaune har dare yayi sosai kafin ya fara hasaso inda zai je yayi wankan, saboda ance masa a tsakar gida, wani keɓaɓen guri ya samu a gidan nasa ya yi zigidir kana ya buɗe murfin jarkar ya fara tsiyayawa a kansa, tare da sha sau uku kamar yanda abokin nasa ya jaddada masa, daga nan ya dawo ɗakinsa yana sauke numfashi, Washe gari, da asbha dama babu maganar sallah, tunda umarnin boka ne, ƙarfe 10:am ya shigo ɗakin momy yana sanye da lallausan yadi, kana yace "shifa jiya ya kasa barci da tunaninta ya kwana, yanayi yana gyara hanky ɗin dake cikin aljihunsa, dama momyn a buƙace take, ta bada kai lokacin da ta gama lulawa duniyar Dady, cikin hikima ya shinfiɗa ƙyallen, ya kwanta akai kana ya ɗora momy a samansa, sosai suka gamsar da junansu, momy ce ta fara miƙewa ta nufi toilet, shi kuma ya fice zuwa ɗakinsa da sauri, leda ya samu ya ƙulle ƙyallen da niyar zai kaiwa boka.. Ina mai bada hakuri babu yawa, amma insha Allah zanyi ƙoƙari inyi muku mai yawa, Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 Free  Book Page 67-68                  _Mom Islam🍹_ Bayan dawowar su Umaimah gida.., Zaune suke a parlor, anty Tasneem tana ɗakinta, Umaimah tace "Aysha wace shawara kika yanke a game da auren baban Laurat?" Aysha tace "uhm ke nifa kaina ya ɗauki wuta, kina nufin in aureshi kokuma me?" "A'a Aysha kawai dai na tambayeki ne" Aysha tai shiru, tare da yin tagumi, a karkashin zuciyarta kam tunani ne fal, "anya zata iya amincewa da tayin da laurat tayi mata kuwa?" Wata zuciyar tace mata, ba fa shine yace yana sonki ba, dan haka kawai ki watsar da wannan maganar, Hakan ko tayi, tun daga ranar ta share maganar, Ranar Monday da ta koma school, suka haɗu da Laurat, canja mata fuska tayi, saboda kar ta sake yi mata maganar mahaifinta, amma Laurat ɗin bata damu ba, sai ta mance da alfarmar da ta nema a gurin Aysha ta dinga janta da hira, daga ƙarshe dai Aysha ta saki jiki, har aka tashi, Arman yazo ya ɗauke ta suka dawo gida. Kwanci tashi asarar mai rai yau watan Aysha uku, a Kano, ta samu sauyin rayuwa, gogewa da sauransu, saura sati ɗaya uncle Junaid ya dawo, dan haka anty Tasneem ta cewa Aysha ta shirya kayanta zata mayar da ita Kano, tunda dama sunyi da anty Jamila akan zatayi wata biyu ne, gashi har ta shiga na uku, a ranar da Arman ya ji maganar tafiyar Ayasha, sam bai ji daɗi ba, ganinta kawai da yake yi duk da bai furta mata wata kalmar soyayya ba, yana jin daɗi a cikin zuciyarsa, rana tsaka wai zasu rabu, anya bazai je ya gaya mata abinda ke cikin ransa ba kuwa?, wata zuciyar tace masa "No karkayi haka, har yanzu bata gama mallakar hankalin kanta ba, tukuna, ana gobe zata koma Abuja, sai da tabi gidan ƙawayenta tayi musu sallama, ko da taje gidansu Laurat, jiki a sanyaye suka fito harabar gidan, cikin tausasa harshe "Aysha idan har maganar da nayi miki akan ki auri mahaifina ne yasa kika ja baya da zumuncin mu, ina mai baki haƙuri, amma karki manta in daɗa tunasar dake lada zaki samu" Tai maganar hawaye na kwaranyowa daga idanunta, cikin Muryar kuka tace "Aysha ina yi miki fatan alheri" Itama Ayshar jikinta yayi sanyi sosai, saboda Laurat tanada kirki ga hankali, tunani takeyi, "mai yasa zuciyarta ta kasa amincewa da tayin da laurat ɗin tayi mata?" Aysha ta bata number wayarta, kana tace "zamuyi waya, insha Allah idan nayi shawara zan nemeki" A ranar ne tayi sallama da school sboda an nema mata transfer, Washe gari, ta gama shirya komai driver ita yake jira, Umaimah kam sai kuka takeyi, haka ma Ayshar sunsha kuka kamar ba zasu sake haɗuwa, tun jiya ta kira Zayd ta gaya masa, ransa sam beyi masa daɗi ba, babu inda ya iya dole sukayi sallama da niyar zasuyi waya. Ƙarfe 9:am aka shigar da kayanta Booth, sosai ta rungume anty Tasneem tana ce mata, bansan da me zan saka miki ba, anty Tasneem Allah ya faranta miki, Umaimah ma rungumeta tayi, tana kuka ta shiga mota, har driver ya fice a gidan suna ɗaga mata hannu, tun kafin a kai ga wuni, sunji gidan shiru babu daɗi, saboda Aysha sam bata da matsala a rayuwarta, sannan ta kasance mai barkwanci, kowa nata ne, yah Arman kam ko leƙowa beyi ba, shikam har ga Allah ya so ace zatayi ta rayuwa a gidan har lokacin aurensu yayi, Suna fita a anguwar ta ciro wayarta, kunnawa tayi, kana ta fara lalubar number Zyd, kamar jiran kiran nata yakeyi, da sauri ya ɗaga tare da cewa "amincin Allah ya tabbata ga beautyna" ta lumshe idanu kamar yana kallonta kafin tace "tare da kai, muna hanyar zuwa Abuja" in Cold voice yace "Allah ya kaiku lafiya Beautyna Please idan kin sauka ki kirani" ta waro idanu tare da cewa "taɓɓ, so kakeyi a ƙwace wayar?" "Toh shikenan ina dai jiran kiranki" Ya faɗa a taƙaice, ba wata hira sukayi ba, ta katse kiran, ABUJA Gulma na cin Muhammad, sai da ya zo gidansu Ma'aruf ya gayawa Hajiya abinda idanunsa suka gane masa, tabbas daga Hajiya har anty Jamila babu wanda yaji daɗin labarin, sai dai sun ɗauki alwashin binciko gaskiyar lamari tunda har abin ya kasance haka, Yau kwana uku kenan basu sanyashi a idanunsu ba, sai safiyar yau ya shigo musu, yayi shirin zuwa office, bayan ya gaishe da Hajiya ya gaida anty Jamila kafin ya miƙe zai fice, anty Jamila tace "Son ina san yin magana dakai" "Anty Please ki bari idan na dawo sai in zo muyi maganar" Ya faɗa yana fara tafiya, Dakatar dashi tayi cikin bashi umarni kafin tace "son ka nemi guri ka zauna" Dole ya zauna sboda yana girmama anty jamila sosai da sosai, Ta fara magana... "Ka sani Hajiya ta riga da ta zaɓa maka matar aure, nan bada jimawa ba, za'ayi bikinku" Anty Jamila na gama magana yace "nidai inada wacce nakeso wlhi gara in aureta da in auri waccer village girl ɗin" Buɗar bakin Hajiya tace "Jamila barshi ya auri wacce yakeso, ita kuma Aysha Allah ya fito mata da miji na gari wanda ya fishi" anty jamila bataji daɗin, hukuncin da Hajiyar ta yanke ba, sai dai tasan cikin fushi ta yanke hukuncin, ransa fess ya miƙe yabar gidan. Yana fita anty jamila tace "Hajiya mai yasa zaki yanke wannan hukuncin, bayan kina ƙoƙarin cika alƙawari?" Hajiya ta sauke ajiyar zuciya kafin tace "Jamila tun ranar da Tasneem ta kirani tacemin Aysha ta kusa dawowa, nayi wani nazari, ina tunanin kar Aysha ta dawo ta samu labarin haɗin da zamuyi mata da ɗanmu taga kamar munso kanmu ne, kokuma da wata manufa muka ɗaukota, sannan duk ba wannan ba, Ma'aruf ba mutum mai sauƙin kai bane, idan har yace baya son abu, ko anyi masa baza'a zauna lafiya ba, Jamila bazan amince ya cutar da yarinyar nan ba, kawai dai abinda na gani shine, idan ta dawo a kaita makarantar kwana, tunda tayi ilimi sosai, sboda tanada basira, insha Allah bazamu sami matsala ba, kinga kafin nan ta sake girma sai mu jira Ubangiji ya fito mata da miji na gari" Har yanzu dai anty jamila bataji daɗin maganar hajiyar ba, dole ta amsa da Amin tunda tana gaba da ita. Acan company soyayya ce mai ƙarfi ta ƙullu a tsakanin Ma'aruf da Layl, ta samu abinda take so, ga shi duk abinda ta tambayeshi sai yayi ƙoƙarin yi mata, hakan ya fara bawa mutane mamaki, shi da kwata-kwata baya soyayya, bikin Muhammad ya rage saura kwana biyu, yayi musu anko iri ɗaya shi da ita na shadda mai tsadar gaske,  duk wasu kayan ƙyale ƙyale wanda zata saka a ranar bikin, hidima yayi mata sosai, kai kace itace amaryar, Ga shi yanzu bai cika zama a office ba, daga suyi nan sai suyi can yayita biye mata, sai da aka zauna meeting ma'aikata sukayi ta ƙorafi, tabbas bashi da bakin magana, dole ya karɓi laifinsa tunda har sun fara yi masa barazanar company ya fara samun matsala. Cikin amincewar Ubangiji, sai ga su Aysha a cikin garin Abuja, hamdala tayi tare da sauke ajiyar zuciya, dambun naman da anty Tasneem tayi mata har ta kusa cinyewa a hanya, ragowar ta bawa driver, horn yayi a bakin get na gidan, mai gadi ya leƙo dan yaga waye, kana ya buɗe musu, bayan driver yai parking kafin ya kashe motar ta fito da gudu kai tsaye ta nufi cikin gidan, tana cewa "Hajiya anty Jamila..." Aiko suka fito da sauri, fuskokinsu cike da murmishin ganinta, sai mamakin girmanta sukeyi, ga shi tayi jajir, dama ita ɗin fara ce sai ta sake gogewa sosai, anty jamila tace "ai na ɗauka jirgi kika biyo" Aysha tayi murmishi kafin tace "driver yana can ma gurin parking suna gaisawa da mai gadi" Hajiya tayiwa Hajjo magana akan ta kai masa abinci, daga nan suka zauna aka fara hirar yaushe gamo, Kana ganinsu kasan suna cikin farin ciki, "ga shi kinzo a daidai, gobe bikin Muhammad" Anty Jamila tai maganar tana kallon Aysha, Aysha tace "anty waye Muhammad?" Hajiya tace "abokin yayanki Ma'aruf mana" Murmishi tayi, kafin tace "taɓɓ ni nama mance da shi tunda rabona da ganinsa tun lokacin da na cijeshi" Suka kwashe da dariya, tana cewa "ai yanzu na girma. Ƙarfe huɗu, ashe driver yayi gudu sosai, Aysha ta faɗa tana miƙewa zuwa yin alwalah, Bayan tayi alwalah tayi sallolinta kana ta dawo parlor, lokacin an shigo da kayanta, tace Hajjo ta shigar mata dasu ciki, sallama sukaji na muryoyi biyu, Ma'aruf da Layla, Hajiya da anty Jamila suka amsa tare da kallon ƙofa dan ganin shi da waye, a tare suka shigo, Laylan tayi kyau  babu laifi, ta sanya leshi coffee brown ya haskata sosai, tasa mayafi milk color tasa sarƙa da warwaro da agogon hannu, suka ƙara so ciki, Hajiya ta bata guri, suka zauna, ita da Ma'aruf ɗin nesa da juna, cike da kunya ta gaishe su suka amsa, Aysha kam ta ganeshi sarai, baya birgeta saboda bata taɓa tsayawa tayi masa kallon nutsuwa ba, shi kuma ya mance da ita, tunda kamanninta na da ya ɓace sosai, tayi haske tayi ƙiba ta cika sosai, kai kace ba ƴar 14yrs ba, "tace antynmu kinzo lafiya" cike da jin kunya Layla tace "lafiya lau" Aysha na dariya tace "ki riƙe mana yayanmu gam gam please, karki wasa fa" tana maganar ne tana dariya, daga Hajiya har anty Jamila babu wanda yayi ko da murmishi, har Ma'aruf ɗin ya lura da hakan, ya tashi yace zasu wuce, su Hajiya sukayi musu Allah ya kiyaye hanya, Aysha ma tace a gai da gida. Kafin su mai ga fita daga gidan, Layla ta kwaɓe fuska tare da cewa "my hero sai naga kamar momynka bata farinciki dani?" Ya ɗage kafaɗa gami da cewa "no karki damu, dani takeyi ba dake ba, gaskiya ko me za'ayi bazan iya rabuwa dake ba Layla" yai maganar cikin ƙarfafa mata guwaiwa, dama abinda take son ji kenan daga bakinsa, hakan yasa tayi murmishi mai kyau suka fice. Suna fita Hajiya ta taɓe baki, kafin tace "hmm ayi dai mu gani" anty Jamila ta kasa ɓoye ɓacin ranta tace "wlhi tallahi kwata-kwata yarinyar nan bata kwanta min ba, yake wani rawar ƙafa a kanta" Aysha tace "oh Allah Wlhi ga ta ƴar kyakkwa, zan dinga zuwa ina tayata aiki" Anty Jamila ta kalleta kallo mai cike da ma'anoni masu yawa, kafin ta kawar da idonta a kanta. Wunin ranar dai komai beyi musu daɗi ba, yau gashi sun ganewa idanunsu dama Muhammad ya faɗa, tabbas beyi ƙarya ba" Lokacin da Hajiya ta shiga ciki, Aysha ta wuce ɗakinta, dan ta gyaggyara kayanta, sai da ta rufe ƙofa kafin ta kunna wayarta da ta kashe, number Zyd ta kira, yana ɗagawa tayi masa murmishi mai sauti, tare da cewa "na isa gida cikin ƙoshin lafiya" "Beautyna wlhi NA KASA JURE rashin ganin kyakkyawar fuskarki" Ta katse shi da cewa "ai Kanada hotona" "Uhm na gaji da kallon hoto, kawai na yanke shawarar zuwa Abuja a satinnan zaki ganni, ko baki gayamin inda gidanku yake ba, tabbas zan bincika kuma zan gano, kawai ki tsumayi zuwana, wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa "dan Allah ka rufa min asiri..." Hhh more comment more typing Mom Islam ce 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋                     _Mom Islam🍹_ _Zakuga na canza tsarin page, kokuma wasu suce yashe akayi nisa haka basu sani ba, ada inayin mai page1 yanzu kuma nayi editing ɗin pages ɗin ya zamo mai 1-2 kin gane?_       Page 69-70 "Beautyna ban fahimceki ba?" Tayi shiru tana nazarin maganarsa, Murya a sanyaye yace "beautyna ina ganin kamar bakya sona shiyasa kike yimin rowar ganin kyakkyawar fuskarki?" "Zayd yayi maganar yana jiran amsarta, A shwagoɓe tace "kaima kasan ina sonka, amma ai na gaya maka idan har kazo Abuja akwai matsala sosai, saboda su Hajiya, zan iya fuskantar ɓacin rai, nikuma bana son abinda zai ɓata musu rai" Sosai ya fahimceta, wannan ma gwaji ne, yanason ya daɗa jaddada soyayyarsa a gareta, sai da ya tabbatar da ta nutsu bata cikin fargabar da ya sa ta, sannan yayi mata sallama. JOS Kwanan Alhaji Abdullahi 3 da rasuwa, anty Asabe tace "kowa ya watse" dole suka tattara suka tafi, dangin Hajiya Salima, ya rage saura anty Asabe da Hajiya Salima, sosai Hajiya Salima ta kama kanta, saboda bata shiga shirginta, dan ɗaki ta kama musamman ta dawo gidan da zama, ɗakin ma na Alhaji Abdullahi, bayan kwana Bakwai da rasuwarsa, washe garin ranar, da safe, ta kira Hajiya Salima zuwa parlon ƙasa, bayan tazo sun gaisa tace "Salima ya kamata ki tattara kisan inda dare yayi miki, saboda baki da gadon Alhaji, sai tumunin takaba, tunda dai ba ƴaƴa ne dake ba" Sosai maganar anty Asabe ta bawa Hajiya Salima mamaki, sai ta basar tare da cewa "naji tumunin takaba ne nawa, amma ai yarana sunada gadon mahaifinsu" Anty Asabe ta taɓe baki, kana tace "ina yaran naki suke?, tun da suka tafi yawon duniya basu waiwayi ubansu ba, kinga kuwa idan har suka ji labari tabbas zasu ci gaba da sheƙe ayarsu, kinga kuwa basu da gado tunda ma, babu wanda ya tabbatar da suna raye ne kokuma suna mace?" Rai a ɓace Hajiya Salima tace "au haka kikace?, wallhi tallahi Anty Asabe san duniya zai kaiki ya baro ki" Anty Asabe ta dafe ƙirji tare da cewa "ni kike gayawa haka?, tabbas kin samu guri, amma ai abinda kike taƙama dashi babu shi a duniya, sai ki tattara ko fice dan wlhi idan baki fita ba, tsaf zansa a fitar dake.." "Ba sai kinsa an fitar dani ba, anty Asabe, gidan duniya sai bana lahira ba, ki kwantar da hankalinki, zan yi takaba a gidanmu, amma ki sani wlhi sai na karɓarwa yarana gadonsu.." Hajiya Salima tai maganar tana wucewa upstairs da sauri ta dinga hayewa idanunta cike da hawaye, har ɗaki ta bita, dan taga me dame zata ɗiba, ta fara ɓalle gado kenan anty Asabe tace "ai naga dai babu wani abu da kika zo dashi daga gidanku, dan haka kawai ki kwashi iya kayan sawa ki fice..." Hajiya Salima ta rufe ido tare da cewa "wallhi kibar gani ina ɗaga miki ƙafa, na rantse da Allah sai na tafi dasu harda kujerun parlor, idan ba haka ba, zaki jiki a kotu, tunda har takardar duk wani kaya da marigayi ya siya min mukeyi, idan kuma kina musu ki jirani " Anty Asabe tace "to naji yi maza ki kwashe amma dai wannan gidan ya haramta a gareki wlhi" tai maganar tana nunata da yatsa. Ba wani lokaci mai tsawo ta ɗauka ba, gurin tattara kayan nata guri ɗaya, sannan ta fito parlor ta samu anty Asabe tace mata, "Allah ya haɗa kowa da alkairi" "Amin" tace tana Bin ta da kallon banza, Hajiya Salima na fita, anty Asabe ta kulle ko ina na gidan, kana ta wuce kai tsaye ɗakin Alhajin ta fara bincike, sai dai ga mamakinta, babu ko sisi a ɗakin, hankali a tashe taci gaba da bincike amma shiru, har jakar kayansa ta zazzage babu komai, tunani ta farayi, na.. "Kuɗaɗen da yake bawa mutane masu zuwa neman alfarma a ina yake ajiye su oho?" Ta zauna tayi jugum abin duniya ya isheta, ta fara tunanin a ina wayar marigayin take, ko wannan munafukar ta ɗauka ne?, Da sauri ta buɗe ƙofar bedroom ɗin nasa, kana ta fito parlor ta buɗe ƙofar sannan ta fito harabar gidan tana ƙwalawa ma'aikatan gidan kira, mai gadi ne ya fito daga ɗakinsa, kana yace "Hajiya gani" Anty Asabe tace "dan Allah ga wayata ka kirawo min lambar Alhajin gidannan, nikuma zan shiga ciki inji ko wayar tana ringing, kasan muna zargin kamar an saci wayar ne" "To" kawai yace mata, Ko da wayar ta fara ringing ta ruga da gudu zuwa cikin gidan, aiko tana shiga ta jiyo ringing ɗin wayar, hamdala tayi tare da sauke ajiyar zuciya, a fili tace "hmm da ace wannan shegiyar ta ɗauki wayar nan, na rantse da Allah da ta cutar dani" Ta dawo gurin mai gadi tace masa ta gode, Ta koma bedroom ɗin nasa, ta fara binciken inda wayar take. Hamdala tayi, saboda taga wayar a cikin bedsite, Kwananta biyu a gidan, tayi abinda ranta yakeso babu wanda ya shigo bare ya sani," A rana ta uku aka kira wayar Alhajin, da gudu ta fito harabar gidan ko nauyin tsufan da ta farayi bata ji, ta fara ƙwalawa driver kira, yazo da sauri yace mata "gani" "Yauwa amsa min kiran nan, ɗazu sai na ji kamar Larabci sukeyi" "Driver yace "Hajiya da dai Turanci ne, Larabci kam ban iya ba" mai gadi da ya jiyo maganar da sukeyi, yace "yanaji" Aka miƙa masa wayar, bayan sun gaisa da wanda ya kira da Larabci, sukaga mai gadi ya zaro idanu yana jujuya hannaye, Allah -Allah, anty Asabe take yi ya gama waya ya gaya mata abinda wannan Balaraben yake cewa, Sun jima suna zuba Larabci a tsakanin mai gadi da wancan Balaraben da yace daga ƙasar Egypt yake, sannan yace ta WhatsApp zai sake turo saƙon dan su tabbatar da gaskiyar magana" Suna gama waya, mai gadi yace "Hajiya ki zauna inyi miki bayani" Anty Asabe tace "kaga ni gayamin koma Meye, idan maganar akawin ne sai a tura musu ina dashi" Mai gadi ya girgiza kai tare da cewa "Hajiya da dai kin zauna inyi miki bayani dalla-dalla" Sai da taja tsaki mtswww kafin ta zauna tace "ina jinka" Sai da ya sauke gauron numfashi kafin yace "Hajiya mutumin nan yana bayani ne akan bashin da ake bin Alhaji, kimanin biliyan goma" lokaci ɗaya zufa ya fara yanko mata, ta fara fifita da hannu, tare da cewa "kashemin wayar nagode, ta shige ciki da sauri, ƙara gudun fanka tayi, ga kuma sanyin AC, amma duk da haka ji take kamar an tsoma ta a cikin ruwan zafi. Acan gidansu Hajiya Salima, mama na ganinta batayi mamaki ba, saboda tasan wacece Amru asabe, kasancewar a tsakar gida ta samu maman, ta ɗauko kujera zata zauna, mama tace "Salima kina takaba bai kamata ki zauna anan ba, suka shiga ciki, Hajiya Salima ta kwashe duk labarin ƙalubalen da ta fuskanta, har musayar yawu da sukayi da anty Asabe, mama tace "mai yasa ta kulata, karta sake duniya ai ba'a yi mata garaje, Hajiya Salima tace "mama waɗannan ƙudaɗen da kike gani, sune a mazaunin dukiyar yarana, saboda Alhaji ya mallaki gidaje sunkai hamsin da filaye, sannan yana da wani Company ma a ƙasar waje, kinga kuwa babu wanda ya isa yace komai akai inhar ba  kotu zamu kai ta ba". Mama ta dakatar da ita, tare da cewa "kotu da kikace, babu inda za'a kaita, ki fita batun matar nan, waɗannan kuɗaɗe kuma kiyi shawarar abinda zai amfaneku keda yaranki, shikuma Allah ya gafarta masa" Hajiya Salima ta amsa da cewa "Amin" washe gari aka dinga zuwa ta'aziyya maza da mata manya da yara, kasancewar Hajiya Salima ta kowa da kowa ce, bata da duhun kai mace ce mai hankali da mayar da kowa nata... KEFFI Rabonsu da ganin anty Hadiza har sun mance, sabda takai kwana biyar, wayarta bata shiga ko sun kira, Salma taje gidanta ance wai tayi tafiya, abin ya bawa Hajiya Zaliha mamaki, anty Hadiza tayi tafiya ba tare da ta sanar mata ba, yanzu ita ya zatayi?, Can gidan Saudart kuwa, a yau ne jirginsu zai tashi zuwa SINGAPORE daga nan kuma zasu wuce Saudiyya suyi Umrah tunda azumi saura kwana biyar, a safiyar yau ne ta mayar da simcard ɗinta kafin su wuce, ta kirawo momy ta sanar mata da cewar zasu je SINGAPORE daga nan zasu wuce Saudiyya, momy tace "me zaki yi a SINGAPORE? Saudart tace "kawai zamuje hutawa ne" Momyn bata sake magana ba, sai dai tayi mata faɗa sosai akan kashe wayarta da take yi, sannan tace su dinga magana ta WhatsApp, sannan mommy ya ɗauki alwashin bazata sanarwa da Dady ga inda su Saudart sukaje ba, idan ba haka ba akwai babbar matsala. Duk wasu abubuwa da zata buƙata ta shiryasu cikin wani kyakkyawan akwati, daga nan suka wuce airport driver ya dawo da motar, daga nan jirginsu ya ɗaga sai SINGAPORE. Tunda suka sauka a airport, take ta rarraba idanu, duk da ƙasar waje na baƙon gurin zuwanta bane, amma guraren da suke wucewa ya birgeta sosai, Mota suka shiga wacce ta kawosu, har Naumi hotel Singapore, bayan sunje reception ya gama duk wasu abubuwa da zasu buƙata, aka basu ɗaki, mai kyau sosai, kai kace gidane guda, saboda ɗakin 3bedroom ne, ga kitchen da guraren hutawa a ciki, sosai duniyar ta zame mata tamkar sabuwa, saboda ko makarantar da tayi a Singapore bata taɓa yawace yawace ba, "Habibty da fatan dai ɗakin ya yi miki?" Gyaɗa masa kai tayi tare da lumshe idanunta, wani irin sanyin ƙamshi na ratsata, sai taji yanayin gurin ya birgeta, Ajiye keys da wayoyinsa yayi, kana yace "Habibty zan watsa ruwa" "Tasan mai yake nufi dan haka ta yi lamo a lallausan gadon, tare da rufe idanu kamar mai yin barci, murmishi yayi Sannan ya matso kusa da ita, kafin ya fara cire mata, ɗan ƙaramin baby hijab ɗin dake wuyanta, a hankali ya ɗan mirgina ta duk tana jinsa, ya zuge mata zip na abayar dake jikinta, kasancewar zip ɗin yana a gaba ne, tana kwancen ya rabata da komai ma jikinta ya kasance daga ita sai vest da underwear, ko bra bata saka ba, ya Subhanallah "na shanunta sun mugun tsole masa idanu, kamar mai jin tsoro, ko kuma wani zai ƙamashi, ya kai hannunsa a hankali ya shafi na shanunta, kafin ya wani sauke ajiyar zuciya, tabbas tayi barci, cike da kallon tausayi ya bita, a fili ya ce "ta gaji sosai" Ya gyara mata kwanciya, tare da jan blanket ya lulluɓeta, ya ci gaba da kallonta cikin so da ƙauna, shikam har ga Allah ya sonta so mai tsanani, A dole yaje yayi wankan shi kaɗai, kana ya fito yana sanye da Bathroom, tsayawa yayi yana kallon mirror, yana tsaye a gaban mirror ɗin, wayarsa da ya kunna kafin shigarsa wanka ta fara ringing, number Hajiya Zaliha ya gani tana yawo a kan screen ɗin wayar, sbda tanada numbers ta waje, amsa wa yayi tare da cewa "Aslmu alaikum" "Ba sallama nace kayimin ba, so nakeyi ka gayamin a wane matsayi na ajiyeni? matar aure kokuma free wife?..! Rashin comments yasa banayi yi muku posting mai yawa, idan kun cigaba da comments nima zan gyara... Mom Islam ce 08141799224 [7/12, 2:34 PM] Mom Islam: *NA KASA JUREWA* 🪻🪻🪻 Mom Islam Masu Arewabook ayi haƙuri anjima zanyi muku posting page 11&12 Please masu nema daga farko kuyi following channel ɗina ga link nan👇 https://whatsapp.com/channel/0029VbBCPdgEawdlPZsXnp3t Domin samun more pages kuyi following ɗina a Arewabook danna blue link👇 https://arewabooks.com/u/momislam11 Ga wanda basa Arewabook ga link na Wattpad hilis ayi following ɗina 👇 https://www.wattpad.com/user/Momislam2021?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends Page 9-10 Cikin isa da jiji da kai ya furzar da isa mai huci kana yace "me kike nufi?, ba dan an takura min ba me zan ci dake?, kinga ni sauƙi ma kika nema min kije na sakeki saki uku" Kafar a kunnen Hajiya mama dake ta kwaɗa sallama tun daga parlo bataji motsin kowa ba, a take a gurin ta faɗi sumammiya, cikin azama Saudart ta taho da gudu zata taimaka mata, yai saurin dakatar da ita gami da cewa "idan har kika taɓa ta wallahi sai na illata ki" Ko da jin haka ta miƙe zuciyarta fess dan har ta fara jin tausayin Hajiya, tunda ya gaya mata magana tayi ta kanta, cikin farinciki da samun ƙwarin gwaiwa ta harhaɗa komai nata, kuɗin da Anam ta turo mata ta sake dubawa, a fili ta tace "hmm wallahi bazan sanarwa kowa maganar sakin nan ba, amma fa dole in nemo sheda kodan kar Dady yace min ƙarya nakeyi. Biro da takarda ta ɗauka zuciyarta fess ta wuce ɗakinsa, a bakin ƙofa ta sameshi yana yayyafawa, Hajiya ruwan sanyi, tace "yaya nazo ka rubuta min shedar saki" Babu musu ya karɓa saboda har ga Allah ta zame masa tamkar gobara, duk da tashin hankalin da yake ciki na suman Hajiya be hanashi rubuta mata saki ba, ya miƙa mata tare da cewa "kafin inje asibiti in dawo kar in sameki anan" "Ai bazaka sameni ba, yanzu kam meye haɗinka dani, Allah yabi bayan me gaskiya" ta faɗa tana wucewa abin ta, Ko saurar ta beyi ba ya kin kimi Hajiya zuwa parking space yana ƙwalawa Idi mai gadi kira, da gudu Idi ya taho yana cewa "lafiya kuwa alhjaji?" "Dalla can buɗe min get, lafiya ne zan dinga yi maka wannan kiran?" Jikin Idi na rawa yai azamar zuwa buɗe masa get sbda yasan halin uban gidan nasa. A guje ya fice daga gidan kamar wanda zai tashi sama, cikin ransa ya dinga mai-maita innalillahi wa inna ilahir raji'un, har suka iso (Mai tama District Hospital) Emergency room aka wuce da ita, inda aka bata taimakon gaggawa, Duk wanda ya kalli fuskar Ma'aruf ko ba'a gaya masa ba yasan yana cikin matsanancin tashin hankali, adu'arsa bata wuce Allah yasa babu abinda ya sami hajiyarsa ba, idan kuma ta kamu da wani ciwon ta sanadinsa fa?" Gaskiya bazai yafewa kansa ba. Duk wani likita me shige da fice a ɗakin da aka kwantar da Hajiya, sai ya bishi yana cewa "likita dan Allah ya farfaɗo? likita tana magana?, Inda kasan zautacce haka ya koma, wayarta dake hannunsa ya kalla, a sanadin faɗuwarta, duk ta farfashe, ya kawar da kallon wayar da yake sakamakon rurin da wayar ta farayi, Sunan Anty Jamila ya gani yana yawo a fuskar wayar, sosai gabansa ya bada rass, lokaci ɗaya zufa ya fara karyo masa, be san amsar da ze bata ba, ƙarfin hali yayi ya ɗaga a ɗarare yace "As...asalamu a.." "A'a Ma'aruf yakuke ina Hajiyar?" Shiru yayi bai bata amsa ba, jin shirun yayi yawa, ta katse kiran ta sake kira, dolensa ya ɗaga, duk girman kansa da jan ajinsa baya yiwa mutum biyu, idan ka cire mahaifinsa da ya rasu, wato Hajiyarsa da Anty Jamila ƙanwarta kenan. "Kayi magana mana, wai meke faruwa ne Ma'aruf?" "Hajiya na hospital" Kalmar da ya iya gaya mata kenan ya katse kiran. Sosai hankalinta in yayi dubu ya tashi, ta fara harhaɗa kaya, ƘAUYE Ko da aka tashi daga islamiyya kowa ya watse amma Talatu bata matsa ko nan da can ba, sbda tun kafin a tashe su malamin ya fita, anyi masa kiran gaggawa, ɗaya daga cikin manyan ɗaliban ne ya yi musu addu'a kowa ya watse, har lungu Talatu taja wuyan hijabin Gudidi, mutane biyu ne a biye dasu, ɗaya sahura ce ƙawar Gudidi, ɗayar kuma Lantana sunanta ƙawar Talatu, Rawa suke tiƙa sunayi musu waƙa suna cewa ... "🎺A casu mata a casu, ku casu ba me rabaku araba ace anyi cuta, a zamanin nan na yanzu" Sosai suke tiƙar rawa, kan kace me har Talatu tayiwa Gudidi lilis, babu mataimaki sai Allah, duk su biyun ƙawayen nasu basu isa suja da ƙarfin Talatu ba, sosai ta haɗawa Gudidi jini da majina, kafin faɗan ya ƙare, Gudidi na tafiya tana ɗingishi, tace "Hegiya maiyya jaka me ƙarfin Allatsine me kai kamar na duwatsun murhu" Talatu ta biyota da gudu, itama gudun takeyi tana ɗingishi har ta ƙarisa gidansu, Tana shiga ta samu Tabaiyye da malam sai uban musayar yawu suke yi, ita kuma ta shigo tana kuka babu wanda ya saurareta, Wucewa tayi ɗakin Tabaiyyen ta kwanta a ƙasa ko zataji sassaucin mutsikar da tasha gurin Talatu. Malam ya gyara zaman babbar rigarsa kana yace "Wallahi wannan hine gargaɗi na ƙarhe idan kika sake ragemin hatsi kowa ze kama gabansa" Cikin masifa Tabaiyye tace "yo in kama gaban nawa mana, ka gayamin me na tsinana tunda na aureka, kaf kiwon da iyayena suka haɗoni dashi sun ƙare, me kake dashi da zan ɗin ga ɗiba? ta gyara ɗaurin zaninta taci gaba da cewa "ko yanzu na fita a gidanka zan samu saurayi sabo fil gada gau me jini a jika" Tun da ya ji ta faɗi haka, ya wuce ƙofar ɗakinsa kana ya ɗauki buta ya kuskure bakinsa, har ya nufi hanyar zaure ya juyo yace "Tabaiyye kiji ta tsoron Allah karki ragemin masara" "Da tsoronka nakeji mtsw" Tai maganar tana yatsina masa fuska. Hankali kwance Talatu ke tafiya har ta iso gida, tunowa da babbar baƙuwar da Inna ta gaya mata zasuyi ne yasa ta washe haƙora, a fili tace "na rantse da Allah ina son ganin ƴan binne" da gudu ta shige tana cewa "Inna dan Allah ki biyoni ban ɗaki da buta tsuuuuu (Gudawa) nakeyi" Sam bata ma ga Anty Jamila dake zaune saman tabarma ba, cikin ɗaga murya Inna tace "Talatu zanci mutuncin ki", tana ƙare maganar ta miƙe takai mata buta, "Yauwa Innata idan nai aure zanyi kewarki" Ko ƙala Inna batace mata ba ta dawo gurin Anty Jamila. Murmishi Anty Jamila tayi kafin tace "wallahi A'isha tana birgini" Inna tace "taɓɓ bakisan waye A'isha bane" "Haba Inna ai Kowane yaro da ƙuruciyarsa" "Hakane kam" Inna ta faɗa tana dariya. Bayan ta fito daga banɗaki ta ware idanunta, fess ta ɗora su kan Anty Jamila, washe jajayen haƙoranta tayi kafin ta taho da sauri tace "ahe kin ƙaraso Inna Jumai?" "Na ƙaraso A'isha, amma sau nawa zan ce miki bana son ki dinga ce min jummai?" "To kiyi hakuri yasin mancewa nakeyi, amma dai kinzo kiyi mana wata da watanni ne ko?" Anty Jamila tai dariya kana tace "a'a yanzu ma daga Madobi nake gobe insha Allah zan koma Abuja" Zaro idanu Talatu tayi sai kuma ta matso kusa da Anty Jamila tace "dan Allah ina Hajiyar nan da take zuwa tana raba mana hinkafa?" Anty Jamila tace "Hajiya tana gida, sbda rashin lafiyarta ne ma zan koma gobe" "Ahe bata da lafiya?" Talatu ta faɗa tana ƙara tattaro nutsuwarta, kai kace dagaske, Ita ko Anty Jamila duk tambayar Talatu tayi mata sai ta bata amsa. Koda Inna tazo ta samesu sunata hira, abin yai mata daɗi, Tace "Jamila kuna zantawa ne da ƴar taki?" Anty Jamila tai murmishi. Jollof ɗin dawa da wake Inna ta kawo wa Anty Jamila, ayko taci sosai ba laifi dan kaɗan ta rage tasha ruwa, Wayar Anty Jamila ta fara ringing, Ganin sunan Ma'aruf yana yawo a kan screen ɗin wayar yasa tai saurin ɗagawa, tare da cewa "my Son ya akayi?" "Anty Jamila Hajiya fa bata magana kwata-kwata" Cikin firgici Anty Jamila ta fara mai-maita "innalillahi wa inna ilahir raji'un" Kana tace "son kayi haƙuri yanzu dare ya fara tunda ana shirin kiran sallahar magriba, insha Allah gobe ƙarfe huɗu zan taho, Allah ya bata lafiya" Sosai hankalin Anty Jamila ya tashi, sanda a iya saninta Hajiya ba ta taɓa irin wannan ciwon ba. Nan ta labartawa Inna abin da ke faruwa, Inna tace "itama zata bi Anty Jamila su tafi tare" Talatu tace "taɓɓ wallahi he anje dani kawai ki tafi har binni ki barni hu'um" "Ba fa wani abin daɗi ne ze kaini can ba, rashin lafiya ne, kuma befi in ɗauki kaya kala ɗaya ba" Da ƙyar da lallashi dan sai da Anty Jamila tayi mata alkawarin zata turo me mota ya kawo ta Abuja sannan ta amince, A daren Inna ta haɗa mata kayanta a bako sbda kafin su wuce zata kai ta gidan mahaifiyar babanta. Bayan sallahar isha'i, suka wuce gidan Kaka, da sallama Inna ta shiga kafin tace "zauna mana ai dai kya gaihe ta" "Ina wuni" Talatu ta faɗa tana turo baki, "lafiya lau ƙawata na ganki da jakar kaya?" Inna tace "wallahi na kawo ta ne zamu wuce Habuja gobe saboda Hajiya Habiba babu lafiya" "Ash sha, Allah ya bata lafiya, zaki daɗe ne?" "A'a kwana ɗaya zanyi" Inna taba kaka amsa, kaka tace "to ki ja mata kunne banda rahin kunya, dan ba kowa bane ze ɗauka" Sosai Inna tayiwa Talatu faɗa kana tayi musu sallama, bayan ta miƙa wa Talatu ɗari biyu taba wa kaka ɗari uku, Kaka ta washe haƙora tana cewa "Allah ya tsare, "maiyyar kuɗi" Talatu ta faɗa tana hararar kaka" "Nayi ɗin naga uwarki ce ta bani ko?" Koda taji barci kaka ta hanata hawa gado wai kar tayi mata fitsarin kwance, sai da Talatu ta bari kaka tayi barci kana ta lallaɓa ta kwanta can gefenta, Kaka dai tasan ta hana Talatu hawa gado, gashi fitila ta mutu, tunda su basa ganin wutar lantarki, cikin ihu da kururuwa take cewa "ke Talatu tahi ki gani kwarto" Tunda Talatu taji kaka ta faɗi haka, ayko ta kunce zanin kaka ta cukuai kuyeshi, ta janyo hannun kaka kiiiii ta janyo ta ƙasa, ta haye gadon daga can inda take ta sauya murya tace "ke ƴar tsohuwa jiya naji kina adu'ar Allah ya baki miji hine nazo mu shirya" Haba kaka ta sake rikicewa, bakinta na rawa tace "nifa tsohuwa ce haba kai kuwa baka ga jikina duk a tamushe ba, na roƙeka nidai ban ce haka ba" "Zo nan" Talatu ta faɗa cikin daka tsawa, ganin kaka ta rikice sosai yasa ta koma kan gadon ta kwanta tunda tasan bazata taba komawa ta kwanta acan ba. Ƙarfe huɗu na asbha Anty Jamila ta farka, dan ba wani barci me nauyi tayi ba, ko wanka batai ba, ta shirya cikin leshi Black anyi masa ado da zare golden color me adon duwatsu farare, mai kawai ta mutsika, tayi tunanin Inna tana barci sai taga itama har ta gama shiri, kasancewar basu da wani kaya me nauyi suka fita neman me mashin, sbda masu mashina ba kasafai suke yawo ba, kasancewar ƙauye ne sosai, idan kaga mashin sai na masu zuwa gona, can maƙotansu Inna taje ta roki alfarma, tai sa'a yaron gidan na nan, ya fito da mashin ɗinsa suka hau zuwa tasha, Sai da suka kai ƙarfe shida kafin motar ta cika, sannan suka fara tafiya...! Ayi haƙuri jiya baku ga posting ba, wallahi kuna raina kunsan weekend mutum ba shi da wani hutu sosai. Share fisabilillah 👏 Mom Islam ce 08141799224 [7/16, 8:21 PM] Mom Islam: *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam🍹_ Kiyi following ɗina Arewabook zaki samu more pages ga link nan 👇 https://arewabooks.com/u/momislam11 Page 71-72 Ranar suna yarinya taci sunan mahaifiyar Yaseen, duk cika bakin da ya dinga yi akan bazai barta taje wankan gida ba, yasha ruwa, saboda daga Hospital gidan Momcy aka wuce da ita, dole ya ƙulla ƙawance da zirga-zirgar zuwa gidan Momcy kullum, kaka ce take yi mata wankan jego, Sati biyu Yusra ta samu a gidan Momcy, tayi kyau tayi ƙiba sosai, ita da yarinyarta da suke kira da Mirah, sosai mimrah take kama da Yusra har ɗan ƙaramin bakin, Yauma kamar kullum, koda ya je can gidansu sai ya ga gidan yayi masa girma sosai, acan gidan Momcy yake cin abincin dare kullum, Ƙarfe 7:pm ya kama hanyar zuwa gidan Momcy, ga wani uban hadari dake haɗawa, hakan bai sa ya fasa ci gaba da driving ba, horn yayi a bakin get ɗin mai gadi ya buɗe masa, ya shigar da motarsa, a lokacin har an fara yayyafi, da sauri ya shige gidan tare da kutsa kai cikin parlorn, babu kowa a parlor dukansu suna ɗarin Momcy hakan yasa shikam kai tsaye ya wuce ɗakin Yursa, wayarsa ya ciro tare da danna numberta ya kirata, kasancewar wayar a vibrat take, ta ɗago kai a hankali kafin ta kalli kaka, sai kuma ta kalli Momcy da ita take kallo, cikin ɗan duburburcewa tace "am..dama...um.." Momcy tace "Yaseen ne yazo ko?" Ta ɗanyi murmishin yaƙe tare da cewa "uhm Momcy ya akayi kika gane?" "Kinga tashi kije, wlhi idan har kika biye masa yayi miki daɗin baki ke kika sani, dan ɓatan watanki ya ɗauke ba shi ke nufin ki koma ga mijinki ba, ah to, wallhi ina nan babu ruwana," Kaka ta faɗa tana bin ta da kallo, sake ɗago idanu tayi ta kalli Momcy, Momcy tace "tashi kije amma fa ki kula" Har ta fito bakin ƙofa, Momcy ta ƙwala mata kira ta dawo, "zo ki ɗauki ƴarki" Momcy ta miƙa mata mimrah, Bayan ta karɓeta ta fice a ɗakin kai tsaye ta wuce ɗakin ta, A saman sallahya ta samesa yana ta kwararo adu'oi, bayan ya shafa, ya miƙe yana ninke sallahyar yana yiwa mimrah murmishi, kafin ya matsa inda Yusra take tsaye, ya buɗe hannayensa, ta matso ya rungumesu, tare da cusa kansa cikin jikin Yusra, a wani irin yanayi ya tsinci kansa, wanda yasan idan har bai samu abinda yake so ba, komai yana iya faruwa, sauke wani irin numfashi yayi, tare da zame jiki sa a na Yusra, in Cold voice yace "my life wlhi NA KASA JUREWA, yanzu shikenan an shiga tsakanina dake har sai nan da sati biyu?" Yai maganar murya a sanyaye, Ɗan murmishi tayi, kafin tace "sati Uku dai" ya runtse idanunsa, tabbas tasan abinda yake damunsa, saboda har Hospital sunje watannin baya da suka wuce, hakan yasa take ƙoƙari gurin ganin ta kiyaye dokokin da aka gindaya musu, domin ya zauna cikin ƙoshin lafiya, Cike da kallon tausayi ta bishi, tare da ajiye mimrah da tayi barci tun bayan da ya rungumesu a saman bed, kafin ta matso kusa dashi tace "Qalbi" Lumshe idanunsa yayi yayinda ta ƙaraso garesa, sannan ya ji faɗar sunan da tayi ya sake saukar masa da kasala, saboda cikin sanyin muryarta da take hargitsa tunaninsa tayi maganar, janyota yayi jikinsa, kana ya rungumeta ya sake sauke numfashi, kafin ya zame ɗankwalin dake kanta, "Qalbi bamu da time wlhi su Momcy zasu gane" muryarsa tayi wani irin lokacin da yake ce mata, "yanzu ni da matata ta sunnah sai anyi min iyaka, gaskiya zanzo in ɗaukeki mu gudu" Tai saurin toshe masa baki, tare da taimaka masa ya samu nutsuwa sosai.. A hankali ya ke sauke numfashi mai cike da nishaɗi, hatta mood na fuskarsa ya sauya, kana ganinsa kasan ya samu nutsuwa sosai, Ya rungumeta yana saka mata albarka, da sauri ta miƙe taje tayi wanka, kana ta tsane jikinta sannan ta dawo gurinsa tace "Qalbi.." ya amsa mata da idanu kamar na mai jin barci, yace "wannan sunan yana yimin daɗi" Ta yi masa murmishi tare da cewa "yanzu dai duk ba wannan ba, ka tashi ka sa kaya ka wuce wlhi zaka janyo min faɗa a gurin Momcy" Dole hakan yayi, bayan ya kintsa, ya sa hula ya miƙe tsaye, ta wangale baki tace "wlhi kayanka sun yamutse ya zamuyi?" Ya ɗage ƙafaɗa kana yace "karki damu, da ace ban samu honey milk ba, da ni kaina sai na zarce kayan gurin yamutsewa amma yanzu normal babu abinda ya dameni" Tsayawa kallonsa kawai tayi, a fili tace "wato ma babu abinda ya dameka ko? baka san idan an aihu ba'a zuwa gurin miji sai anyi arba'in ba?, shikenan Qalbi ka sake yimin wani cikin" ta faɗa tana rushewa da kuka, "calm down haba wane ciki kuma, saboda shigar cikin babu wahala? Kinga ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru, ni bari in wuce, me kuke buƙata sai inyi miki transfer?" "Zamuyi waya" ta bashi amsa tana share hawayen dake Zarya a kumatunta.. KD Sosai take gudu har ta fita daga anguwarsu, kafin hankalinta ya kwanta, wayarta dake hannunta, ta kunna da tuni ta kasheta, hankalinta ya gushe tunaninta ya ƙare, ta rasa wa zata kirawo, kai tsaye ta saka number Sabeer, saboda ɗazu ta gogeta kuma ta haddace number a kanta, yana kwance inda ta barshi, yana kwasar barcinsa, gefensa wani glass cup ne mai ɗauke da wine a ciki, da alamu yasha ya bugu saboda wannan barcin nasa kamar ba na lafiya ba, ringing ɗin wayarsa ce ta tashesa, idanu a lumshe da ƙyar yake buɗesu ya ɗaga kiran tare da cewa yaaaa..akaaaayiiii...neeee.., murya dai sak ta mashayi, tana kuka game da toshe bakinta tace "Sabeer kaga abinda ka janyo min ko? Ga shi nan momy ta ce, sai ta kasheni " Da sauri ya tashi zaune tare da ware idanunsa kana yace "akan me zata kasheki, tasan hukuncin wanda yayi kisa kuwa?" Cikin daka tsawa tace "ni dallah rufemin baki, ba duk kai ka jawo ba, na biyewa daɗin baki da kuɗinka, ga shi yanzu ina ɗauke da juna biyu "kai haba, ya faɗa yana washe haƙora" dogon tsaki tayi "mtswww" sannan tace "au na ga kamar murna kakeyi?" Ransa fess yace "nikam karki zubar min da ciki, ai ba shege bane da ubansa gani, ko a ina zan amsa ni ne ubansa" Ta zaro ido saboda lamarin Sabeer ya fara bata tsoro ya daina bata mamaki, "Kawai kizo mu haɗe zan baki gidana dake Tudun Wada karki wani damu, idan ta kasheki ai ni tayiwa asara" jin haka yasa ta ce "yanzu kana inane?" "Ina hotel ɗin da kika barni, dama wlhi ina hungry ɗin..." Ta katse kiran. Mashin ta tare ko mayafi babu a kanta, kana ganinta tayi wuji wuji saboda ta fita a kamininta na ɗazu, wasu ma sun ɗauka Cristian ce, wanda suka santa kuma suyita yi mata adu'ar shiriya, tunda dama an daɗe ana bada labarinta, mahaifiyarta ce kawai bata sani ba. Dan Allah iyaye mata mu kula, dan tayi wannan abin bai kamata, ace mahaifiyarta ta ɗauki alwashin kasheta ba, yanzu dai ga shi mai gari ya waya?, zata koma inda ake gudunta dashi, ya kamata da wani ƙwaƙwaran mataki ta ɗauka a kanta, duk da nasan tayi furucin cikin fushi ne, Allah Ubangiji ka tsare mana imaninmu ka kyautata farkonmu da ƙarshenmu ka bamu ikon riƙe amanar ƴa ƴanmu da ka bamu Amin. Bayan sun iso ta kira Sabeer, ya fito ya bawa mai mashin kuɗinsa ya wuce, Wani irin kallo yake mata wanda ya tabbatar mata da abinda ke cikin ransa, hannunta ya riƙe suka wuce room ɗin da yake, a ranar dai wuni yayi yana aikin Abu ɗaya, tabbas Ruqaiyya ta gane Allah ɗaya yake, a ranar yayi mata kyautar mota, mai kyau, sai dai bata kai tsadar tasa ba, sosai suka kasance manne da juna, kai kace yau ne rana na farko da suka taɓa haɗuwa, kokuma muce kamar wani sabon ango, siyan abinci ne kawai yake fitar dashi daga room ɗin, haka suka kasance babu sallahar azhar babu na la'asar bare na magriba da isha'i, koda dare yayi, haka ta shiga toilet ta dinga kwarara amai, cike da tausayinta ya taimaka mata har ta gama, sannan yace "akwai abinda take buƙata ne?" "Babu tace masa lokacin da take mayar da numfashi" Magunguna ya haɗo mata, tare da su peakmilk da moltina ya bata tasha ya ajiye mata na anjima dana gobe, fitar da yayi har boutique ya wuce, ya siyo mata kayayyaki masu tsada harda hijabai da takalmi, sosai soyayyarsa ta sake samun sabon mazauni a cikin zuciyarta, a ranar dai kwana sukayi farantawa junansu, can dare sosai barci ya ɗaukesu, koda aka kira sallahar asbha babu wanda yayiwa ɗan uwansa magana, basuyi ba, sai ma shiga wanka tare da sukayi suka dinga iskancinsu daga ƙarshe dai suka fito tsirara manne da juna, suka shafa mai suka saka kaya, da yake yau ne zai koma gidansa da yake zaune, suka shirya kayan su, kana suka bada key sannan suka wuce gidansa, tangamemen gidane, idan ka gansa sai ka rantse babu talauci a duniya, bayan mai gadi ya buɗe masa ya shiga, suka fito, tana sanye da dogon hijabi, bayan sun shiga cikin gidan, ta tsaya tana ƙarewa gidan kallo, saboda tunda take bata taɓa ganin gida irin wannan ba, saboda su ɗin bawai sunada hali irin sosai bane, dan kwananan ma momynta take cewa zata sallami mai gadin, tunda mahaifinta ya rasu komai sai yayi ƙasa, hakan yasa momyn ta nemi aikin gwamnati domin ta ci gaba da taimakon kansu.. Ko me ta gani sai ta ƙura masa ido kai kace makauniya, haka ta dinga kalle-kalle har ya kaita ɗakin da zata zauna, wani sassanyar ajiyar zuciya ta sauke, tare da rungumeshi tana murmishi tace "masa godiya nake" Ya zauna saman bed tare da janyota ta faɗo jikinsa, sannan yace "Ruky anan zamu ci gaba da rayuwa babu mai takura mana, sannan inson kisa a ranki ni mijinki ne, ban taɓa son wata ƴa mace ba, bayan ke, wlhi tallahi duk wayar da kikaga inayi a gabanki kawai dan in gane kinaso na ko a'a ne, karkiji shayin yimin biyayya, ko kuma tambayata wani abun da kike da buƙata.. ta amsa da "to" tana sake ƙamƙameshi. Waye Sabeer? Sabeer ɗane ga Alhaji halliru, Alhji Halliru wani attajiri ne mai kuɗi sosai, matarsa ɗaya Hajiya Zainab, ba itace mahaifiyar Sabeer ba, saboda a gidan tazo ta sameshi kuma da wayonsa, sannan tun Sabeer yana ƙarami babu wanda ya isa ya ɗaga masa yatsa, hakan yasa, ko ke shayinsa, sannan mahaifinsa ba basa zabi akan ko ina yakeson rayuwa yayi, sai dai kar ya sake yayi kwana biyu basuyi waya ba, sannan idan har bashi da kuɗi, ko nawa yakeso zai bashi" Wannan matar tasa a iya matsayinta kawai take zaune, tabbas idan har zata kawo wata magana akan Sabeer, to tabbas ranta in yayi dubu sai ya ɓaci, hakan yasa tayi haƙuri ta zauna, taƙi gani taƙi ji. Bayan tafiyar Ruqaiyya Hajiya Lubabatu ta fara numfarfashi sama-sama, wata maƙociyarta da ta shigo suyi magana akan ankon bikin ƴar matar, tazo ta sameta rai a hannun Allah, kai tsaye taje ta samu mai gidanta, ya fito da mota suka wuce Hospital....! Mom Islam *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam🍹_ Kuyi following ɗina Arewabook zaku samu more pages acan https://arewabooks.com/u/momislam11 Page 73-74 sai da suka wuni a hospital ɗin ita da matar, saboda har test akayi mata, sannan aka saka mata drip, doctor ya tabbatar musu da damuwa ta saka a ranta shine ya haifar mata da wannan ciwon, ga shi ta kamu da hawan jini, zuwa yamma aka sallameta, mijin maƙociyarta ne ya biya komai, daga nan suka dawo gida, babu abinda take yi sai kuka, hakan yasa mutane suke ta cewa ƙila ta tuna da mutuwar baban Ruqaiyya ne, shiyasa take ta kuka, Ita kaɗai tasan abinda ke damuta a cikin zuciya. KD Ƙauye Bayan sun dawo gida, malam yace "Najma ta miƙa niƙan masara ingi" suka wuce gona shi da Majeed da Haladu, malam na tafiya, cikin daka tsawa Inna tace "zoki miƙa kiƙannan dan ubanki akwai bayinki ne anan?" Najma ta miƙe jiki a sanyaye ta wuce miƙa nika, Acan a gona, zaune suke a gindin bishiyar ɗorawa Haladu da Majeed, Haladu yace "Majeed dan Allah ina neman wata alfarma a gurinka?" Majeed yayi shiru yana nazarin shi kuwa wace alfarma Haladu zai nema a gurinsa me yake dashi?" Majeed yace "Haladu insha Allah zan yi ƙoƙari gurin ganin na amsa maka tambayar da zakayimin?" "Ina son Najma.." Haladu yai maganar yana sunkuyar da kansa ƙasa, Majeed ya girgiza kai tare da cewa "Najma bata da iyaye taya zakuyi soyayya har takai ga kunyi aure?" Haladu yace "Majeed ka fahimceni, amma inason ka sani iyayena ai sun zamo iyayenku, wai dai tsaya akwai wata tambaya da nakeson yi maka, sannan inason ka bani labarin asalinka, malam dake tsaye a kansu yace "Haladu abi komai a hankali, kasani fa har yanzu ban gama yi masa magani ba, saura kwana biyu mu kammala kuma insha Allah muna saka rai da alamun nasara daga shi har ƴar uwar tashi" Majeed ya sunkuyar da kansa yana sake godewa Malam, daga nan suka ci gaba da aiki, Mai motan da suka haɗu dashi ɗazu ne ya aika yaro gidansu Karima, a kirawo masa Najma, a kwatancen da yayiwa yaron yace farar yarinya, yaro ya shigo gidan tare da cewa "wai wannan baƙuwar tazo" Inna ta yatsina baki kafin tace "kace gata nan zuwa" lokacin har ta dawo daga kai niƙan tana gida a kwance sbda barci ma take yi, Inna tasa Karima ta shirya cikin kayan sallah tare da yin kwalliya ta fito kamar wata dodanniya, ta cika janbaki ja yayi mata yawa sosai, ta fito tana rangwaɗa tare da isa gurin mai motar, yana ganinta ya tuntsure da dariya kafin yace "kwalliya tayi kyau, amma ni ba ke nake nema ba, wannan yarinyar da na ganki da ita ɗazu ita nake nema" ta turo baki tare da cewa "to ai ta koma garinsu, kuma ni kaɗai ce a gidan" ya figi mota ya wuce ba tare da ya sake yi mata magana ba. Da gudu ta shigo gidan nasu tana kuka mai sauti wanda har yasa Najma ta farka, kana ta fara sauraren dalilin kukan Karima, "uhm....um...hum... Inna wai dan nace masa tayi tafiya shine kawai ya wuce ya barni, wlhi Inna ya wulaƙantani" tai maganar tana share hawayen dake zubowa daga indanunta kamar an buɗe famfo, Sai yanzu najma ta gane abinda sukayi, murmishi tayi ko me yasa oho. Haka dai Najma taci gaba da rayuwa cikin tsngwamar Inna da kyarar da Karima take yi mata, tunda yanzu Karima ko cokali bata ɗagawa komai Najma ce take yi. Bayan kwana biyu, malam ya kawo shinkafa mudu biyar wane mudu ɗaya, yasa aka daka yaji sannan yace a dafa masa shinkafar, bayan ta dahu, malam yasa aka zuzzuba a tray kamar guda biyar, ko wanne aka saka mai da yaji, yasa aka fitarwa da almajirai abincin. Bayan abincin sadakar ya ƙare, malam yace a yau ne ya kammala aikin da yake yiwa Majeed da Najma, dan haka ya bawa Majeed wani ruwan magani yayi wanka dashi har kansa, hakama Najma yace har tsarki tayi dashi, dukkansu sunyi yadda malamin yace, bayan sun sanya kaya ya kirasu dukansu zuwa ɗakinsa, suka zo suka zauna saman buhu, yayi bismillah tare da watsa musu wani ruwan magani kana ya fara karanto musu ayoyin Alkur'ani mai girma. Ina one time suka wani sauya yanayi Najma ta sake fari sosai, wato farinta na da lokacin tana gidan mahaifinta ya dawo, shi kuma Majeed shima ya sake haske da fresh fatarsa ta da ta dawo, Malam yayi hamdala tare da sake ɗaga hannu ya godewa Allah, kafin ya sake yin bismillah Sannan yace "ku suwaye?" "Majeed ya fara kallon ɗakin yana waige waige, Najma kam kuka ta fara tana cewa "momyna wlhi karki sake yarda da mugaye" malam ya sake watsa mata adu'a kafin ta natsu, cikin nutsuwa Majeed yace ni ɗan PLATEAU ne, Jos mahaifina sunansa Alhji Abdullahi" malam yace "ko zaka iya bani lambar wayarsa?" Majeed yace "eh malam" Malam ya miƙawa Majeed waya yasa number mahaifinsa, sai dai a kashe, saboda tunda anty Asabe taji wannan maƙudan kuɗaɗen da ake bin bashi ta kashe wayar, Ya saka number mahaifiyarsa Hajiya Salima, cikin sa'a ta ɗaga tare da cewa "waye?" Duk da Majeed ɗin yaso ya yi magana amma sai ya miƙawa malam saboda girmamawa. Bayan Malam ya karɓi wayar cikin nutsuwa da Dattaku yace "sunana Malam Isyaka, ina zaune a garin Kaduna acan ƙauyen ƴan kifi, dalilina na kiranki wani yaro ne ana ce masa Majeed... Hajiya Salima na jin an ambaci sunan Majeed ta zaro idanu tare da sake riƙe wayar da kyau, kana tace "malam ina jinka" yace "siyarsu nayi a gurin wani mutumi a matsayin dabbobi, da yake dai Allah ya bani ilimi dai-dai gwargwado yasa na dinga yi musu magani, har muka yi nasarar karya sihirin duka, yanzu dai inason in kawosu gareku ya za'ayi?" Hajiya Salima tace "malam idan har kuɗi kakeji babu damuwa, ki taho dukkanku da mutanen gidan malam" Malam yace "a'a, zan fara kawosu ni da yarona, daga baya mai ɗakina zata zo, ai kuma zumunci ya ƙullu" Sukayi sallama da Hajiya Salima da niyyar gobe insha Allah zasu taho Jos, Ko da mama taji labarin an ga su Najma har rawa sai da tayi, tare da yiwa Allah godiya, tun a ranar suka fara shirye-shiryen abubuwan da zasu tarbi Malam dashi... MASARAUTAR MANDU A wani ɗaki mai kyau tangameme akayi mata masauki, ɗaki ne wanda yake ɗauke da gado irin na zamani mai kyau, sannan gefe da gefen gadon akwai wani bedsite masu kyau, a gaban gadon kafin ka hau sai ka taka wani lallausan carpet mai taushi sosai, daga hannun hagu wata doguwar drowa ce mai kyau irin kwaliyar gadon ne a jikinta, sai dressing mirror dake can gefe da stool shima mai kyau, Jakadiya tace "nan ne ɗakinki kafin ki koma ga iyayenki " Gudidi ta harareta tare da cewa "yasin baki isa ki koreni ba, zama a gidan nan daram ko mutum yana so ko baya so" ficewa jakadiya tayi ta barta tanata surutunta, saboda ta ga zatayi mata rashin kunya tunda dai a haife ta haifeta, da gudu tayi tsalle tare da hayewa saman haɗaɗɗen gadon, alamun buɗe ƙofa da taji ne yasa ta sauko da sauri tare da tsugunawa a ƙasa kamar mai karɓar gafara...! Ayi haƙuri babu yawa Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 Mom Islam Kuyi following ɗina Arewabook zaku samu more pages acan 👇 https://arewabooks.com/u/momislam11 Page 75-76 Gimbiya ce ta shigo, tana sanye da dakakken leshi mai kyau da tsada, leshin milk color ne, kwalliyar jikinsa sai ta kasance golden da duwatsu masu ɗaukar idanu, ta saka alkyabba a saman kayan, "Tashi ki zauna" Gimbiya tace tana yi mata alama da hannu, Inda kasan ruwa ya cinyeta haka tayi, bayan ta zauna Gimbiya tace "ke ƴar ina ce?" Sam bata yiwa Gimbiya ƙarya ba, ta kwashe labarin dalilin da yasa ta fito daga ƙauyensu har zuwa gidansu Rukaiyya da tayi da kuma dalilin da yasa ta gudu, Sosai Gimbiya ta jinjina kai tana dubansa, cike da nuna kulawa tace "ai nasan ƙauyenku saboda akwai wata yarinyar yayar mahaifiyata acan, kasancewar yanzu babu zumunci, wlhi iyayemu sunfimu zumunci, Gudidi tace "ahe ke ƴar garinmu ce?" "Ai kuwa amman a Kano muke zaune, aure ne ya kawoni nan garin" imbiya tace "zanyi bincike game da labarin da kika bani, idan har aka tabbatar min da gaskiya kika faɗa, tabbas zan roƙi iyayenki su bani ke sai in saki a makaranta" kamar wacce aka jefo daga sama ta wuntsulo tare da cewa "haba Hajiya, ai sun amince ma" Gimbiya tayi murmishi tare da fita daga ɗakin, Bayan fitar Gimbiya, Jakadiya ta shigo mata da wasu kaya masu kyau, kana tace "kije kiyi wanka" idan da akwai abinda ta tsana a duniya bai wuce maganar wanka ba, turo baki tayi, tare da cewa "toh naji" Jakadiya ta fice ba tare da ta sake bi ta kanta ba, Miƙewa tsaye tayi, tare da taɓe baki kafin tace "uhm komai iyayi mtsw, ni yanzu ina zani in watsa ruwan mtswww komai a takurawa mutum mtswww, ta dinga maganganunta ita kaɗai, wata ƙofa ta gani, ta tafi da sauri, kasancewar ta iya buɗe ƙofar tun a gidan Hajiya mama, tana buɗe kofar tayi mutuwar tsayi, wasu na'urori ta hango wanda ake amfani dasu gurin wanka da busar da gashi, harda su turaren wanka da towel masu kyau an rataye su, dube-dube ta farayi, a ina zata samu kofi ta ɗibi ruwan daɗi, cikin ƙasa da murya tace "ahe dai zamu sake haɗuwa da kai" cikin sa'a ta hango wani cup mai kyau, ga dukkan alamu watsa ruwa akeyi dashi ko meye oho, da sauri ta isa gurin cup ɗin ta ɗaukoshi tare da buɗe murfin, can dai ta hango sabulun wanka mai masifar ƙamshi ga shi pink color, ƙarisawa gurin sabulun wankan tayi tare da ɗaukoshi, kafin ta jujuyashi, kana tace "wlhi ƴan binni almubazzarancin su yayi yawa, wato biskiti ma a banɗaki, wlhi cinyewa zanyi idan har wacce aka ajiye wa tazo ita ta sani, saboda ba zanga samu inga rashi ba" Cikin gaggawa takai sabulun baki, ta gutsiri babba, sai da ta tauna sosai, ta tabbatar da ai ba abin ci bane, ta yamutsa fuska gami da furzarwa tana shirin yin kuka, tace "yasin Allah ya isa, ko meye oho, "to dame zan hyahe baki na?" Tai saurin ɗauko wata ƙatuwar mai coconut oil ta kurɓa, wani tsaro idanu tayi tare da haɗiyewa ba tare da ta shirya Ba, ji kake maƙwattt.. ta riƙe baki, tace "Allah yasa ba guba naci ba" kofin dake hannunta ta kalla, tare da buɗe p-toilet ta dumbulo ruwan tana cigaba da runtse idanuwanta, tana cewa "da nasani tun farko ruwan gaɗi na ɗiba da duk hakan bata faru ba" bayan ta gama magana ta kurɓa tare da lumshe idanunta, tace "Amincin Allah ya tabbata ga wanda ya haƙa rijiyar daɗi, billahi da ruwan zanyi kwaskwarima, tayi maganar tana sake dumbulowa tana shafawa a jikinta, daga ƙarshe ta fito bayan ta ajiye cup ɗin a inda ta ɗauka, samu tayi an ajiye mata wani kyakkyawan tray an jere kulolin abinci, gyara ɗaurin zanin dake jikin ta tayi kafin ta durƙusa fara buɗe foodflaks ɗin, na farkon da ta buɗe faten doya ne da wake, yaji hanta da busashen kifi, ɗayar foodflaks ɗin kuma, farfesun kan rago ne, wanda yaji kayan ƙamshi sai tashin ƙamshi yake yi, "rufe waccar kular tayi, ta ɗauki cokali tace "wlhi romo zan fara warɓa" tai maganar tana ɗibar romon a cokali, "wayo daɗi" ta faɗa lokacin da tayi cokali ɗaya, duk yawan romon sai da ta shanye shi tass, kafin ta fara cin naman, inda kasan kura haka ta koma, saboda ko kaɗan bata rage ba, Bayan ta gama ci ta miƙe tsaye tare da fara taka rawa, tana cewa... "Inci farfesu Sannan inhya ruwan garɗi" Tana faɗa tana rawa, har sai da ta gaji, ɗaurin bandejin dake goshinta ta fama garin yin rawa, da sauri ta haye gado ta kintsu, sai yanzu ma ta tuna da ledar maganin ta, an nuna mata amma bata sha ba.. Fulani part Zaune take a saman lallausar couch mai kyau, babban parlor ne kamar na Gimbiya wato Umma, sai dai ko kusa bai kamo kafar na Gimbiya a kyau ba, amman shima ɗin yayi babu laifi, domin a hakan ma Naira ta raina kanta, Ruma ce zaune a kujerar da take kallon tata, cikin shiga ta alfarma, idan baku manta ba, da Mai martaba mahaifin Prince Murad da mijin Fulani uwarsu ɗaya ubansu ɗaya sai dai mahaifin Prince Murad shine babba, " Ruma tace "Momy yanzu haka zamu zubawa yaya Murad idanu, ko tani da bayayi, ita kuma Uwar tasa ta zuba masa idanu kuma tasan alƙawarin da mai martaba yayi akan maganar aurenmu, Fulani ta taɓe baki kafin tace "akwai shirin da nake yi a kansu, tabba bazan barsu haka kawai ba, gara ma su samawa kansu lafiya su yi maganar tun kafin lokaci ya ƙure musu" Fulani ta ƙarashe maganar tana yin wani irin murmishi mai wuyar fassara. Acan fada, Akwai wasu dattijai waɗanda suka zamo masu bawa mai martaba shawara, sosai suka zamo Amintattunsa Cike da izza da kamala mai martaba ya fara magana yana daga zaune a kyakkyawar kujerarsa wanda gabaki ɗaya gidan an zaneshi da tambarin sarauta, "Ina son asa ranar auren Murad da Ruma, nan bada jimawa ba" Wani dattijo yace "ran Sarki ya daɗe Allah ya ƙara girma Ubangiji ya tsare ka daga dukkan sharri, abinda kace shi za'ayi" Kan kace me, labarai sun isa ɓangarori biyu, ɓangaren Fulani da kuma ɓangaren Gimbiya, cike da ɓacin rai Gimbiya ta miƙe tare da cewa "tabbas anzo gurin, gaskiya bana fatan haɗa zuri'a da Fulani, mai yasa mai martaba zai yi haka?" Shigowar Prince Murad kenan ya tsinkayo maganganun Gimbiya cikin fushi, Cikin ƙanƙanin lokaci ya birkice, saboda ya ji maganganun da Umman tasa take yi, Hadimanta suka tashi suka bata guri, domin ta gana da ɗanta ɗaya tilo, Zagaye ɗakin Gimbiya ta fara yi, tare da ɗaga kai sama cikin fushi tace "Murad tabbas wannan hukuncin beyi min daɗi ba, mai yasa mai martaba ba zai yi shawara dani ba?" Murad ya zauna a saman couch domin kuwa ƙafafuwansa sun gaza ɗaukarsa, yace "Umma shin da gaske ne mai martaba zai haɗani da Ruma?" Yai maganar cikin yanayi na damuwa, "tabbas Murad kasani idan har mai martaba ya yanke hukunci babu wanda ya isa ya sashi saɓawa, dan haka kawai kayi masa biyayya, saboda yana girmama duk abinda ɗan uwansa ya bari, nima kaina banji daɗi ba, babu inda zamuyi kayi haƙuri karka nuna ɓacin ranka bare har akai ga labari yaje wa mai martaba" Kansa a sunkuye yake saurararta, shiɗin mai biyayya ne, amma baya jin zai iya karɓar Ruma a matsayin matar da zasuyi zama na har abada, Wunin ranar Prince ya rasa abinda yake yi masa daɗi, acan part na Fulani abin ya birgesu, saboda babban burinta ƴarta ta auri Murad ko babu soyayyarsa a cikin zuciyarta, gashi buƙatarsu ta biya tun ba aje ko ina ba, tabbas wannan rana ta zame musu abin alfahari abin kwatance domin kuwa har sun fara tsara yanda shagalin bikin zai kasance.., Kano A ƴan kwanakinnan barci yayiwa idanunsa ƙaura, babu wacce yake muradin gadi da ya wuce Aysha, sosai yake jin zuciyarsa tayi masa ƙunci, hatta iyayensa ma sun kasa gane masa, har wata ƴar rama yayi, fuskarsa tayi fayau, Babbar damuwarsa ya za'ayi yaji koda muryarta ne, ko zai samu sassauci daga ciwon soyayyarta da ya addabi zuciyarsa, badan ya shirya zuwa gidan anty Tasneem ba, ya fice a motarsa, saboda baya zuwa idan har Junaid ya dawo, koda ya shigo cikin gidan, nocking ya dingayi, ya jima yana tsaye, badan uzirinsa ne ya kawosa ba, da tuni ya cikawa rigarsa iska, Junaid ne ya buɗe ƙofar tare da fitowa, cike da fara'a ya miƙawa Junaid hannu, suka gaisa, Junaid ɗin yace ka shiga tana ciki, dama yayi shirin fita ne, zai mayar da Umaimah gida, yau kwanansa ɗaya da dawowa, Allah ya kiyaye hanya yayi masa kana ya wuce ciki, ya samu Umaimah na fitowa, hannunta riƙe da jakar kayanta anty Tasneem tana ce mata ta gaida su Hajiya, sai sunyi waya. Bayan ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun mai zaman mutum ɗaya, ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya kafin yace "anty Please kizo ki sallameni" Anty Tasneem ta nemi guri ta zauna kafin tace "Arman ina saurarenka?" "Anty dan Allah ki taimakawa rayuwata zuciyata tana daf da fashewa na rantse miki da Allah anty ina son Aysha, tun daga ranar da na fara sanyata a idanunsa, har kawo yanzu wlhi bazan iya daina sonta ba, gashi yana neman yimin illah" sosai ta hango tsagwaron gaskiyarsa a ƙwayar idanunsa, tabbas yana sonta, saboda ko itama ta zargi hakan, sai dai bata furta ba, itafa abin ya ɗaure mata kai, tace masa "Arman yanzu mai kakeso?" Murya kamar zai yi kuka yace "anty dan Allah kije ki nema min izinin yin hira da ita, kokuma kisan inda za'ayi in dinga jin muryarta wlhi zan iya shiga wani hali idan har ban samu Aysha ba" Ajiyar zuciya ta sauke tare da riƙe baki kana tace "taɓɓ hmm Arman ka manta ko wacece Hajiya mama?, in tashi daga nan in tafi Abuja in dawo raina a ɓace?, sai dai zanyi maka abu ɗaya, zan kira anty Jamila idan har wayar ta shiga zance a bawa Aysha mu gaisa idan na gaisa da ita zan baka sai ku gaisa, amma wannan maganar kam a WhatsApp zanyi da anty Jamila" sai yanzu yaji zuciyarsa ta fara sanyi, Neman guri tayi ta zauna, kafin ta kira anty Jamila tace "Arman wai ma tukunna kasan me kake faɗa kuwa?" Aysha kwata-kwata shekarunta 14yrs ne fa?" Ya katseta da cewa "anty wlhi ko goma ne zan iya aurenta" Anty Tasneem tace "tabbas ka samu taɓin hankali wlhi ba za'ayi wannan haukar dani ba, ƙaramar yarinya? ai ni su Hajiya zasu bawa rashin gaskiya gaskiya Arman bazan iya ba, ka sauya shawara, kokuma ka bari idan ta sake girma tunda girman ɗan mutum babu wuya" Tai maganar tare da sauya yanayin fuskarta zuwa ɓacin rai, "Allah sarki anty wato bakisan abinda nake ji bane da har zaki yanke min wannan hukuncin" "Hmm Arman ga ƴan mata nan da yawa, ka tsaya bata lokacinka akan wata Aysha da ko two weeks batayi da fara period ba?" "Nidai ita nakeso kuma zanje Abuja a satinnan wlhi" Ya faɗa yana miƙewa tsaye da sauri ya fice a parlorn ransa a ɓace... Bikin bidiri Zyd a Abuja Arman a Abuja hhhh yanzu wasan ya fara Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam🍹_ Kuyi following ɗina Arewabook zaku samu more pages ga link nan 👇 https://arewabooks.com/u/momislam11 Page 77-78 KEFFI Dady ne zaune a gaban boka, yana labarta masa nasarorin da ya fara samu, tunda yayi wanka da ruwan jini, Cikin Muryar mai ɗauke da ƙaraji boka yace "nasara yanzu ka fara ganinta, sannan komai zai ci gaba da tafiya yanda ya kamata" Cike da samun ƙwarin gwaiwa Dady yace "godiya nake" ya ajiye wa bokan wata ƙatuwar jaka mai ɗauke da maƙudan kuɗaɗe kana ya miƙe yana yi masa sai anjima, boka yace "duk halin da ake ciki su dinga yin waya.." Zaɓe ya rage saura wata biyu, daga Dady har momy babu zama, shi yana neman inda zai cigaba da samun ƙarɓuwa a gurin mutane, ita kuma tana son ta mallakeshi, ta kowace hanya, na duk abinda tace sai yayi mata shi. Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya anyi primary Election anci nasara, duk wani Election Dady ne a first, saboda ya samu magoya baya sosai da sosai, domin kuwa ya ɓarar da Naira tare da jinin al'umma, shikam ba a gurin ubangiji yake neman dacewaba, a gurin boka yake nema. Gidan Dady ya kasance cikin tsaro koda wane lokaci, tun kafin ya zamo shugaban ƙasar ma mutane suka daina sashi a idanunsu, domin kuwa ya tafi ƙasar waje, hatta ita momyn uzuri takeyi masa saboda su samu abinda suke so. Acan fanin anty Hadiza, sun tafi Dubai ita da ƴarta da mijin Salma zai aure wato Junaid, Siyayya suka dinga yi kamar na hauka, saboda Junaid ya tabbatar ma da hindu yana dawowa daga Kano, zai turo iyayensa, yafi son ayi komai a gaban idanunsa, 2weeks suka kwashe kafin suka dawo Nigeria, washe gari Iyayen Junaid suka zo gidansu Hindu nema masa aurenta, cikin mutuntawa sukayi komai da tsari tare da girmama juna, sha tara ta arziki anty Hadiza tayi musu, manya manyan kaji anty Hadiza tasa hindu ta soya musu, akayi musu cake da kunun gyaɗa mai daɗi, tare da shinkafa da miya, bayan sun ci sunsha anyita yin raha da wasa da dariya, aka yanke wa iyayen Junaid dukiyar aure, dubu ɗari bakwai aka yanke musu, sai suka bada, 1million kasancewar su ɗin masu hali ne, sosai, haka ma mijin anty Hadiza shima yana da nasa halin dai-dai gwargwado saboda baza'a kirasa da talaka ba, a take a gurin aka saka rana wata ɗaya, Bayan tafiyarsu, baban Hindu ya mayar wa da Anty Hadiza inda sukayi, har rawa sai da tayi tsabar farin ciki, tana cewa "ashe zanga aurenki hindu?, idan kana da ƴa mace muddin baka aurar da ita ba, kana cikin fargaba, yau dai Allah ya yanke miki wahala Hindu, yarinya kamarki shekaru 34yrs talatin da huɗu wasa ne?" Baban Hindu yace "dama komai da lokacinsa, idan ka miƙawa Ubangiji lamuranka, sai kaga komai ya zo maka da sauƙi cikin sassauci, dama shi muke roƙo kuma gashi ya amsa mana" baban Hindu yace "ku samu paper da pen ku rubutomin duk wani abu da za'a buƙata ni zan fita" Anty Hadiza tace "to baka da matsala" yau dai sun kasance cikin farin ciki, idan ka cire hindu da ta rasa inda zata tsoma kanta tsabar farinciki. Hajiya Zaliha ce zaune a parlor ita da Salma, Dan tunda Junaid yayi tafiya ta dawo gidan suna ta jajantawa juna, Wayar Salma ce ta fara ringing, suna cikin magana da mahaifiyarta, ta janyo wayar kasancewar tana ajiye a gabanta saman table, a kunne ta kara bayan ta danna kore, lokaci ɗaya walwalar fuskarta ta ɓace ta fara haɗa gumi, cikin sauri ta janyo mayafinta tana fifita, sai kuma ta miƙe tsaye a zabure cike da masifa tace "wlhi tallahi yau akwai kutumar bura uba, ni anty Hadiza zata cutar?" tai maganar tana ajiye wayar, Cikin sauri Hajiya Zaliha ta miƙe tsaye tare da yi mata alama da hannu "mai ya faru?" Salma na sauke numfarfashi tace "momy anty Hadiza wlhi tallahi ta cuceni ta gama da rayuwata, Junaid har ya kaiwa ƴarta sadaki bani da labari, yanzu ƙanwarsa ya kirani take gayamin, ta janyo mayafi zata fice da sauri, Hajiya Zaliha ta riƙo mata hannu kafin tace "wato Salma ita duniya dama haka take, wlhi ni dama hankalina gabaki ɗaya bai gama kwantawa da wannan muguwar matar ba, wato tanan ta ɓullo, wallahi idan har zan ƙarar da duk abinda na mallaka akanta billahillazi sai na sa ta shiga taitayinta, kokuma ni ban cika ƴar halak ba, Salma ki kwantar da hankalinki, abinda nake so dake... Ki aiyyanawa ranki cewar, labari aka baki bai tabbata ba, idan har ina numfashi bazaki haɗa miji da wata ƴa mace ba, sannan Junaid naki ne har abada" Cikin faɗa da tashin hankali gami da tsananin ɓacin rai mahaifiyar tata take maganar, Salma ta durƙushe a gurin tana kuka, cikin muryar kuka take cewa "momy Meye bana yi masa, ga shegiyar jaraba koda yaushe a cikin yin wankan tsarki nake, haka nake daurewa amma yace zai..." Ta sake fashewa da kuka, sosai mahaifiyar Tata, ta lallasheta kana tayi shiru. SAUDIYYA Idan kaga gidan nasu sai ka rantse ba hannu ne ya gina shi ba, saboda kyau da tsari, kasancewar ginin irin na turawa ne, babban parlor ne mai ɗauke da ɗakuna sunyi bakwai, ko wanne da abinda ake sawa a cikinsa wani mutane ne a ciki, zaune suke a parlor shi da Mahaifiyarsa da ƙanwarsa da akayi mata tiyata ta warke, Umminsa tace "Thabit ya maganar ƴan matan da muka yi magana dakai kwanakin baya kace zaka cetosu?" Thabit ya dafe goshinsa kana yace "ummi tunkarar Oga Reed ba abu bane mai sauƙi, nidai yanzu abinda nake buƙata adu'arki tare da fatan nasara" Ummi ta kai lallausan tafin hannunta ta shafi kwantaccen baƙin sumar da yayi luf a kansa, kana tace "insha Allahu bazaka taɓa shiga musifa ba" ya haɗe hannunsa da nata yace "amin ya rabbi Ummina" Ummin tace "Thabit Ubangiji yayi maka baiwar da ba kowane ɗan Adam yayiwa ba, Kanada damar da zaka taimaki waɗannan bayin Allahn bansan mai kake jira ba?" Ummi tunda har kinyi min adu'a insha Allah zan sake sabon shiri in koma, ammafa Ummi idan na samu wanda sukayi min gardama tabbas bazan taho dasu ba" Ummin tace ta amince, Yace "nan da kwana bakwai zan je Singapore, dalilin da yasa zan bari sai zuwa one week, zan dai daici lokacin da aiki yasha masa kai, Ummi ƙazantar rayuwar da sukeyi acan wlhi babu kyan gani, ni kaina badan dole ba, wlhi ba zan raɓesu ba... Tofa, gadai Thabit ya fara shirye shiryen zuwa taho da ƴan gidan oga Reed. ƘAUYE Tun bayan tafiyar Gudidi Ramma ta gamu da wani irin ciwo, wanda ta rasa inda kanta yake, saboda Allah ya ɗora Mata son Gudidi kasancewar su biyu kawai ta haifa, da Gudidi da ƙaninta, a halin yanzu kullum suna cikin yawon zuwa karɓo magani, ita da mahaifin Gudidi, basa nan basa can, koda yaushe bata da maganar da ta wuce "a nemo mata Gudidi ina Gudidi take?" Shi kansa mahaifin gudidin tafiyarta yana damunsa, babu inda zai yi ne kawai, har Hajiya mama aka kira a waya ko da ta ɗauka tace musu gudidi bata zo gidansu ba, dole suka haƙura suka ci gaba da adu'a, Can fannin Inna kuwa, tunda Aysha ta dawo gidansu Hajiya suke yin waya akan lokaci, hakan yasa hankalinta ya daɗa kwanciya, sannan duk ƙarshen wata sai Hajiya ta aika mata da kayan abinci, ko ya ƙare ko bai ƙare ba, a halin yanzu ma da ake ta shirye-shiryen watan azumi Hajiya ta aika mata da buhun dawa da Gero dana shinkafa da kayan haɗi, akan kullum Inna ta dinga yin abincin sadaka, ABUJA Bayan kwana biyu da zuwan Ma'aruf da Layla, Aysha tace "anty wlhi budurwar yah Ma'aruf ta fiye ƙaton baki ga dogon gashi🤣. Hajiya taso yin dariya, amma sai tayi murmishi kana tace "itace zaɓinsa" anty Jamila ta taɓe baki, kafin tace Wlhi ni haushi ma take bani, nifa lamarin mamaki ya bani, son da baya kula ƴan mata, ko auren da akayi masa da Saudart zaɓin Alhji ne, amma wai shine har da kawo mana wata yarinya mai buɗaɗɗen idanu, wannan yarinyar da gani bata da kunya kuma ni ina ganin a girme na ta girme masa" Hajiya dai ko uffan bata ce musu ba, saboda tsananin ɓacin rai da zuciyarta take ciki, su biyu suke ta surutansu, Wayar anty Jamila ce ta fara ringing, bayan ta amsa wacce ta kirata tace "Please ki hau WhatsApp yanzu zan tura miki da wasu abubuwa, dan Allah ki fahimceni" cikin sauri anty Jamila ta katse kiran tare da kunna data kana ta online, wasu hotuna masu yawa ne suka dinga shigowa, sunkai guda goma, sai da ta bari sun gama buɗewa kafin ta mayar da hankali ga hotunan da aka turo, Hajiya dai na kallonta ita da Aysha, Hajjo ce tayi nocking a bakin ƙofar ɗakin Hajiya, bayan an bata izinin shiga tace "wasu ƴan mata ne suka shigo sai matar aure guda ɗaya, Hajiya tace "ayi musu iso zuwa parlor gani nan zuwa" Aysha ta miƙe tare da cewa "anty inzo mu kalla ne?" Anty Jamila ta girgiza mata kai fuskarta a murtuke kamar zata fasa ihu, lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya sauya, Aysha ta miƙe ta fice tana cewa "anty Allah dai yasa lafiya, Kai tsaye ɗakinta ta wuce kana ta kunna wayar ta, massage ne ya dinga shigowa yakai kamar guda biyar duka na saƙon soyayya, daga masoyinta, wani irin murmishi tayi mai kyau, kafin ta fara karantawa.. "Kullum da nake numfashi, ka lmar da zuciyata ke furtawa ita ce: ‘Ke ce masoyiyata ta har abada" "Sonki ya shige ni kamar jini cikin jiki, ba zan iya janyewa ba har sai zuciyata ta daina bugawa." Haka ta dinga karantawa tana sake faɗaɗa fara'arta, idan har taga saƙon Zyd ko taji muryarsa sai ta rasa sukuni, sbda ta mugun kamuwa da soyayyarsa, Kamar yasan ta kunna wayar, aiko taga kiransa, maganar jan aji babu tunda yau kwana ɗaya kenan bataji muryarsa ba, cike da shagoɓa tace.... Wallahi, idan soyayya ce mafarki, to ni bana so in tashi... in dai kai ne a cikin mafarkin.” Ita kanta bata san ya akayi ta iya jera masa zance haka ba, yayi murmishi tare da cewa " "Tabbas Ubangijina ya cancanci yabo ta kowacce fuska, bayan ni'imar rayuwa da ta lafiya da yayi mana, sai kuma ya kara mana da baiwar kasantuwar sanyin idanun mu a cikinmu, wadda muke kalla muji nutsuwa ta sauka a jikinmu, muji tabbas muma wasu mutane ne masu daraja, saboda kasantuwar me daraja a cikin mu." Ya faɗa yana sake sanyaya muryarsa, murmishi tayi mai sauti kafin tace "kasan me?" Yace "a'a" "Mijina na shirya shiga ko wace gwagwarmaya idan har zan sameka" "Wani irin shauƙin so yakeji wanda shi kaɗai yasan da hakan, a ganinsa ko ita idan yayi mata bayani ba ganewa zatayi ba, kai tsaye yace "gobe ina hanya.." tabbas tayi ganganci soyayya ta sanyata suɓutar baki yanzu ya zatayi..? Oho ho, labari ya ɗau wuta 🔥, sai dai ina mai baku haƙuri tare da sanar muku da cewar, book 2 da book3 na littafin NA KASA JUREWA zai zo muku a na kuɗi, akan Naira 500 special group 1k nasan masoyana bazasu bani kunya ba, ta hanyar yin payments. Insha Allah na kusa gama book1 saboda yana iya ƙarewa a koda yaushe, Ga wanda zasu tura da kuɗinsu ga account number na 3175689751 Zainab Habibu first Bank, shaidar biya ta wannan number 08141799224, idan zakiyi vtu kimin magana idan kuma kati ne mtn Idan na kammala book1 zan cigaba da posting a Arewabook idan kuma an gama payments zan fara posting a WhatsApp da wuri. Mom Islam 08141799224 Mom Islam *NA KASA JUREWA* 💋💋💋 💋💋 💋 _Mom Islam🍹_ Page 79-80 Singapore Tunda Hajiya Zaliha ta fara magana bai ce mata komai ba, har ta gaji tayi shiru, cike da jin haushi gami da takaici tace "Alhaji na rantse da Allah bazan bari abinda kayimin ya tafi a banza ba" Ta ƙarashe maganar tana katse kiran, Har takai ƙarshen maganarta bai tanka mata ba, saboda yasan idan ya biye mata sai su wuni aje ma a samu matsala, lokacin da suke zuwa ƙasar waje Tare, duk ƙasar da ta zaɓa nan zasuje, "mai yasa tasa Saudart a gaba, yarinyar da babu ruwanta?" Bayan ya ajiye wayar ya juya ya kalleta, barcinta takeyi cikin kwanciyar hankali, Allah ya jarabceshi da son Saudart, so mai tsanani, hayewa gadon yayi tare da jan blanket ɗin kana ya matsa kusa da ita, hugging ɗinta yayi sosai, ya matseta a jikinsa, daƙyar yake fusgar numfashinsa saboda tun ɗazun ta kwance masa lissafi, bazai iya bari sai anjima ba, hannunsa yakai dai-dai kan nipple ɗinta da suke a tsaye cak ya fara wasa dashi, yayi amfani da dayan hannunsa gurin tallafo kanta, a hankali ta fara jiyo wasannin da yake yi mata, miƙa tayi wanda ya sake fito da asalin halittar jikinta, aiko Alhaji ya rikice sai wani irin Abu yake yi jiki na rawa, ita kanta ta kasa hanashi, daga ƙarshe ma sai ta fara mayar masa, hakan ba ƙaramin daɗi yayi masa ba, kan nipple ɗinsa ya fara murzawa a hankali cikin salo mai motsa sha'awa, tabbas tasan ta rikitashi, kai tsaye ya fara kokawar neman haƙƙinsa, bata hanashi ba, sun shafe lokuta suna jiyar da junansu farin ciki, a hankali ya mirgina gefe yana sauke numfashi tare da cewa "Habibty Allah yayi miki albarka Allah yasa ki haifamin yara masu irin halin ki, idanunsa a lumshe yake maganar, wayarsa tayi ringing ko da ya ɗan buɗe ido ya danna receive ya mance bai sa wayar a kunnensa ba, Muryar Saudart a sanyaye tace "mijina i love You so much, da sauri ya ajiye wayar a gefe yana sauke numfarfashi yace "Habibty i love You too, Habibty na rasa irin son da nakeyi miki kin jiyar dani ni'imar ki kin shayar dani Habibty Allah yayi miki albarka, Cikin daga murya Hajiya Zaliha da ta gama jin duk abinda suke cewa, zuciyarta na tuƙuƙi tace "mu kuma Allah ya tsine mana ko?" Sai a lokacin ya tuna ashe ya danna bai sa a kunnensa ba, "Hello Hajiya" ya faɗa murya kamar ta mai barci, cike da takaici ta katse kiran, Salma ta gama kukanta ɗazu ita yanzu take yin nata, ta kwashe duk abubuwan da taji sunayi ta gayawa Salma, rai a ɓace Salma tace "momy wai bakisan gurin bokaye bane? wlhi inhar dani aka tafi sai nasa an haukar da matar Dady, anty Hadiza dake rangaɗo sallama tace "Salma kibi a hankali duniya ba matabbata bane, hamdala Salma tayi, saboda dama babban burinta tayi ido biyu da Anty Hadiza kuma gashi tayi, kukan kura tayi ta cafko wuyan hijabin anty Hadiza, suka fara dambe Hajiya Zaliha ma ta shiga, sukayi wa anty Hadiza dukan tsiya, tare da yi mata gargaɗin idan har ta bari hindu ta shigo gidanta, ta ƙaddara wa kanta kamar ta shigo cikin kabari ne, saboda ta ɗauki alwashin sai ta kasheta har lahira, Anty Hadiza ta miƙe tsaye tana kuka, tana cewa "wlhi tallahi nayi dana sanin saninki a rayuwa, kishin banza kishin wofi, idan har wannan abin da kikeyi Sannan kika koyawa ƴarki shine kishi Allah ya tsine muku keda kishin jahilci kawai, kuma wlhi Hindu sai ta auri Junaid ko ta halin ƙaƙa idan har kunce bin bokaye ne aikinku wlhi tallahi nasha gabanku, ada na bayar da aiki akan kishiyarki Saudart, yanzu kuwa na riga da na janye kuma wlhi sai ta zauna a gidan mijinki ta haifi yara, kuma wlhi ni na gaya miki sai kin zamo ƴar kallo, ai bazan bari wannan dukan ya tafi a banza ba, Salma ta shige kitchen da gudu ta ɗibo wuƙaƙe ta dawo parlor tana cewa "yau sai na kasheki, anty Hadiza ta fice da gudu cikin ɗaga murya take cewa "wlhi kun gama samun nasara a rayuwarku har abada ku da cin galaba akan wasu, tana gudu tana maganar, Salma na binta da gudu, mai gadi kam yaga ikon Allah, saboda Hajiya Zaliha a kaf ƙawayenta sunfi shaƙuwa da anty Hadiza, yau kuma gashi yaga ƴar Hajiyar ta biyota da wuƙa ko lafiya oho, bayan Salma ta koma parlorn tana mayar da numfashi, Hajiya Zaliha tace "Salma sai yanzu na sake tabbatar wa lallai ɗan adam ba abin yarda bane, ki kalli alkairin da nake yiwa Hadiza amma ni zata yiwa zagon ƙasa?, kinsan me nakeso dake ? ki shirya kayanki ki koma gidan Junaid, idan har ke jinjina ce nasan zaki iya aikata duk abinda nace kiyi" Hajiya Zaliha taci gaba da magana cike da ɓacin rai, "Salma idan kin koma, karki fito da kishinki a fili, nasan ma haɗaku zaiyi gida ɗaya, ki bari sai a daren farko idan ya fita yin wani abun ki shiga kisa key a ƙofar, karki bari ya raɓi shegiya, daga nan kiyi mata mugun duka sannan ki tattakata, daga miliyan ɗaya zuwa sama zan ajiye inhar yarinyar nan tayi sallama da gidanki, ni gashi saken da nayi ne har ya janyo wai Alhaji yana Singapore shi da tsinanniyar yarinyar nan, Haɗamin kayana wlhi na ɗauki alwashin kashe Saudart ko zanyi gidan yari " Hajiya Zaliha ta faɗa tana miƙewa, juyi ta farayi a tsakiyar ɗakin, babban abin tunaninta a ina zata samesu, wata shawara ce ta faɗo mata, na ta haɗa plan da abokinsa sai ta bashi kuɗaɗe masu tsoka,. Ta nemi guri ta zauna tare da danna number abokinsa, bayan ya ɗaga da farko tace masa inaso kayimin wani aiki zan baka 2millions waro idanu yayi, kamar tana ganinsa, jikinsa na rawa yace "Hajiya wane irin aiki ne gayamin inji?" Hajiya Zaliha tace "inason ka kirawo Alhaji cikin siyasa ya sanar maka da inda yake, idan har ya faɗa maka gaskiya zan tura maka" A take a gurin yayi mata alƙawarin zai tambayesa, ba tare da ɓata lokaci ba rayuwa mahaifinta magana, kasancewar mahaifin Hajiya Zaliha yayi tashen kuɗi kuma ma har yanzu yana kai, tace "visa takeso zataje Singapore, kasancewar duk wani mai fita ƙasar waje su suke sa hannu, "baki da matsala, kawai ki shirya" Mahaifin nata shima yayi mata alƙawari.. 🙅 Tofa, ya kuke ganin zata kaya idan har Hajiya Zaliha ta sauka a Singapore, zata samu damar ganinsu kuwa kokuma bulayi zatayi, idan har sukayi ido biyu da Saudart mai kuke tunanin zai kasance ? PLATEAU Jos Ko da su Malam suka isa Jos, basu sha wahala gurin gano gidansu Hajiya Salima ba, kasancewar sunata waya da juna, sallamarsu kawai taji, ta kasa ɓoye farincikinta, ta fito kana ta bisu da kallon tausayi, babbar tabarma aka shimfiɗa musu kasancewar gari akwai zafi, mama ta kawo musu abinci kala kala, da drinks masu sanyi, Masha Allah sunci sunsha dukkansu, saboda Majeed shi da Haladu a tare da malam suke cin abinci, hakan ko ya birge Hajiya Salima, bayan sun gama ci, suka tafi masallaci sukayi Sallah itakuma Najma tayi a gida, malam ya sake basu labarin inda akayi suka zo gurinsa, godiya su mama suka dinga yi masa harda kuka, daga nan malam yayi musu sallama cewar zasu tafi tunda dai lokaci babu wuya, Haladu ne yace "Majeed dan Allah kazo" suka fice waje, "Majeed dan Allah ka gayawa Najma ina sonta, Majeed bakasan ya nakeji bane a cikin rai na" Majeed ya kalli ƙwayar idanun Haladu kafin yace "tabbas babu karya a maganarka, nayi maka wannan alƙawarin ai ka bani lambar ka zamu dinga gaisawa, Suka dawo cikin gida, Hajiya Salima ta shiga ɗaki ta ɗibowa Malam kuɗaɗe masu yawa, wanda a ƙalla zasu kai 2 millions malam ya zaro idanu tare da cewa "Hajiya ni nayi ne domin Allah Wlhi karki damu" duk da hakan, sai da Hajiya mama tayi masa kuka akan sai ya karɓi kuɗaɗen nan, kaɗan ya ɗiba wanda bai wuce dubu ɗari biyu ba, ya miƙe suka fice, Hajiya Salima na yi masa godiya, Bayan tafiyarsu, su Najma sukayi wanka, ta basu kaya suka saka, saboda har da kayansu ta ɗibo a can gidan, sai gasu sun fito gunin ban sha'awa, washe gari ta suka shirya da Hajiya Salima da Najma da Majeed zuwa gidan mahaifinsu, ko da sukayi nocking mai gadi ya buɗe sai da ya tsorata, saboda an ce musu sun mutu, sam ya kasa ɓoye tambayarsa yace "ashe kuma raye?" Murmishi sukayi masa, kasancewar motar haya suka shigo. Hajiya Salima tace mai gidan tana ciki? "Eh suka ce mata bayan su gaishe ta cike da girmamawa, driver yace "Hajiya dan Allah ki dawo wlhi rabonmu da abinci tun da kika tafi, murmishi kawai tayi, suka shige ciki, ƙofar parlon a buɗe yake hakan ya basu damar kutsa kai ciki tare da yin sallama, fara saukewarta kenan daga upstairs tayi tozali da fuskar abinda ta tsana a duniya wato Majeed, sake mutsike idanu tayi suna kallonta, ta wani fara gungure har ta sauko gabansu, kamar da wacce aka hankaɗo babu numfashi, Najma ta miƙe da gudu ta nufi fridge tana neman ruwa ta yayyafa mata, Hajiya Salima na zaune suna kallonta ita da Majeed, 🤗Ana wata ga wata, gafa Mutuniyarku zata kashe kanta, idan ta farka ko a wane hali zata kasance oho? me kuke tunanin zai faru a tsakanin Haladu da Najma zata amince ta karɓi soyayyarsa kuwa?.. KD Bayan tafiyar Yaseen, Kaka ta kalli ƙwayar idanunta, murmishi tayi wanda ita karsa laɓenta, Momcy sarai ta fahimta, hmm kawai tace, wanda yasa Saudart ɗin cewa "lafiyarku" Momcy ta watsa mata daƙuwa tare da cewa "dan ubanki kinje kin bashi abinda yazo nema ko?, wlhi ko kwana arba'in bazakiyi ba zaki koma ɗakinki kije can ki ƙarata, kaka tace "ba haka za ayi ba, kawai idan yazo a dinga miƙa masa mirmrah ita kuma su dinga yin waya" momy tace hakan ko za'ayi, sororo ta tsaya tana kallonsu, domin ta fahimci abinda suke nufi, ta fara kallon jikinta a tunaninta ko sunga wani abun ne suka gane abinda tayi, sai dai bata ga komai ba, tsabar haushi ma ta fice musu a ɗakin, Bayan kwana uku, har yau bai sake dawowa ba, sai dai suyi waya time to time, tabbas taji babu daɗi, Yau kam ta tashi da son ganin mijinta, kai tsaye ta wuce ɗakinta ta danna numbersa, yana ɗagawa ta fashe masa da kuka, ita ta gaji da zaman gidansu Momcy yazo ya ɗauketa, ya zaro idanu kamar tana ganinsa, tare da cewa "wane ni, ai ban isa ba, kinsan kuwa ranar da Manzo zan fita, naci karo da kaka a hanya cemin tayi idan ta sake ganin ƙafata sai ta karyani, shine kikaga naja baya, my life wlhi ko muryarki naji sai ta saukar min da sha'awa mai tsanani, kai tsaye tace "my hero kawai kazo, koma me zasu faɗa su faɗa, idan ba haka ba wlhi zan dawo gidana saboda na gaji da barci ni kaɗai" Ko kaɗan baya son ɓacin ranta, hakan yasa yayi mata alƙawarin zai zo anjima, Aiko ya kama hanya, bayan ya shigo da motarsa, lokacin kaka ta fito harabar gidan, tana ganinsa tayi saurin zuwa burinsa tace "kai dai ka fiye naci, kuma wlhi iyakacinka parlor, yau dai kaka ta ƙuresa, yace "wai kaka ina ruwanki, mutum da matar.., kafin ya ƙarasa magana, kaka ta ruga da gudu ta shiga ɗakin Yusra, kaka ta nunata da hannu tare da ƙarasawa taja kunnenta kana tace "wlhi idan baki sallami jarababben mijinki a can parlor ba, sai na saɓa miki wannan da gani ma kwanannan zai sake yi miki wani cikin, wawuya kekuwa kina wani rawar kai" Allah Allah take yi kaka ta fice ta fito parlor, saboda duk faɗan da take yi bai dameta ba, satinsu uku da kwanaki amma ana gindaya mata wasu dokoki idan maganin mata ne ai tasha sosai, Cikin sanɗa ta fito parlor tare da kamo hannunsa, sun fara tafiya kenan kamar marasa gaskiya, sukayi ido biyu da Momcy ta fito... Hhhh wasa farin girki "kuna ganin zasu shiga daga ciki kuwa kokuma sun haƙura da cimma burinsu?" Yanzu wasan ya fara. ABUJA Hawaye ne ya fara bin kumatun anty Jamila, da sauri ta kashe wayarta gabaki ɗaya saboda tiririn da zuciyarta keyi, acan parlor ma hakane, Hajiya kuka takeyi harda majina, cikin ɗaga murya take cewa "wlhi tallahi idan har Ma'aruf ya auri wannan yarinyar sai dai idan har bana numfashi.. Matan suka fice Hajiya na yi musu godiya, tana shiga bedroom ɗinta tayi ido biyu da Anty Jamila na matsar ƙwalla, Hajiya batasan lokacin da ta fashe da matsanancin kuka mai sauti ba, Can ɗakin Aysha, tana rungume da waya, sai ga kiran Laurat, waro idanu tayi, saboda tayi mata alƙawarin zata kirata gashi har kwananta huɗu ko flashin batayi mata ba, bayan sun gaisa Laurat tace "Aysha muna hanyar zuwa Abuja nida dadyna, tama rasa abinda zata ce, kawai tace "toh laurat, sai ga kiran wata sabuwar number, tana ɗagawa daga can ɓangaren yace Arman ne, Aysha yau ɗinnan ina hanyar zuwa Abuja.., hayaniyar da taji ne yasa ta fito da gudu, muryoyin Hajiya da anty Jamila, anty Jamila na magana cikin ɗaga murya tana cewa "dole Ma'aruf ya auri ƴar uwarsa Aysha, Hajiya na cewa "bazan shiga haƙƙin Aysha ba, dole a barta ta zaɓi wanda takeso, turus taja ta tsaya jiki babu ƙwari tama rasa a wace duniyar take, lokaci ɗaya taji garin yayi mata wani iri, kanta ya gaza ɗaukar damuwar da yake ciki, Zyd yace zai zo, Laurat ita da dadynta Arman shima zai zo duk da bata san Meye silar zuwan nasa ba, gashi bata san inda ya samu numberta ba, sai jin ƙarar faɗuwar mutum sukayi tiiiimmm...! To da wasa farin girki, Aysha dai tana cikin cakwakiyar soyayya, mai kuke tunani duka zaku samu amsoshinku a cikin book 2 ALHMDULILAH, anan na kawo ƙarshen book 1 na Littafin NA KASA JUREWA, idan kinason book 2 & 3 ga tsarin inda zaki biya 👇 Normal group 500 posting sau ɗaya a rana Vip 1k posting sau biyu a rana Account number 3175689751 Zainab Habibu first Bank, Shaidar biya ta wannan number WhatsApp only 08141799224 Idan zakiyi vtu kimin magana, idan har kika tura ta numberta babu ruwana. Insha Allah zan cigaba da posting a Arewabook har zuwa lokacin da za'a gama payments, idan aka gama da wuri zan fara posting a WhatsApp insha Allah. Allah yasa mu amfana da darasin dake cikin littafin muyi watsi da abinda bashi da kyau, sannan ina neman yafiyar wanda na ɓatawa rai, sai mun haɗu a book 2&3 👏 Taku har kullum Mom Islam, An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels