An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels [6/4, 7:46 PM] maman sauban: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GMAOuujeP6dLtFTHo1Edxx 🌹 *KUKAN ZUCIYA* 🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYYA AIMANAH AND NOW KUKAN ZUCIYA 1-2 Safa da marwa kawai take a ɗakin gaba ɗaya hankalinta yaki kwanciya tunda Prince AMEEN ya shiga wajan Abbi zuciyarta ta gaza nutsuwa so take taji mai zasu tattauna gaba ɗaya a Jiya zuwa yau xuciyarta ba daɗi tun da Prince yadawo daga CANADA tasan cewa tayi bankwana da kwanciyar hankali itakam ta matukar tsanar Prince AMEEN inama inama inama itama tana da ƴaƴan nan da tabbas saita shiga ta fita taga Prince bai sami sarautar nan ba tabbas a yanzu ma sai tayi duk abinda zatai wajan ganin ta ɓata masa suna ta yanda masarauta zasu hanasa sarautar "Ya zama dole naga bayanka Ameen ko zanyi yawo tsirara saina ga bayanka Ameen", jin karar tafiya ana sakkowa daga bene yasa tai saurin komawa kan kujera ta zauna ta fara tsinkayo muryar dogari na faɗin "Gaba salama baya salama a lafiyar takawa Prince Amin amanar mai martaba taka lafiya jikan sarki Abdulmunab" dai dai sannan Prince ya gama sakkowa nan falon inda Hajiya Jameelah ke zaune "Barkanmu da safiya Anty" Prince Ameen ya faɗa yana daga tsaye nan kafar benan, ɗan taɓe baki Anty Jameelah tayi kana ta ce "Barka dai sannu da fitowa" tana gama faɗar haka ko amsa mata baiyi ba yasa kai ya fice daga falon, da sauri dogari ya buɗe masa murfin mota ya shiga yana masa kirari, saida suka hau kan titi sosai sanan sarkin mota ya ce "Ranka yadaɗe ina muka dosa?" "Masarauta" yafaɗa a dakile yana wani haɗe rai, har suka karasa gidan sarautar bai ko kara magana ba danna wayarsa kawai yake hankali kwance yana hakimce a bayan motar, suna parkin da sauri dogari ya fito daga tasu motar da take takewa tasu Yarima baya ya buɗe masa murfin motar ya fito "Kai tsaye sashin Fulani ya nufa yai sa'a kuwa tana nan part ɗin nata bata shiga wajan takawa ba, zama yayi kan lallausan kafet ɗin dake malale cikin ɗakin yana ɗan rusunawa ya ce "Barka da Hutawa Umma fatan na sameku lafiya" Numfashi ta sauke zuciyarta fal farin ciki yau gata ga Aminunta kusa da ita tsawon shekaru goma kenan daya gudu CANADA yaki dawowa "Lafiya kalau ka same mu One Boy ya gajiyar hanya baka bari mun gaisa ba da safe ka fita ba sanarwa sai da na ce wa JAKADIYA ta kai maka break fast ta dawo ta sanarmin ka fita" "Naje wajan Abbi ne ranki ya daɗe inya koma kafin mu haɗu za'a jima shi yasa nai sakko ayi min Afuwa FILANIN MAI MARTABA" "Anyi maka ONE BOY yaka baro su? ya Hajiya Jamila fatan ka baro su lafiya" "Lafiya kalau" yafaɗa yana bin Juhaina da kallo wacce ta fito yanzu daga bedroom ɗinta "Yaya Ameen barka da Safiya" JUHAINA ta faɗa da wani iri sauti mai jan hankali "Barka dai Juhaina ya school da fatan dai kina kokari sosai" "Inayi sosai ma Yah" "To da kyau Allah ya taimaka, Ranki ya daɗe in Allah ya kaimu gobe zan kaiwa Abokina FAHAD ziyara mun jima bamu haɗu ba fitar safiya zanyi sabida mu isa da wuri" "Allah ya kaimu Ameen amma da kabi jirgi daga garin nan zuwa garinsu FAHAD akwai tafiya fa zaku iya shafe yini guda kuna tafe fa" "Sarkin Mota yace na tafi da Yunusa dogari ya iya tuki sosai" "Cewa zakayi zaku tashi sama, to Allah ya tsare gobe HIDAYA nada manyan baki koda yake nasan ka haɗu da FAHAD sai yanda hali yayi kilama ka kwashe kwana biyu a can batare daka lega wajan HIDAYA ba" "Baza'ayi haka ba insha Allah" yafaɗa yana mikewa tsaye "A huta lafiya UMMANA Zan shiga wajan Mai martaba daga nan zan shiga wajansu Momy Da Mama mu gaisa" yafaɗi haka yana ɗan risinawa alamar girmamawa "Afito lafiya" Umma ta faɗa tana murmushi Washe gari sassafe Prince Ameen ya ɗauki hanya gudun da sukai sosai yasa suka shiga garin bayan sallar la'asar gidansu FAHAD ba bakon gida bane a garesa amma dai a wannan karan ya kasa gano gidan a shekara goma dayai baya kasar harya manta gidan, Prince Ya jingina a jikin motarsa kyakkyawane ajin farko wajan haɗuwa fari ne tas mai doguwar fuska wacce ke ɗauke da dogon hanci irin wanda ake kira da har baka ɗin nan, sumar kanshi wacce take baka kirin tasha gyara sai sheki take da walwali tayi luf luf kwance akan nasa kallo ɗaya zakayi masa kasan ya haɗa jinsi da larabawa, yana sanye da bakar shadda yar gaske mai sheki da walkiya hular kansa tangaran wacce tai matukar dacewa da shaddar jikinsa. Ahankali yake danna tamfatsetsiyar wayar dake hannun sa, fuskar nan tashi murtuk da ɓacin rai yakusa minti goma a tsaye a wajan yana neman layin abokinsa amma bata shuga a karo na karshe yasake kira yayi sa'a wannan karon ta shuga amma harta gama ring ba ba'ayi picking ba, sake jingina yayi da jikin motar shi escape baka mai matukar kyau da tsada, kamar baya so ya buɗe back seat ya zauna yana kallon driver ɗinsa cikin raunananniyar murya ya ce "Yanzu in muka ɗau hanyar komawa gida sai tsakar dare zamu sauka ko, har yanzu bai ɗaka wayar ba nakasa gane gidan" cikeda ladabi driver ɗin Ya ce "Yallaɓai kadai sake gwada kiran kila yana wani uzurin ne shiyasa bai ɗaga kiran ba" Yarima Ameen baiyi musu ba yasake kira saida kiran yakusa katsewa kana aka ɗaga cikeda ɗoki AMEEN ya ce "Hello freind yakake" Daga ɗaya ɓangaran aka amsa da "Lafiya kalau amma ban gane mai magana ba" "Da gaske ka manta ni Al'ameen Muhammad Bello Fu'ad" Wani ihu ɗayan yasaki kamar zai fasa wayar ya ce "da gaske amma naga kamar da lambar nageria ka kirani yaushe ka shugo kasar tamu" Fu'ad yana murmushi yace "Najima yanzu haka ina cikin unguwar ku dai dai asibitin nan amma nakasa gane gidan" "Ok jurani bari na turo a tafi dakai ni ina airport naje ɗakko Daddy da Ummie sun dawo daga cairo bari naiwa Su'ad waya tazo ta karasa dakai gida" "Ok ina jira" yafaɗa tareda kashe wayar yana gyara zaman sa a cikin motar. Ina zaune gaban madubi ina tsara kwalliya ta murnar dawowar Daddy na daga Cairo, nagama saka kayana kenan ina ɗaura ɗan kwali najiyo muryar Mamina daga kicin tana kaɗamin kira, "Su'ad! Su'ad!! Su'ad!!! kina ina ne?" Da sauri na futo zuwa kicin ɗin inda na tarar ta tsaye tana saka lemun data gama haɗawa a cikin frezeer, batare data kalleni ba tace "Ga wayan ki nan kin barta anan tun ɗazu kira ke shugowa" Wayar na ɗauka tareda karawa a kunne na ina murmushi ganin Uncle Fahad ne ke kiran nawa cikeda karaɗi irin nawa nace "yeee su Daddy sun sauka ko" "Kee sarkin karaɗi karki kashemin dodon kunne kije nan bakin layin su kawar ki Ameera akwai abokina dayazo yakasa gane gidan ki kawo sa gida muma gamu nan tahowa tun ɗazun jirgin nasu ya sauka" "Ok" kurum nace masa sannan na kashe wayar na koma ɗakina, yau garin akwai sanyi sosai hakanne yasa nasa jibgegiyar rigar sanyi na mai tsayi da kauri, duk tsayina amma rigar sanyin saida ta kawomin har gwiwa ma saka baby hijab tareda saka plate shoe nafuto zuwa dinning inda na hangi Mami tana shirya warmars a saman danning ɗin. "Mami zanje bakin titi Uncle ya ce yanada bako a can na karaso dashi gida" "Ok saikin dawo karki manta da addu'ar fita, in kuma baki gansa ba ki dawo karki daɗe" "TO Mami" nafaɗa ina fucewa daga third falon zuwa seceound falo, ko'ina kamshi ne kawai ke tashi murmushi nayi ina karasa futa daga first falo, zuwa compound, saida na gaida sojojin dake tsaye baki get kana na futo, seteven na tsokana ta ina zani bayan Daddy yana hanya, dariya kawai nai masa harya buɗemin kofa na futa, ahankali nake tafiya cikin nutsuwa irin tawa kamar yanda nasaba tafiya, mutane dayawa idan sukaga yanda nake takuna sai su zata yanga nake ni kuma sam ba haka yake awajena ba tun tuni haka nake tafiya tun ina yarinya kamar yanda naji Mamina na faɗa idan su Uncle da yaya Jabeer sun tusoni a gaba suna tsokana. Harna karasa inda Uncle Fahad yagayamin banga kowa ba, hasali ko mota ɗaya babu, hannuna nasa cikin aljihun rigar sanyi na na ɗakko wayata na kira Uncle Fahad ina gaya masa gani a wajan amma banga kowa ba, kashe wayan yayi kusan mintina uku wata bakar mota ta faka a gabana Sosai motar tabani tsoro ganinta baka wuluk sai walwali take, glass ɗin motar tinting ne shiyasa baka ganin wanda ke ciki. Kafar sa yafara sakowa waje kafin ya futo gaba ɗayan sa, subhanallah nace a fili ganin yau gani ga balaraben kasar saudiyya sam banyi zaton yanajin hausa ba shiya sa bance masa kala ba, yajima yana kallona kafin naji muryar sa mai daɗin sauraro kamar bayason magana Yace "Are you Su'ad?" ya tambayeni yana taɓe fuska kamar yaga kashi Ina girgiza kaina nace "Yess i Su'ad" taɓe baki yayi kana Ya ce "Amma kika tsaya ɓatamin lokaci dan Allah wuce ki kaini gida" Nidai sakin baki nayi ina kallonsa yanda naji yayi hausa raɗau,kin shuga motar nayi har sanda nafara jiyo jiniyar motar yan sanda motace Hilox baka cikeda yan sanda da bindigogi sai wata farar mota a tsakiya sannan wata Hilux ɗin shake da yan sanda har sun gifta mu naga sunyo baya sun tsaya dai dai inda nake da sauri ɗaya daga cikin yan sandan yadiro daga saman mota yabuɗe murfin karamar motar da suka sako a tsakiya,Yah Mukhutar ya fito daga motar yafara takowa inda nake tsaye, kamewa nayi ina binsa da kallo harya karaso inda nake na sara masa tareda faɗin "Ouwr wellcome sir" "Wellcome Su'ad mai kike tsaye anan wajan" Uncle FAHAD ne ya ce nazo na tafi da bakonsa gida" hannu yaya Mukhtar yabawa bakon balaraben suka gaisa kana ya umarce sa daya shuga motarsa, ni kuma ya tusa keyata zuwa tasa motar inda na tarar da babbar yayarmu Fateema zaune aciki, itama tambayata tayi mai nake tsaye a bakin titi, nabata amsa kamar yanda na bawa mijinta, ba jimawa muka koma gida na shuga ciki hannuna ɗauke da Sajad ɗan Anty Fatima, "Ke kuma ina kika samo wannan yaron" Mami ta tambayeni tana amsar Sajad dake hannuna, kafin nabata masa Daddy ya shugo wani tsalle nayi na ɗane Daddy ina masa sannu da zuwa tareda tambayar sa yaya jikinsa. Ummie dake biyeda bayan Daddy ta daka min tsawa tana faɗin na sakesa banga bashida lafiya ba, niko ko sauraron ta banyi ba naci gaba da makalkale Daddy na da shima yake murnar ganina yana faɗin "Auta me Mamie take baki ne naga kin yi kiba kamar ba keba" dariya nayi ina bin kofa da kallo ganin shugowar Uncle Fahad da bakon balaraben sa, da gani zakasan ba karamin farin ciki sukayi ba da ganin juna ba, nifa har ga Allah mamaki bakon nan ke bani yanda naji hausa raɗau a bakinsa kamar jakin kano😂 yana gaida su Daddy yanda suke amsawa cikin sakin fuska ya tabbatar minda sun san sa, bayan sun gama gaisawa kai tsaye Uncle Fahad yaja hannun balaraben bakon sa suka wuce sashin samarin gidan mu. Mami ce ta umarceni dana kaiwa su Uncle Fahad abinci, nakuwa ɗauka zuwa ɗakin sa suna baje saman bed sai hira suke, nayi sallama na shuga ina ajje warmars ɗin hannuna bakon balarabe ya kalleni kallon dana kasa fassara sa wanda ban cika ganin irinsa awajan kowa inba Uncle ɗina Fahad ba "Wai da gaske wannan Su'ad ce ta girma haka?" bakon ya tambayya yana kallon Uncle Fahad, zama nayi a kan kujera ina kallon Fahad dan naji amsar da zai basa ai kuwa naji yana faɗin "Itace mana kaga tazama yammata ko?" ɓata rai nayi ina kallon Uncle Fahad batare da nace komai ba, nasaba sosai da Uncle Fahad kusan komai tare mukeyi dashi kama daga cin abinci buga kollon kafa ya kaini makaranta ya ɗakkoni, dan duk cikin samarin gudanmu banida Amini kamar Fahad, ganin zaman danai na jiran yazo muci abinci ne yasa yace "Yau inada bako bazanci abinci dake ba kije kuci tareda Daddy ko Ummi" na ɓata rai tareda mikewa ina faɗin "Ai dai bakon naka zai tafi! zaka dawo ka same ni, ni kuma a sannan zan canza Amini na komawa yaya Yazeed" ina gama faɗar haka na fuce a fusace ina bugo masu kofa, murmushi Fahad yayi yana bin Fu'ad da kallo ganin yanda yabi Su'ad da kallo harta futa bai kawo komai a ransa ba yace "Kaganta nan yar rigimar gidan nan kenan haka take hukuma ce ita saida lallashi" murmushin gefan baki Fu'ad yayi batareda ya kalli inda Fahad yake ba yana sauke ɓoyayyar ajjiyar zuciya. Kwanan Fu'ad biyu a gidanmu bana shuga sabgar sa haka shima bai shuga tawa, ko gaisuwa bata taɓa haɗamu ba, haka kurum dai inason ganin sa shiyasa sau tari nake zuwa wajan Uncle Fahad innasan suna tare, wasa wasa nafara gane son bako ya shuga zuciyata. Mami tana zaune a bedroom ɗinta na shuga da sallama zama nayi kusada ita ina wasada zoben hannuna da Uncle Fahad ya kawo min kwanakin baya dayaje Saudiyya umara "Mami wannan bakon balaraben wai a ina Uncle ya samo sa yazo ya zaunawa mutane a gida duk ya hanamu sakewa nida Uncle ɗina" mami kallona tayi tana murmushi "Abokin Fahad ne tun zamanin scoundry harma da jami'a, shekarunsa goma kenan yana CANADA acan yake aiki tun bayan kammala karatun su na jami'a Ƙanin mahaifinsa yasamar masa aiki a can" mikewa nayi na koma ɗakina ina shirin tafiya makaranta yau lacture ɗin yamma nake da'ita, tsab nagama shirina cikin doguwar rigar Atamfa kamar yanda na saba nayi kusan rabin kayana duk dogayan riguna ne acewar Uncle Fahad wai doguwar riga tafimin kyau shiyasa in muka kai ɗinki kannace komai yagayawa telor ɗin amin doguwar riga, tun ina mita harna saba koni ɗaya nakai ɗinki ita ɗin nake cewa amin saboda ina son duk abinda Uncle ɗina keso, kamar yanda shima yake son abinda nakeso, rolling mayafi karami nayi na futo ina baza kamshi, Uncle na tarar a falo shida bakonsa wanda yakafe ni da lumsassun idanuwansa kamar na maijin barci, harna karaso na zauna hannun kujerar da Uncle ke zaune akai "Kinyi kyau besty irin wannan tashin kamshi haka sai ina?" "Uncle inada lacture yau na shirya ka tashi ka kaini" "Besty futa nakeson nayi a hospital inada feshan amma bari na ajje ki inyaso in kika tashi zansa Seteven ya ɗakko ki" mikewa mukai atare muka jera zuwa wajan adana motoci na gidanmu. Ahankali Uncle ke tukin motar kamar bayaso yanayi yana kallona wani bin yayi murmushi wani bin ya kashe min ido ɗaya nidai bance masa komai ba harya ajjeni cikin school ɗinmu yana ɗagamin hannu har yabar harabar makarantar tamu, jinai an ruko hannuna na juya da sauri ina kallon kawata Ameera dake min dariya Tace "Nakasa gane maku keda Uncle Fahad kamar wasu masoya ko yaushe kuna tare jibi yanda yake wani ɗaga maki hannu yana kashe maki idanu kamar yana gaban budurwar sa" dariya nayi tareda soma tafiya ina faɗin "Ina kikaga Amini ya koma masoyi akwai abota mai karfi a tsakaninmu shiyasa kowa yake mana kallon masoya amma ni sam bama haka da Uncle, ban taɓa masa kallon masoyi ba yanzun dai na faɗa soyayya wacce nake zaton zata wahalar dani danna ɗakko da zafi" har muka gama lacture na futo zuciyata makale da tunanin bakon Uncle, zuciya da ruhi na ɗokin komawa gida nayi tozali da kyakkyawar fuskarsa mai cikeda annurin dake sanyaya zuciyata, wajan dana hango motar gidanmu na dosa kofar baya naketa kokarin buɗewa amma taki buɗuwa sai ta gaba dana ga anbuɗe min da sauri na shuga duk azatona Uncle ne saida na zauna ina buɗe jakata batare dana kalli wanda ke ciki ba nace "Uncle amma kayi saurin dawowa" jin baice min kala ba yasa na ɗago ina kallonsa, kallon kallo mukai ido cikin ido ni nafara ɗauke idanuna daga cikin nasa tareda sauke ajjiyar zuciya take wata kasala ta rufeni, nai saurin ɗora kaina saman seat na motar na lumshe idanuna ina jin yasoma tafiya da motar munyi tafiya mai nisa naji yayi parking gefan titi sai sannan na buɗe idanuna ina kallon sa, hannunsa duka biyun yana saman stearin motar yayinda ya ɗora kansa saman sitiyarin yana kallona da lumsassun idanun sa masu samin kasala kamar bayaso yasoma magana da muryar sa mai matukar daɗin ji da sauraro kamar baya so "Ke bakya yiwa mutane magana saidai kirinka azabtar da zuciyar mutum!" da sauri na ɗago na sake kallonsa kashe min ido ɗaya yayi tareda ɗage gira, da murmushin sa daya doki zuciyata, bance masa kala ba saima gyara zamana danai "Kinsan yanda nakejin zuciya ta kuwa?" zuciyata bugawa take ko wanne bugun numfashi yana bugawa da sonki da kaunarki!, Su'ad hakika zuciyata tayi sartse da kaunarki ina sonki! ina sonki Su'ad!!, da sauri na ɗago ina kallonsa dan tabbatar da gaske bakon Uncle ne ke gayamin yana sona....✍️ Free book ne idan kinbi link baiyi ba kimin magana kai tsaye ta wannan lambar 07039793439 ki save Number ta da Mamie Yusuf Daboo [6/4, 7:46 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA* 🌹 Story and Writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 2-3 Kafin na gama tantance shin da gaske daga bakin Fu'ad maganar ke futowa na kuma tsinkayo miryar sa yana cewa "Ki tausayawa jaririyar zuciyata ki amshi soyayyarta na taɓa soyayya a can baya da wata wacce na mato a kanta kullum mafarkina da burina shine tazama matata ashe ita ba da gaske take sona ba yaudara ta take sai daga baya naji labarin auranta da wani bani ba! ni bana yaudara ba kuma nason a yaudare ni, mutum ne ni kaifi ɗaya idan nace E! to bazan taɓa canzawa ba nace a'a, Su'ad dan Allah karki yaudare ni in kinsan kinada wanda kikeso karki ɓoyemin zuciyata bata iya soyayya ba in inason abu haukan so nake masa So nake masa bana wasaba, kaunarki ta shugeni tun kallon farkon danai maki Su'ad" Tsit nayi a zuciyata ina tunanin Shin wai wacce amsa zan bawa Uncle Fu'ad shin na amshi soyayyar sa kona ja aji, batare dana gama shawara da zuciyata ba najiyo ina magana "Ina sonka Uncle Fu'ad nima dan Allah karka yaudare ni ban taɓa soyayya ba banma taɓa yin saurayi ba ko yaushe idan wani yazo wajena Uncle baya bari ya kuma dawowa yace yafison nayi karatu mai zurfi kaima na roke ka muyi soyayyarmu cikin sirri karka bari ya sani!" "Bakida matsala dani bazan taɓa bari Uncle ɗinki yasani ba nidai fatana ki soni sona gaskiyya! ina mai tabbatar maki auranki zanyi nan bada jimawa ba" sosai muke soyayya da Uncle Fu'ad munyi wata iriyar shakuwa musamman a waya mukan ɓata lokaci muna waya musamman cikin dare inda muke musayar kalaman soyayya, zuciya ta tuni ta narke a kaunar Fu'ad ta yanda nake jin inban aure shi ba bazan taɓa iya zaman aure da wani ba, gaba ɗaya na basa dukkan soyayya ta. Ina kwance cikin ɗakina Uncle Fahad yashigo yasha kwalliya cikin shadda ruwan zuma ya ɗora farar rigar su ta likitoci a saman kayan sa hannunsa na rikeda wayoyinsa ahankali yake bubbuga fulon danake kai, buɗe lumsansun idanuwa na nayi wanda suka rune da barci turo baki gaba nayi tareda gyara kwanciya ta "Ni maizan maka wai Uncle?" kallon agogo yayi yana nunamin "Kalli mana na makara fa tun ɗazu ke nake jira baki futo ba" saida na kuma gyara kwanciyya ta sannan nace "Yau banida lacture kaje kawai" ina kallonsa yafuta yanamin wani kallo da ako yaushe shi nake gani akan fuskarsa harya fuce yana murmushi. Karar shugowar sako cikin wayata yasa na tashi ina dubawa dan azatona Uncle Fu'ud ne ilai kuwa shine yake sanar dani yana garden mu haɗu acan, a gurguje na shirya ina kallon agogo sha biyu saura kwata, harna futo na koma na sako rigar sanyi saboda wani sanyi danaji anayi ga iska tana busawa, ahankali nake takawa har na shuga garden ɗin tun daga nesa na hangosa ya haɗe sosai cikin kananun kaya jan wando sai farar shart daya ɗorawa rigar sanyi mai haɗe da hula itama ja mai farin layi layi wayarsa yake dannawa harna karaso baisan nazo ba saida nayi gyaran murya, a hankali ya ɗago kyawawan idanuwansa yanamin wani shagalallan kallo mai haɗe da murmushi, ni gaba ɗayama Fu'ad mamaki yake bani yanda yake wani narkemin in muna tare, kiran daya shugo wayarsa ya katse masa maganar dayai niyar yi yana mirmushi yai picking call ɗin, banji mai a kace a ɗaya mangaranba sai shi danaji yana faɗin "Oh Khady ba haka bane kinsan dai yanda muke dake, ina kano akwai abinda ya rikeni shiyasa ban dawo ba amma ina hanya gobe indai haka zai faranta maki rai" bai kara cewa komai ba yakashe wayar yana kallona ganin yanda na haɗe rai, "Ran hukuma ya daɗe wannan fuskar shanun fa" kwafa nayi ina gyaɗa kai nace "Wacece Khady?" "Au shine abin fushin Khady kanwa tace mu biyu kaɗai mahaifiyarmu ta haifa, kafin Allah yai mata rasuwa ina matukar ji da Khady kasancewar bata da kowa a kasar nan mahaifiyarmu yar kasar sudan ce ta haɗu da mahaifina Alhaji bello a jami'a lokacin yana malamin makaranta a jami'ar su sunyi soyayya sosai dashi kafin maganar aure ta shuga tsakani, kakana wanda ya haifi Abbunmu shine sarkin garinmu su biyu jal ya haifa shiyasa yake matuwar son ya'yansa da basu duk abinda suke so shiyasa a sanda yaji labarin soyayyar Abbi da Ummu takanas yatashi zuwa Sudan bai dawo ba saida ya tabbatar an ɗaura masu aure sannan yabaro su acan yadawo, shekara biyu da auran Allah yaiwa mai martaba rasuwa hakan yasa Abbi suka dawo nageria lokacin ina ɗan shekara ɗaya, ankai ruwa rana akan naɗin sarauta inda majalissar sarki suka zaɓi Abbi shi zai maye gurbin mahaifinsa sam shi dama can baya ra'ayi sarauta, cikin dare ya lallaɓa sukabar gida shida Ummu dani ba'a sake jin labarin suba saida aka naɗa kanin Abbu ɗinmu sannan suka dawo, shekarata goma sha biyar lokacin muna secaundry nida Fahad aka haifi Khadija nayi murna sosai lokacin da muka koma gida muka tarar Ummu ta haihu, nida Fahad mun shaku sosai shakuwarmu tasa ko hutu akai tare muke tafiya gidanmu muyi rabin hutunmu acan sannan muje gidansu mu karasa hutun a can shakuwarmu ta zarce Abota tazama aminta, a shekarar da muka gama Secaundry Allah yaiwa Ummuna rasuwa sakamakon haihuwa datazo yi Allah baisa zata haifi abinda ke cikinta ba suka koma tare! munyi kuka kamar bazamu daina ba nida Khadija da Fahad, awannan yanayi Abbansu Fahad ya ɗaukemu yakaimu Rasha karatau acan mukayi karantu likita, bamu taɓa komowa gida ba har saida muka kammala karatu watanmu biyu da dawowa nan ma Allah yaiwa Abban su Fahad rasuwa, nadawo na samu Abbunmu yayi aure kawar Ummu wacce tunda tazo nageria batada aminiya sama da'ita, sosai take azabtar da Khadija ni kuwa daman ba zaman gidanmu nake ba ko yaushe ina tareda mai martaba kanin mahaifina acewarsu nine yarima mai jiran gado saboda mai martaba bayada ɗa ko ɗaya ya'yansa duka matane, shiyasa ko yaushe muna tare, awannan lokacin Fahad yayi aure ni kuma na wuce Canada inda naci gaba da karatu bayan na kammala na sami aiki acan shekaruna goma acan ban sake waiwayar gida ba inadai bincikar rayuwar Khadija wacce nasa matar mai martaba Umma ta ɗauketa ta maidata wajanta, Umma nada kirki ita kullum mukewa kallon uwa mahaifiya wacce bata ɗauki lamarin mu da sauki ba, ko kafin rasuwar Ummu akwai aminta mai karfi tsakaninta da Umma idan bakasani ba ka ganmu tareda Umma bazaka taɓa zaton ba ita ta kawomu duniya ba duk da wasu na mata kallon da wata munufa take nuna mana so". Sosai Fu'ad yabani tausayi ganin yanda yake goge kwalla tabbas rashin uwa babban rashine daba kowane ke ganewa ba sai wanda yarasa tashi Cikeda tausayawa nake kallonsa nama kasa cewa komai, kiran sallar damukaji yasa muka mike atare zuwa cikin gida, da yaya shareef naci karo abakin kofa ya harɗe hannu yana kallona fuskarsa babu walwala yace "Ke meke tsakaninki da AMEEN Fu'ad" ɗan ɗagowa nayi na kallesa yasake haɗe rai yana kallona nace "Ba komai kawai naje garden ne nagansa shine fa mukayi hira" wucewa yayi da'alama daman masallaci zashi ganinmu dayai tareda Fu'ad yasa ya tsaya tambayata, kai tsaye ɗakina na wuce wanda ke manne dana mami na, kasancewar ina priod yasa banyi alwalaba na kwanta saman gado. Alhaji Usman karaye shine mahaifina haifaffan garin karaye ne, makarantar allo yakawo sa cikin garin kano inda bayan yasauke kur'ani ya shuga makarantar boko, wanki da guga yake shiya rikesa harya kammala pramary da sceundry, anan karatun nasa ya tsaya saboda awancan lokacin ba abune mai sauki ba shiga jami'a kusan sai kanada hanya sannan zaka samu shuga, Alhaji Usman ya haɗu da wani tsohon soja dayake kawo masa wanki sun saba sosai ta yanda har gidansa yakanje anan ne yake gayawa Genaral Aliyu cewa yana son shima yazama soja amma bayada hanya, haka Genaral ya shuge masa gaba harya sami damar tafiya makarantar horar da sojoji dake kaduna, bayan kammalawar sa aka tura sa aiki can jos, Genaral yaɗauki babbar yarsa ya aurawa Usman, Allah ya jarabci Alhaji usman dason matarsa Amina wacce keda tsananin biyayya gatada kirki, Alhaji Usman yataka mukamai na soji da dama ya zauna a garuruwa sosai, shekarunsu goma da aure da matarsa Amina amma bata taɓa haihuwa ba, ko kaɗan hakan bai damesa ba saboda son dayakewa Amina bayajin zai iya haɗata zama da wata ɗiya mace, gwaggo mahaifiyar Kanol Usman ita ta takura masa lalle saiya kara aure inba hakaba wlh saiya saki Amina, cikin haka Allah yahaɗa kanol da Dr Baseera Wali wacce ke aiki a babban asibitin kasa dake JOS, ya nuna sha'awar auranta saboda ya lura itama tanada saukin hali, watan Baseera goma a gidan Kanol ta haifi yarta mace kyakkyawa mai matukar kama da'ita ranar suna yarinya taci sunan Gwaggo waton Fateema, shekara biyu tsakani Baseera tasake haihuwar ɗa namiji Jabeer sannan Shareef daga nan haihuwar ta tsaya mata har sannan hajiya Amina bata haihu ba, ko kaɗan rashin haihuwar bai dameta ba ta dogara ga Allah tasani shike bada haihuwa, iyayanta ma saida suka jima kafin suka haifeta tana scoundry sannan aka haifi FAHAD Yaran gidan Kanol sun taso kansu a haɗe bazaka taɓa gane cewar Baseera ce ta haifesu ba, Baseera suna kiranta da Ummi yayinda Hajiya Amina sukr kiranta da Mami, shekarun Shareef goma Ummi tasake haihuwar ya mace ranar suna yarinya taci sunan Hajiya Amina suke kiranta da Su'ad ba karamin gata Su'ad ke samuba awajan Mami itace komai nata kusanma awajanta take sai shan nono ke kaita wajan Ummi koda aka yaye Su'ad gaba ɗaya Ummi ta barwa Mami Su'ad, Fahad kanin Mami ba karamin so yakewa Su'ad ba ko yaushe yana tareda ita, shekarun Su'ad goma sha biyu Fahad ya auri yar wan babansa bayan rasuwar mahaifinsu Genaral Aliyu, Kanol Usman da Ummi yanzu haka suna zaune a kaduna inda Ummi ke aiki shima Kanol acan yake aiki, Mami da yara suna zaune a kano saboda Su'ad dake makaranta da kuma su yaya Jabeer dake aiki, tuni anyi bikin Yaya Fateema tana auran babban ɗan sanda suna zaune anan kano. Su'ad dake shirin yin barci taga shugowar Fahad ɗakinta, saida ya zauna saman stool kana Yace "Naga abincinki baki ciba, Ummi tace yau gaba ɗaya bata ganki ba ina kikaje" turo baki gaba tayi dan in tana gaban Uncle ɗin nata gaba ɗaya narkewa take ta koma karamar yarinya, shi kuma yayita biye mata tana zuba masa shagwaɓa da shiririta "Nifa Uncle yau ba kalar abinda nakeso ba akayi, kuma ai Ummi tasan bansan kunun gyaɗa da doya shine tayi ni bazanci komaiba yau" tafaɗi haka tana gyara kwanciyarta, "Wacce irin maganace haka Besty amma dai kinsan banson ki zauna da yunwa ko yanzu fa har karfe biyu bakici komai ba, kinga tashi gayamin mai kike son ci saina saka a siyo maki" da sauri na mike na zauna saman gadon ina murmushi kafin nace "Nifa Uncle kawai ka kaini nayo take away chips nakeson ci da shawarma sai meat pie da Peach mai sanyi" dafe kansa yayi yana kallonta kafin yace "Oh Su'ad nagaji dayawa yau mutum biyu naiwa cs yanzu haka gudowa nayi nazo na huta kuma ki sani na sake futa, bari kawai nabawa Seteven yasiyo maki" komawa tayi ta kwanta tana ɓata rai ahankali take mita "Shikenan kaje ka kwanta ɗin aidaman nasan basona kuke ba yan gidan nan ace na wuni banci abinci ba amma ba wanda ya damu dani, dan anga Mami da Daddy basa nan ne aida ko shi nasan zai kaini naci abinda raina keso" Fahad zama yayi gefan gadon yana cewa "Kinga bafa wani abun damuwa bane wane yace maki bamu damu dake ba, yanzu dai bari naje nayi wanka nazo na kaiki kici abinda ranki keso, kema ai kinsan bama haka dake farin cikinki ai shine nawa koba hakaba yar Uncle" yafaɗi haka yana kashe mata ido ɗaya, gabanta ne yai wata irin faɗuwa saboda ganin kallon dayake mata wanda baida maraba da irin wanda Fu'ad ke mata ako da yaushe, Bayan yayi wanka yazo suka fita tare basu wani jimaba suka dawo gida Su'ad tare suka shugo gida da Uncle Fahad, shike rike da ledojin da tayo siyayya, tsakiyar falon ta baje taci wancan taci Ummi da yaya shareef na kallonta ba wanda ya kulata harta gama ta wuce ɗakinta. AMEEN sosai yakejin daɗin zaman Kano tun washe garin randa yazo yacewa Yunus ya koma gida inzai komo zai biyo jirgi ko fita zaiyi shi kaɗai ke fita a motar FAHAD sau biyu yana kaiwa HIDAYA ziyara suyi hira sosai yai wasa da yaranta sannan yadawo gidansu Fahad kusan baida matsala da kowa a zamansa na gidan, sosai Ameen keson rayuwa irin haka ta ba ruwan kowa da kowa ba kamar suba a masarauta ko ina zaka kana tareda rakiyar fadawa shi yasa ya kwashe sati biyu a garin kano kafin ya saka ranar tafiya, karfe goma na safiyar Ranar Lahdi Fu'ad yagama shirinsa na komawa garinsu, har sannan baiga futowar Su'ad ba, har sun gama sallama da Ummi sun futa compound yanata waige waigen inda zaiga Su'ad ta fito harya shiga mota yahangi futowarta lokacin Fahad na kokarin tasar mota, da sarsarfa ta karaso wajan tareda buɗe back seat ta zauna, Fu'ad ya sauke wata nauyayyar ajjiyar zuciya wacce har Fahad ya kallesa batare dayace komai ba ya juya yana kallon Su'ad "Daman kinada lacture amma baki shirya da wuri ba sai yanzu, bayan nagaya maki karfe goma zankai Fu'ad airport" cuno baki tayi gaba kana ta ce "Aini dai rakaka zanyi banason zaman gidan nan gaba ɗaya su Ummi basa son gani na dan anga Mami bata nan kowa baya kulani kaima duka ka canza min yanzu ba ruwanka dani ko kaɗan baku rike amanar da Mami ta baku ba Allah ma yasa yau Mami da Daddy zasu dawo" Fahad tasar motar yayi batare dayace komai ba ya girgiza kai kawai yana yaba rigima irinta Su'ad yafara tafiya gate man ya buɗe mana kofa muka futa, saida Fahad ya fara tafiya saman kwalta sannan na futo da wayana na kunna data sakon Fu'ad shiya fara shugowa na buɗe da sauri ganin yana online _"Princess kinyi kyau! bakiji yanda naji zuciyata ba dana ganni cikin mota zan bar gari batare dana ganki ba"_ _Tayaya zan bari farin cikina yatafi batare dana sake ganin saba zanyi kewarka_ ɗagowa yayi yana kallona ta madubin motar yakashe min ido tareda murmushi mai narkar da zuciyar masoya, haka mukaita musayar zafafan kalamai nida Fu'ad har muka karasa airport ɗin, zama mukayi muna jira sai nan da minti goma sha biyar jirgin da zaije garinsu zai tashi, Uncle Fahad ya zuba mana ido yana murmushi yace "Duk kun ɗauki waya kunata chat kun manta dani awajan, Su'ad dawa kike chat ne?" FAHAD ya aika mata da tambaya yana kokarin leka screen na wayar tai saurin kifa wayar a kan cinyarta kana ta basa amsa "Da Ameerah" Fu'ad ma wayar ya ajje suna ɗan taɓa hira har jirginsu yatashi raina duk ba daɗi haka muka koma gida. Da yamma ina zauna inda nasaba zama na cikin gidanmu wata yar rumfa ce da'aka kawatata da shuke shuke kala kala wajan yanada daɗin zama ga iska dake kaɗawa, kamshin wajan kawai ya'isa yaja hankalin mutum ya zauna, Uncle Fahad ne yakaraso wajan cikeda damuwa yaja kujera ya zauna kusa dani yajima yana kallona batare da yace komaiba na kula yana cikin damuwa hakan yasa nace "Uncle lafiya kake kuwa" ajjiyar zuciya yasauke a fili tareda saka hannunsa ya shafi sumar kansa kana ya ce "Besty ina cikin damuwa sosai, wata yarinya nakeso amma narasa ta hanyar da zanbi na faɗa mata ina sonta, tsoro nakeji gani nake kamar bazata soni ba, besty bani shawara bakiji yanda zuciyata take kaunar yarinyar ba" saida nayi dariya sosai sannan nace "Wacce mai sa'ace wannan da har Uncle ɗina yake shayin gaya mata yana sonta! kasan me kafuto kawai ka faɗa mata na tabbata zata soka, kai kasan yanda ka haɗu kuwa ko wacce mace zatayi farin ciki ace namiji kamar kai mai tarin ilimi hankali da nutsuwa babban likita yace yana sonta na tabbata komai takeji dashi kafita, bama haka ba mazai hana kasami mahaifinta ka gaya masa kanason yarsa yabaka dama ka gana da'ita kaga shikenan in yayi na'am dakai itama dole tabi" kai kurum ya girgiza batare dayace komaiba yabar wajan. Prince AMEEN Fu'ad lafiya yasauka airport na garinsu manyan motocin masarauta daya gani cikeda airport yasa ya dafe kansa cikeda damuwa yake takawa, Allah yasani baiso mai martaba yasan da dawowarsa ba shifa sam bayason rayuwar nan ko yaushe yana kusada sarki Allah ya sani baya ra'ayin sarautar nan, yana kokarin guje masu yaji muryar Chiroma yana dariya yace "Barka da zuwa magajin sarki" Fu'ad dafe kansa yayi🤦‍♂️ cikeda damuwa yake kallon Chiroma yace "Kaine ka gayawa Mai martaba yau zan dawo ko?" hmm yayi kwafa tareda cikin jibgegiyar motar da Sarkin mota ya buɗe masa, tafiyar yan mintuna takaisu gidan sarki, sosai ake murna da zuwansa musamman Deejah da Juhaina nan ya baje cikinsu sai surutu suke masa da kyar yasamu ya zille zuwa sashinsa na gidan mai martaban. Kanol Usman na zaune cikin falonsa Fahad yai sallama cikeda ladabi yazauna saman carfet yana gaida Daddy sannan ya sunkuyar da kansa yana wasada yan yatsun kafarsa yafara magana muryarsa na rawa "Daddy daman ina son na ce" yanda yake magana a rarraɓe yasa Daddy yadakatar dashi da faɗin "Nutsu Fahad gayamin damuwarka kai tsaye yanda zakai magana da Amina kullum ina gaya maka karinkamin kallon nine yayanka ba Amina ba ina jinka" kasa Fahad ya kumayi da kansa kana yace "Daddy daman sonake kamin izini inason Su'ad sona gaskiyya inhar ka amince auranta zanyi! nafara zuwa kamin izini na nemi amincewarta" Daddy farin ciki ya lulluɓe zuciyarsa shi daman yadaɗe yana wannan hasashan cikeda farin ciki yace "Nabaka Su'ad Fahad na tabbata kai mai kaunarta ne, fatana ka rikemin ita amana kabata kulawa ko bayan raina! basai kayi mata magana ba kabarni da'ita kawai gobe insha Allah zanje karaye muyi magana da Baba Sunusi zan tsaida ranar auranku banason aja lokaci burina daman ako da yaushe naga na aurar da Su'ad kafin Allah ya karɓi raina kasan yanayin cutar danake fama da'ita ba lalle nasake shekara nan gaba a raye ba" Kanol yakarasa faɗa cikin damuwa "Insha Allah Daddy zama ka wuce hakan ai kanabin ka'idoji kuma kana kan magani" murmushi Kanol yayi tareda maida kansa saman kujera yana lumshe ido shi kaɗai yasan maiyakeji ajikinsa a jiya zuwa yau daya dawo Kano shi kaɗai yake jin matsanancin ciwon da cikinsa keyi.......✍🏻 07039793439 [6/4, 7:46 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA* 🌹 Story and Writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 5&6 Kanol yashuga ɗakin Ummi da murmushi a fuskarsa, Ummi dake tsaye jikin madubi tana shafa humra tajuyo cikeda mamaki tana kallonsa, ba kasafai ya cika shugowa ɗakin matansa ba kusan saidai su samesa a samansa, ajje humran tayi tazo kusa dashi gefan gado ta zauna, jawota yayi jikinsa suka kwanta saman gado yana dariya "Kanol da'alama yau kana cikin nishaɗi gayamin maiya saka farin ciki haka" sake rukota yayi jikinsa yana murmushi "Abin farin ciki yasamemu Dr yanzu Fahad yake gayamin yanason auran Su'ad harma nayi wayada Baba sunusi mun tsaida rana nan da sati huɗu masu zuwa gobe ma zanje karaye mu sake tattaunawa, ni uban ango shi uban amarya" Ummi da itama daɗi ya kumeta tasake kankame mijin nata tana faɗin "Kai naji daɗin zancan nan sosai Allah yasanya albarka amma Mami bata sani ba", "E sai gobe zan gaya mata na shuga ɗakinta naga sunyi barci itada ɗiyar tata" anan Kanol yai shirin kwanciyar barci Ummi tana mitar yatashi su koma samansa yace "Dan Allah Dr kibarni na kwana anan daga yau fa shi kenan bazan sake kwana anan ba" shuru tayi kawai taja masu bargo suka koma suka kwanta. *MUTUWA YANKAN KAUNA* Lafiya kalau Kanol ya kwanta bayan yasha magungunan sa, amma cikin dare wani azababban ciwon ciki ya turnike sa sai murkusu yake tun yana iya daurewa harya tashi Ummi dake barci, ganin halin dayake ciki gaba ɗaya hankalinta yatashi ta gigice tama kasa basa taimako, Fahad taiwa waya sukazo shida Jabir suka garzaya asibiti, Su'ad da Mami basusan Kanol ba lafiya ba saida safe sukaje asibitin, lokacin yaɗanji sauki ba kamar sanda aka kawo saba, Su'ad na rikeda hannun Daddynta tunda suka shugo take hawaye shidai Kanol kallonta kawai yake yana girgiza mata kai alamar tai shuru, "Yi shuru Autata daina kukan haka nafa ji sauki Fahad yana shugowa zance ya sallamemu mu koma gida ko haka kike so" kai kurum Su'ad ta girgiza masa, shafa kanta yayi yana faɗin Allah yai maku albarka ya albarkace ku gaba ɗaya" shugowar Fahad yasa Kanol cewa "Yauwa maida Auta gida zamuyi magana da su Mami kici abinci ki wanka anjima saiki dawo ki tahomin da fatan dankali" kai Su'ad tasake gyaɗawa haka kurum takejin jikinta duk ba daɗi, jiki a sanyaye tamike zata futa, ta juyo tana kallon Kanol daya rike hannun Fahad duk da bata jiyo abinda Daddyn yake faɗa haka kurum take zaton maganarta yakewa Uncle ɗin"Ga amanar Su'ad nan na damka a hannunka itace karama kabata kulawa kabata duk wani farin ciki na rayuwa kada kabari ta koka ko bayan raina" Fahad yace "Insha Allah Daddy zanyi abinda kake so Allah yabaka lafiya" Ameen ya furta saman laɓɓansa kana muka fita daga ɗakin, Kanol ya kalli Mami yana murmushi "Kuyi hakuri banjin wannan ciwon nawa na tashi ne! kuyafemin ga amanar yarana nan na damka a hannunku kuci gaba da basu ingartacciyar tarbiya kamar wacce muke basu ina raye, dan Allah kada kubari wani ruɗe na duniya yasa ku raba kanku kuci gaba da haɗe kanku kamar yanda kuke ayanzu, sannan Su'ad na bawa Fahad ya aureta ko bayan raina kuka canza ban yafe ba! da sauri Mami ta kalli Kanol "Abban Su'ad yazakace haka su yaran sukace maka suna son junansu shakuwa ce kawai fa a tsakaninsu ba soyayya, inma shi Fahad sonta yake to ita Su'ad tanada wanda ta..."Umarni na bayar lallene acikan burina ko bayan raina! "Kanol dan Allah kayi shuru cuta fa ba mutuwa bace, kabari inkaji sauki saimu tattauna" murmushi kawai yayi yana kallon Ummi data kasa magana hawaye kawai take, Kanol ya lumshe idanu yana faɗin "La'ilaha illallah muhammadan rasulillah" azabure Ummi ta ɗago tana kallonsa ganin yanda hannunsa dake cikin nata yasaki, wata kara tasaki haɗeda salati itama nan ta zube, dai dai shugowar Fahad daya dawo daga gida dan ganin yaya jikin Daddyn turus yayi ya tsaya bakin kofar ɗakin yama kasa shugowa, Mami ke salati tana girgiza Ummi datake zaton itama mutuwar tayi, "Fahad ka tsaya anan karaso ciki ka bata taimakon gaggawa Daddy yau Allah ya amshi abinsa, hasbinallahu wani'imal wakil" azabure fahad yashugo ɗakin yasoma tattaɓa Daddyn saida ya tabbata rai yayi halinsa kana yasa Mami ta ɗora Ummi saman gadon dake kusa dana Daddy yasoma bata taimakon gaggawa, a firgice ta farka dai dai shugowar Fatima da sai sannan taji Daddy bayada lafiya, ganin mutum lulluɓe da farin yadi yasa Fatiman ta buɗe yanayin dataga Daddy yatabbatar mata baya lumfashi luuu tayi baya zata faɗi mijinta ya rukota ta faɗa jikinsa tana fashewa da kuka, Fahad da kwamishina su suka jajirce kan gawar Kanol aka gama haɗasa suka ɗaukesa zuwa gida dan masa sallah akaisa makwancinmu na gaskiyya😰 *Su'ad* Sauri sauri nake na kammala fatan dankalin da Daddy yace nayi masa ko wanka banyi ba haka kurum duk nakejin jikina yai wani irin sanyi, na zuba dankalin kenan naji wata faɗuwar gaba tareda kara haɗida salati kamar muryar Yaya Shareef nakeji shiyasa na futo daga kicin ɗin da sauri kamar zan faɗi na nufi compound na gidan inda nake jiyo hayaniya, nima salati na saki ina kamewa awaje ɗaya saboda abinda idanuna suka ganemin, wata irin girgiza nayi sai gani gaban motar na rirrike Uncle Fahad ina kuka kamar raina zai futa, Rukoni yayi sosai yana goge hawayan fuskarsa yama kasa cewa komai, hannuna yaja muka shuge cikin gidan ɗakinsa yakaini ya zaunar dani gefan gado shima ya zauna har sannan hawaye ke zuba daga cikin idanunsa yabuɗe baki zaiyi magana kawai yafashe da kuka, sosai yake kuka yanda yake kukan zakasan mutuwar ta taɓa masa zuciya, cikin kuka yake lallashina "Muyi hakuri! bamuda yanda zamuyi inama wani yana fansar wani dana mutu Daddy ya rayu, tabbas munyi babban rashi Su'ad dabazamu samu madadinsa ba" mikewa yayi ganin yanda na haɗe jikina waje ɗaya ina kuka dukkan ilahirin jikina karkarwa yake allura yake shirin yimin na ɗago ina kallonsa "Uncle mai zakamin allurar barci please dan Allah karkamin kabarni naga Daddy na nai masa kallon karshe nai masa addu'a", ajje alluran yayi muka futa falo tuni mutane sun fara taruwa, kasancewar juma'a ce ana idar da sallah a masallacin unguwarmu aka sallaci gawar Daddy munaji muna gani badan ranmu naso ba aka kai Daddy makoncinsa, mutuwar Daddy gaba ɗaya ta canzar rayuwata nazama wata slent sam ba rigimar nan dana saba bana komai sai karatun kur'ani dan tuni Mami ta takamin burki da yawan kukan danake, tace ba abinda zai amfanarwa Daddy saima azaba da zanja masa, Fu'ad yazo tun randa akayi matuwar dashi aka sallaci Daddy, yan uwansa ma sunzo sosai harda Umma da mai martaba, Abbi ɗinsa ne baya nan a waya yamin ta'aziya nai mamaki sosai yanda yan uwansa suka san dani, hatta babbar y'ar mai martaba Hidaya wacce ke auran sarkin garinmu saida tazo mana gaisuwa. Rasuwar Daddy ta canza rayuwar jama'ar gidanmu baki ɗaya kowa yazama ustaz sai ahankali muka saba da rashin Daddy tuni kowa ya koma bakin aikinsa, yaya sharif ya koma kaduna inda yake aiki domin shima soja ne sai yaya Jabeer dake aikin banki nida Yazeed mun koma makaranta ni ina shekara ta biyu shi kuma yana shekarar karshe, duk fanni ɗaya muke karanta low. Watan Daddy ɗaya da wani yammaci ina zaune falo na biyu wata mata tayi sallama ta shugo duka shekarunta bazasu wuce ashirin da biyar ba yanda take wani kalle kalle yasa nima nake kallonta kamar na santa amma na manta inda na santa, ta zauna saman kujera kamar bataso tacemin "Hajiya Amina tana nan kuwa?" kamar nace mata bata nan ganin tambayar rainin hankalin dataimin mutanan dake takaba ina zasu futa wata unguwa, bance mata komaiba na mike na shuga ciki danna kira Mami, tare muka futo da Mami da Ummi jin danai Mami tace "A lale da zuwa Zainaba daman kece?" ɗan shuru tayi kana ta gaida su mamin, jin danai ance Zainaba yasa na gane inda nasanta matar Uncle Fahad ce wacce suka rabu dashi shekaru biyar kenan, Ummi ke tambayar ina "Ameera yammata yanzu nasan ai ta girma" bata bawa Ummi amsaba sai dariya da tayi kawai tana nan har Uncle Fahad da yaya Jabeer suka dawo, ko zama Uncle baiyi ba bayan sun gaisa tai masa gaisuwa ya wuce ɗakinsa, bin bayan sa nayi yana tsaye cikin ɗaki harya fara rage kayan jikinsa yarage daga shi sai dogon wandon shadda sai farar singileti yana kokarin cire dogon wandon ni kuma nayi sallama na shuga kai tsaye, jin sallamata yasa ya juyo yana kallona yaɗan ɓata rai yana cewa "Banace ki daina shugomin ɗaki kai tsaye haka ba, kina fara neman izini tukunna" nidai bance masa komaiba na zauna gefan gado ina cewa "Uncle wai maiyasa bazaka maida Zainaba ɗakintaba kodan Ameera ma dake tsakaninku" ɓata rai yayi yana kallona ya ce "Kintaɓa ganin inda mutum yazauna da makiyinsa" turo baki gaba nayi ina cewa "Tayaya masoyi zai koma makiyi baka sonta daman ka aureta harda yara" zama yayi nesa dani kaɗan yadafe kansa yana magana. "Bantaɓa son Zainaba ba, Mahaifinta wan mahaifi nane shiya ɗauramin aure da ita nazauna da'ita zaman amana, duk da inada wacce zuciyata keso tun tana jaririya amma haka na danne son na zauna da Zainaba da zuciya ɗaya, ashe itada mahaifinta suna da wata manufa akaina, mun haifi yaranmu guda biyu Abdallah shine babba sai mariya damuke kira da Ameera saboda sunan mahaifiyata dataci! acan baya bayan matuwar mahaifina yayan babanmu ya auri innarmu ashe shi da biyu ya aureta saboda ya kwace duk dukiyar da Abbanmu yabar mana nida Mami, Innarmu ta gano haka saita gudu garinsu ta damkawa mahaifinta duk kanin takardun kadarorinmu sannan ta dawo gane ba komai a wajanta da baba yayi yasa ya rinka wulakanta ta har Allah ya amshi ranta!😰 bayan rasuwarta kakanmu yabamu duk wasu takardunmu Mami ta adana mana, wata rana bayan aurena da Zainaba na dawo daga hospital ranar agajiye na dawo gajiya tasa bana kojin yunwa, ina zama takawomin abinci nace mata banajin yunwa ta ajjiye sai zuwa anjima zanci, bata ɗauke abincinba ta shuga ɗakinta, dai dai sannan Ameera da Abdallah suka dawo daga school, Abdul daman bayada juriyar yunwa yaro ɗan shekara goma jakarsa kawai ya ajje yacemin Uncle Abinci zanci nazuba masa abincin da Zainaba ta kawomin lomarsa uku yafara dafe ciki yana murkususu kafin wani lokaci kumfa tafara futa daga bakinsa ihun yaron yasa Zainaba futowa daga ɗaki ganin halinda Abdallah ke ciki yasa ta kwala ihu tana kallona Fahad abincin dana kawo maka kabasa banbi ta kanta ba na ɗauki Abdul da abincin zuwa Asibitinmu kafin najema rai yayi halinsa Abdul ya rasu😰na bincika abincin saina gano guba a ka saka, bayan ankai Abdul gidanmu na gaskiyya na tsare Zainaba da tambaya anan take gayamin Babanta be yakawo guba yace tazubamin a abinci naci na mutu dansu gaje duk dukiyar da Abbanmu yabar min ni kuma jin haka yasa na saketa saki uku kar naje wataran cikin dare da burma min wuka ta kasheni" Shuru nayi kawai ina bin Uncle da kallo tabbas nasan lokacin da Abdul ya rasu amma banzance ga dalilin rasuwarsa ba" jiki sanyaye na bar ɗakin nasa na koma nawa ɗakin na kwanta lamo ina tunanin lamarin duniyar nan HAJIYA JAMILA Harara tabi Fu'ad da ita sanda suka gama gaisawa ya haura sama inda Abbinsa yake mikewa tayi daga inda take zaune tabi bayansa cikin sanɗa ta tsaya a bakin kofa ta saka kunne tana so ta juyo maganar da zasuyi da safiyar nan....✍🏻 Idan har kin tabbatar kina son cigaban labarin nan kuma zakina yin comment to maza yimin magana ta wannan lambar nai adding ɗinki a group ɗin da nake posting:. 07039793439 [6/4, 7:46 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and weitting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 7&8 kunnanta ta saka a jikin kofar ta fara jiyo maganarsu "Abbi barka da safiya" Fu'ad ya faɗi haka yana tsugunne gaban mahaifin nasa "Barka dai Ameen jiya Mai martaba ke sanarmin za'a tura manya su shiga maganar auranka da Su'ad nayi farin ciki sosai My son na godewa Allah dayasa zanga wannan lokaci Allah yasa albarka" can kasan makoshi Fu'ad ya amsa da Ameen kafin ya jiyo Abie din dayaci gaba da magana "Takawa ya gayan yanason buɗe maka hospital akwai babban fili da Takawa ya baka kyauta za'a fara aikin gininsa kwanan nan" "Abie nidai bana ra'ayi buɗe hosoital ɗina ason raina a barni na koma canada naci gaba da aiki dasu ko kuma a barni a hospital ɗin gwammanati" "To bazan hanaka ba amma dai kayi magana da Takawa sannan gidana dake nan baya nake ga a gyara sa saika zauna anan ko?" "Abie nifa gaba ɗaya bana son zaman kasar nan dan Allah basai an gyara inda zan zauna ba kawai zan fara zama a part ɗina na masarauta kafin na gama shirye shiryan komawa canada" "To yanda kace" "Abie bari na koma sai munyi waya kenan?" "Haka ne jirgin yamma zanbi na koma" hannu Daddy ya mikawa Fu'ad sukai musabaha kafin daga bisani sukai sallama, da sauri Anty Jamila ta fara sakkowa daga step ɗin tana haɗawa bibbiyu ta sakko da sauri ta faɗa ɗakinta tana zagaye sa, da sauri ta ɗauki wayarta ta lalumo wata lamba bugun farko aka ɗaga batare data amsa sallamar da wacce aka kira tayi ba ta fara masifa tana magana cikin faɗa faɗa "Hajiya Nafisa anya bamu gama barci ba kuwa to yaron nan aure zai" da sauri wacce aka kira da hajiya Nafisa ta tashi zaune daga kwance da take tana zabga salati "Aure ai kuwa matukat ba ƴaƴanmu zai aura ba to kuwa tabbas Ameen zai tabbata ba aure wacce mai tsautsayince ta kinkimowa kanta wannan gingimeman aiki?" "Ban sani ba amma dai a kano take ya zama wajibi mu mike tsaye mu kara kaimi wajan ganin hakanmu ya cimma ruwa" "To yanzu Hajiya Jamila yaushe zaki shigo kizo mu leka wajan na gangare" "To kinsan Alhaji na gari ama dai inya tafi zan zo muje bamuga ta zama ba" sallama sukayi Hajiya Jamila ta ajje wayar har sannan tana jin zuciyarta ba daɗi SU'AD Na gyarawa kwanciyata saman gado ina kara manna wayata da jikin kunnena ina jin jerin kalaman soyayyar da Fu'ad ke faɗa min masu saka duk kan ilahirin jikina kara amsar soyayyarsa, kai hakika Fu'ad karshe ne yakai matuka a soyayya gaba ɗaya ya mamaye zuciyata bana iya kallon ko wanne namiji kallo na soyayya inba Fu'ad ba, "Kinyi shuru kin barni inata zuba ko, Su'ad lokaci yayi da zamu bayyana soyayyarmu kowa ya sani a gidanku, ni dama tuni kowa yasan da zamanki, ɗazu mai martaba yake cemin yanason shugowa kano tambayarmin auranki" zaro idanu nayi kamar yana kallona na ce "Uncle Fu'ad karatunafa gaskiyya banason barinsa kai kuma nasan ba zaman kano zakayi ba" "Mai zanyi a kano Canada nakeso mu wuce ana ɗaura auranmu kinga sai ki cigaba da karatunki acan" murmushi nayi tareda kallon kofa jin motsin shugowa da sauri na kalli kofar a tsorace danna zaci Uncle ne amma sainaga Mami ce bata tambayeni dawa nake waya ba dan tuni tasan da soyayyarmu da Fu'ad ce masa ne "Muyi waya anjima Mami ta shugo zamuyi magana" kallon da Mamina kemin yasa jikina yin sanyi domin kallone na tausayawa a sanyaye nace "Mami wai Fu'ad ke cewa zai turo mai zance masa" shuru tayi alamar akwai abinda ke cin ranta, nasan Mami farin sani kusan shakuwar da mukayi da ita koda Ummi data haifeni bamuyi ba, hakan yasa na ruko hannunta ina cewa "Mami akwai matsala ko naga kina cikin damuwa" kanta ta girgiza tana kakalo murmushin yake tace "Kigaya masa yazo gobe suje karaye shida Shareef saiya sanar da Baba sunusi" kai kurum na girgiza kana nayi masa text na faɗa masa abinda Mami tace. Washe gari kuwa karfe goma a kano tayiwa Fu'ad muna zaune nida Mami ya shugo da sallama daman yarigada yasaba kai tsaye yake shugowa gidanmu, gaisar da Mami yayi yana tambayar ina Ummi, Mami tabasa amsa da "Ummi tana asibiti jiya aikin kwana tayi kuma kaga har yanzu bata dawo ba" kafin Mami ta rufe baki Ummi ta shugo itada Jabir, zama tayi tana kallona "Ke ina kika saka wayanki anata kiranki baki ɗagaba, motana ta lalace a hanya inaso ki kaimin mota sai Jabir na kira nataso sa daga office" ni sai sannan ma na tuna da wayan tawa dana barota a ɗakina tun wajan tara rabona da'ita, Ummi da Mami suka wuce ciki kasancewar muna first falo ne, suna wucewa ciki Fu'ad matso kusa dani yana faɗin "Amarya ta" ni kunya ma yabani hakan yasa na rufe fuskata ina murmushi, zuwan Shareef yasa bamuyi wata doguwar hiraba suka wuce karaye Fu'ad yace yau zai koma saboda shirye shirye da suke jibi juma'a za'ayi sabbin naɗi a masarautar Ummi ta kalli Mami tana faɗin "Mami yakamata ki gayawa yarki gaskiyar wasiyar da Kanol yabari lokaci yayi dazatasan komai, naga wannan dogon mai tsayi kamar falwaya zuruftun dayake mana a gida kamar saboda yarki ne yake yawan zuwa kuma na fahimci akwai soyayya a tsakaninsu" Mami haɗa hannuwanta biyu tayi alamar roko🙏"dan Allah Dr na rokeki mubar maganar nan wallahi Su'ad batason Fahad, Fu'ad takeso abata abinda takeso" Ummi mikewa tayi daga inda suke zaune ta soma tafiya tana faɗin "Narantse da girman Allah babu abinda zai hanani aiwatar da wasiyar da Kanol yabari saidai in mutuwa nayi!" tana gama faɗar haka ta wuce ɗakinta, kwana biyu gaba ɗaya na fahimci Ummi da Mami sun sami saɓani saboda yanda naga basawa juna magana daga gaisuwa ba abinda yake sake shuga tsakaninsu, tunda aka haifeni na taso indai har Ummi suna kano to plat ɗin abinci ɗaya sukeci da Mami amma yanzu sai naga kowa ya zuba abincinsa yana ci, in Mami tana ɗaki to Ummi tana falo sam basa zaman hira kamar can baya, banyi masu magana ba ina jiran su Yaya Jabeer da Uncle su dawo daga garinsu Fu'ad inda sukaje wajan bikin naɗin sarauta Ranar juma'a bayan sallar la'asar ina zaune saman sallayata ina lazimi tun bayan mutuwar Daddy na ɗorawa kaina zama duk juma'a bayan sallar la'asar ina masa addu'a yaya Shareef ya shugo ɗakina jikinsa duk asanyaye yace "Su'ad kizo Baban karaye yazo" bayan sa nabi muka shuga tare, zama nayi kusada Mami ina gaida Baban Karaye kamar yanda muke faɗa masa, yan falon nabi da kallo Mamina ce sai Ummi da yaya fatima da bansan sanda tazo ba saiko yaya Sharif Uncle da Jabir daman basa nan suna garinsu Fu'ad. Baba Sunusi yayi gyaran murya yana faɗin "Alhamdulillah shekaran jiya wani yaro yaje wajena shida Shareef yagayamin yanason nai masa izini zai turo iyayansa su nema masa auran Aminatu Su'ad kamar yanda kuke faɗa,na tambayesa yataɓa sanar da Kanol kafin rasuwar shi yace min a'a nace masa yaje zan nemesa, abinda baku saniba shine adaran da Kanol zai rasu munyi waya yake gayamin yabawa Fahad auran Su'ad harma ya tsaida rana wata biyu! Allah baiyi zai gani ba, amma ni zan cika masa burinsa daya mutu yana fata, bazan taɓa canzawa ba!" yana gama faɗar haka yafuce daga falon murmushi Ummi tayi tana faɗin "Fenally", kwantar da kaina nayi saman kafaɗar Mami na fashe da kuka "Wayyo Allah na shuga uku wallahi bazan auri kanin babata ba bansonsa banason Fahad wallahi Fu'ad nakeso *wayyo zasu rabani da rayuwata farin cikina shine zaɓina hasken idaniyata hasken rayuwata* rasa Fu'ad daidai yake da katsewar numfashina wayyo na shuga uku ni su'ad nafaɗi haka ina ɗora hannuna aka🙆‍♀️ na fasa uban ihu tareda bajewa akasa ina kurma ihu kamar wata sabuwar yar bori, Yaya Fatima ta mike a fusace tayo kaina zata dakeni, da sauri na makalkale Mamina ina cigaba da ihun kukana waini ko zasuji tausayina su lallaɓa baban karaye ya janye, "Yaya daman nasan bazakiji tausayina ba saboda ke anbaki wanda kike so dan anga Daddy na baya raye shine za'ace yabawa Uncle ni, wallahi bana sonsa bakisan zafin rabuwa da masoyi ba shiyasa zaki dakeni maimakon ki tausaya min," Mami ta jani jikinta fuskarta fal damuwa tace "Yi shuru babyna daina kukan haka bawanda ya isa yai maki dole matukar ina numfashi Fahad ɗin zai dawo yasameni ne inbai janye batun auran nan ba bani ba shi!" sai sannan naji sanyi a raina na kwantar da kaina saman kafaɗarta ina sauke ajjiyar zuciya har barci yayi awon gaba dani. Jingine yake jikin bishiyar sab sab data kawata wajan iska na kaɗawa a hankali yajima a wajan ya kaɗaice kansa, gaba ɗaya bayason hayaniya ko kaɗan shiyasa yazame daga cikin sauran mutanan dasuka rage a gidan dan tuni wasu sun tafi tunda angama naɗin harma anyi walima, wayarta yaketa faman kira tana ring amma ba'a ɗagaba, tun daga nesa Juhaina take hango Fu'ad a nan rayuwarta ta duniya ba namijin datake so samada Yarima Fu'ad hankalinta duka yana kansa shiyasa ma takasa kula ko wanne saurayi amma shi ta lura sam hankalinsa baya kanta kwanakin nan takejin raɗe raɗin wai yana son wata yarinya a kano, ahankali ta karaso wajan tana murmushi bishiyar dake kallon wacce yake jiki taje ta tsaya tana faɗin "Yaya Turaki ashe kana nan anacan cikin gida ana nemanka, Umma tace nazo nan tasan bazaka wuce nan ɗin ba" batare daya daina danna wayar dayake dannawa ba yace "Kice gani nan zuwa" ɓata rai Juhaina tayi kana tace "tace kafata kafarka" fara tafiya yayi tabisa da sauri danya fita sauri kasancewarsa dogo shiyasa yakeda sauri, saida ko yarugata shuga sasin Umman, yasami Umma da Anty Jamila matar Abbi ɗinsu baiko kalli inda Antyn takeba ya zauna kusada Umma ya ɗora kansa saman kujera ya lumshe idanu ahankali yace "Umma duk bana cikin nutsuwata wani iri nake jina kamar wanda zan rasa wani abu arayuwata!" Umma ajjiyar zuciya tayi ahankali tana kallon Fu'ad tace "Al'ameen ba abinda zai sameka sai alheri wannan nauyin da'aka ɗaura maka ne yasa kakejin haka, kazama jarumi mana kaida ke shirin zama sabon sarki😹" murmushi yayi tareda mikewa ya wuce sashinsa dake cikeda abokansa ciki harda Fahad, Anty Jameela kwafa tayi tareda girgiza kai tana bin Fu'ad da kallo wanda yai burus kamar bai ganta ba, fuuu ta fuce daga falon ranta na suya da watsin da fu'ad yayi da ita, tabbas saita basa mamaki tayi alkawari saita lalata rayuwarsa saitayi silar da zai rasa duk wani farin cikinsa harma da sarautar da ake son naɗasa dan wannan turakin da aikai masa taga alamar sharar fage ne. Fu'ad can bedroom ɗinsa yashuge yana sake kiran layin Su'ad haka kurum yakejinsa wani iri muryarta yakeso yaji kozai sami nutsuwa, wannan karon bugun farko ta ɗaga muryarta a sanyaye ta masa Allah yasa alkhairi da addu'ar Allah yataya ruko "Princess naji muryarki ba dai dai ba" kamar zatayi kuka take faɗin "Barci nayi na gaji shiyasa kaji muryata haka" sake gyara kwanciya yayi yana faɗin "Ban yarda ba indai kina cikin damuwa kema kinsan ina ganewa faɗamin kawai maike faruwa" fashewa tayi da kuka, gaba ɗaya ya ruɗe harda tashi zaune yadafe kai🤦‍♂️ "Oh Baby gayamin maike damunki inbaki gayamin ba billah yanzu zan kamo hanyar kano batare da kowa yasani ba" shagwaɓe murya tayi "Banida lafiya zazzaɓi nake tun safe Ummi taki kulani Mami kuma bata nan bare ta kaini hospital" komawa yayi ya sake kwanciya "Raguwa zazzaɓin kikewa kuka tonan da watannima haihuwa zaki, wacce tafi zazzaɓi wahala, kisha ko paracetamol ne anjima zan kiraki naji yaya kikeji" kai kurum ta girgiza masa saboda wani tausayinsa daya mamaye zuciyarta tayaya zata bari a rabatada Fu'ad wanda yai soyayya akaro na farko baiji daɗiba yanzuma ace bazai sameta ba, ai wallahi ko sama da kasa zata haɗe koda tsiya koda tsiya tsiya sai an aura mata Fu'ad idan suka ki kuwa wallahi guduwa zatayi tashuga duniya dadai ta auri Uncle wanda takewa kallon kanin uwa. Fu'ad da Fahad da dare suka shirya cikin koriyar shadda wacce Fu'ad ya ɗinka masu, sosai sukai kyau komai nasu iri ɗaya suka saka sai suka futo kamar wasu twince inka gansu inba saninsu kayiba zakace uwa ɗayace ta haifesu saboda kamanni dasuke ɗanyi kaɗan saidai Fu'ad dayafi Fahad fari da tsayi, Fahad ba fari bane can shidai baza'akirasa da baki ba hakaza baza'ace masa fariba yanada tsayi kaɗan amma saboda yanada kiba saita shanye tsayin nasa, Suna hakimce a bayan mota yayinda Sarkin mota kejansu, har zuwa G R A gidansu Fu'ad yazo gaida mahaifinsa dayazo garin jiya da dare basu sami haɗuwa ba saboda hidama dasuke da mutane, Anty Jameela suka samu a falo taci uban kwalliya tana hakimce tanacin Apple, Fu'ad ko kallon inda take baiyi ba kai tsaye ya wuce sashin Abbi ɗinsa, ya mugun tsanar matar nan tunda take ƙazabtar masa da kanwarsa guda ɗaya tilo dayakejin duk duniya bayada sama da'ita yana matukar ji da Deejah akanta zai iya rabuwa da komai indai zatayi farin ciki, Fahad dakebin Fu'ad da kallon mamaki yace "Amma naga kamar Anty Jamila muka wuce a Falo ko bamu gaidata ba" taɓe baki Fu'ad yace "Saime to dan bamu gaidata ba haifarmu tayi!" karaf maganar a kunnan Antyn dake shirin shugowa sashin murmushi tayi tareda laɓewa har suka gama gaisawa da Abbi saida taji suna sallama kana tai saurin ɓuya a bayan labule saida suka futa ita kuma ta shuga, Washe gari sassafe Anty Jamila taiwa Abbi karyar zataje gidansu yajirata ta dawo bazata jimaba zata dawo saisu wuce Kaduna inda can Abbi ke aiki, bata doshi gidan nasu ba kai tsaye hanyar wani daji ta yanka a motarta tajima tana gudu a motar nan cikin jejin kana ta sauka a motar da jingina tareda rufe idanunta tasoma karanto wasu ɗalasimai kafin tarufe bakinta wata iriyar guguwa mai karfi tayi sama da ita🙆‍♀️🏃‍♀️🤭 Zainaba zaune gaban mahaifinta dake cin tuwo, saida tajira ya gama ci sannan tace "Baba waiya maganarmu ne ta Fahad wai haka zanyita zama nifa indai ba gidansa ba wallahi bazan sake aure ba, kuma zuwan danaima rannan na gano wata babbar masifa dake shirin faruwa damu domin na gano son Su'ad a cikin idanun Fahad" Baba ya bushe da dariya yana faɗin "Wannan shine kuskure na karshe da Fahad zaiyi idan har yasake ya sake aure Allah ne kaɗai zai fuddashi daga tarkona amma badai mutumba"😂dariya Zainaba tayi tana jinjinawa Baban nata ganin ashe shima har yanzu hankalinsa nakan Fahad ɗin "Ai baba basai kayi komaiba ni kaɗaima na ishi Fahad inada tarin abubuwan dana tanadar masa matukar yai kuskuran auran wata batare daya maidani ɗakina ba...✍️ Inkinsan kinason karantawa kuma zakina yin commeny to maza yi save ɗin wannan lambar 07039793439 da Mami Yusuf Daboo kimin magana zanyi adding naki a group ɗina🙏 [6/4, 7:46 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and weitting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 9&10 Fahad cikeda kewar Su'ad yashugo gida kwana biyun nan dayayi babu ita ba karamin ɗaga masa hankali yayi ba musamman jiya zuwa yau gaba ɗaya taki ɗaga kiransa a waya, kai tsaye ɗakin Mami ya shuga ganin ba kowa a falon sai hanne mai aiki, Su'ad na kwance kan gado ta lulluɓa da katon bargo jiya zuwa yau ita kaɗai tasan mai takeji a zuciyarta batajin zata iya hakura da soyayyar Fu'ad data gama mamaye mata dukkan zuciyarta, ɗakin shuru ba motsin komai saina zubar ruwa dayake jiyowa daga bathroom, harya juya zai futo azatonsa Su'ad ɗince ke wanka, jiyowa yayi jin saukar numfashin mutum a bargo janyo bargon yayi tareda saurin zama gefan gadon a ruɗe yake faɗin "Besty bakida lafiya ne" taɓa jikinta yayi yaji zafi sosai dafe kansa yayi yace "Kinsan kina zazzaɓi kikazo kika lulluɓa da bargon nan kinaso kimin asara ko" kallon inda yake banba saima tsaki da naja tareda juya fuskarta na daina ganinsa, hawa yayi saman gadon sosai yana matsawa kusada niba hasale nace "Ka futar mana daga ɗaki Fahad banason ganinka banason sake ganin fuskarka" dafe kai yayi🤦‍♂️cikada damuwa ya sauka daga gadon yana kallon Su'ad da mamakin maganarta, futowar da Mami tayi daga bathroom yasa ya kalli Mamin yace "Mami maiya sami Besty naji tana magana kamar wacce aljanu suka taɓa" Mami jingina tayi da kofar bathroom tana kallon Fahad da duk damuwa ta bayyana karara a fuskarsa tausayin ɗan uwanta yakamata tasani ba karamin so Fahad yakewa Su'ad ba saidai yayi sake yayi wasa da damarsa tuni wani yariga sa shuga zuciyar Su'ad "Fahad maiyasa zakamin haka? taya zaka sami Kanol ka gaya masa kanason Su'ad waya gaya maka haka ake soyayya ina mai umartar da lalle ka janye batun auran nan domin yata tanada wanda takeso har sunyi alkawarin aure" da sauri ya zauna gefan gado saboda jirin dayaji yana kokarin kayar dashi, "Mami tayaya zan hakura da soyayyar da zuciyata ta rayu da'ita samada shekara ashirin! inason Su'ad banajin akwai wani namiji a duniyar nan daya fini kaunarta, itace rayuwata zuciyata gaba ɗaya itace ni" yakarasa faɗa hawaye suna biyo kuncinsa "Fahada na rantse da Allah koda son Su'ad zaiyi ajalinka saika barta, inba haka ba babuni babu kai kaje kanemi wata yar uwar bani ba!" tana gama faɗar haka ta koma bathroom saboda wani kuka dake kokarin taso mata na tausayin ɗan uwan nata guda ɗaya jal daya ragemata anan duniya, Fahad kallon Su'ad yayi wacce ke kuka kamar ranta zai futa jin maganganun su Mami wai ita yaya zatayi da ranta shin Aminci zata zaɓa ko kauna, sosai kukanta ke taɓa zuciyar Fahad jiri na ɗibansa haka ya fuce daga ɗakin zuwa nasa ɗakin ko takalminsa bai cire ba ya kwanta saman gado tareda fashewa da kuka. Yaya Jabeer wanda yafuto daga ɗakin Ummi kasancewar tare suke da Fahad basusan da zuwan baban karaye ba sai yanzu daya dawo Ummi ta faɗa masa komai, turus yaja yatsaya sanda ya shuga ɗakin Fahad ya gansa kwance yana rizgar kuka kanar wanda akace masa Mami ta rasu, gaba ɗaya Jabeer ya kiɗime ɗago Fahad ɗin yayi yana faɗin "Uncle lafiya kake kuka haka?" ruke Jabeer yayi "Jabeer kataimakeni yaya zanyi da zuciyata Su'ad bata sona tace bazata aureni ba!" Jabir dafe kansa yayi shi dariyama Fahad ɗin yaso basa hakan yasa yace "Shine zaka tsaya kana wannan kukan sai kace wanda akaiwa mutuwa wallahi kaji na rantse matukar ina raye Su'ad batada wani miji inba kai ba barima kagani" Mikewa yayi ya fuce daga ɗakin zuwa na Mami baiko kula da Mami dake zaune gaban madubi ba ya janyo Su'ad daga saman gado wacce ke faman kuka har lokacin, fuskarta ya ɗauke da mari "Ashe bakida hankali bansani ba! ke harkin isa kifaɗawa Uncle magana toki sani auranki da Uncle ba fashi saidai in an kaiki ki mutu!" "Jabeer agabana kake dukan yata ko mutuwa tana kunyar idon mahaifi fa" ta tashi ta rungume Su'ad tana lallashinta. Fu'ad yafuto daga fada kenan yau tun safe suna tareda mai martaba yana futowa Fahad yafara kira yaji yaya sukaje gida amma har wayan tagama ring bai ɗagaba hakan yasa ya kira lambar Su'ad wacce rabon dasuyi waya tun jiya da dare gashi yanzu har karfe uku na rana yasan yayi laifi yana zaton hakan yasa bata ɗagaba har kiran ya katse saida ya shuga sashinsa ya cire rawanin kansa ya ajje saman kujera ya zauna kana ya sake kira, Su'ad tana gani kiran harya katse bata ɗagaba saboda batasan yaji muryarta yanaji zai san kuka take hankalinsa zai tashi ita kuma batason damuwar sa, ganin kira yanata shugowa yasa ta ɗaga tana kokarin saita kukan dake shirin kwace mata amma ina ta kasa musamman dataji yace "Hubbina inata kira kinki ɗagamin waya ko" kukane mai sauti ya kwace mata shuru yayi yana sauraron kukan nata dayakejinsa har tsakiyar kansa "Princess kinada damuwa amma kinki gayamin haka mukayi dake! damuwarki damuwata ce dan Allah gayamin maike damunki tun jiya kike kukan nan Mamin bata dawo ba?" kai ta gyaɗa masa kana tace "Fu'ad muna cikin matsala kayi mana addu'a Allah yasa mu kasance da juna" mikewa tsaye yayi tareda ɗaukar rawanin sa a hannu yafuta bayan ya kashe wayan yana kwaɗawa Sarkin mota kira, ko rawanin nasa bai mayar ba ya shuge mota yana bawa sarkin mota umarnin yai gudu sosai soyake suje kano nan da awa awanni gudu sosai Sarkin mota keyi amma Fahad gani yake kamar ba gudun yake ba ji yake kamar ya karɓi tukin gaba ɗaya ya lulluɓe sarkin mota da masifa faɗa yake masa kamar zai ari baki baiyi aune ba ji kake kiiiiii sitiyarin motar ya kwace motar ta daki wani gini dake gefan titi tafara hayaki Fu'ad ya runtse idanunsa saboda azabar dayaji na glass daya shuga hannunsa, ɗayan hannunsa yasa yazare glass ɗin yana lumshe idanu saboda azabar daya sha, ganin motar na kokarin kamawa da wuta yasa ya tattara duk kanin karfinsa ya daki murfin motar yabuɗe yafuta da sauri tareda jawo sarkin mota daya soma futa a hayyacinsa saboda buguwar dayayi a kansa, Fu'ad ya raba rawaninsa biyu ya ɗaurewa Sarkin mota kansa daya soma zubar da jini shima ya ɗaure hannunsa dake masa wani azababban zugi, dai dai sannan motar yan sanda tazo wajan domin kiransu da wasu jama'ar dake gefan wajan sukayi tun sanda sukaga motar ta gangara gefan titi, Asibiti aka wuce dasu fu'ad da gaggawa ganin yanda jini ke zuba daga kan sarkin mota, Fu'ad ciwon hannunsa kawai aka wanke masa tareda saka masa bandeji, duk wannan abun gaba ɗaya zuciyarsa tana wajan Su'ad da har sannan yakejin sautin kukanta acikin kunnuwansa, kai tsaye gidan yayarsa Hadiyya yanufa acan yai wanka ya canza kaya ko abincin data ajje masa baici ba yafuce zuwa gidansu Su'ad baiko tsaya neman motaba, yahau adaidaita shidai kawai burinsa yaje ga Su'ad yaji damuwarta, baisha wahalar shuga gidanba kasancewar masu tsaron gidan sun ruga sun san sa. kai tsaye garden yanufa inda suka saba zama da Su'ad ɗin saida yazauna saman kujera kana yakira lambarta ya shaida mata gashi nan cikin gidansu inda suka saba zama, da sauri takatse kiran ta futa da gudo ko mayafi bata saka ba, baisan da shugowarta garden ɗinba sabida idanunsa dasuke rufe haka kawai yakejin wata irin faɗuwar gaba wacce bai taɓajin irinta ba a rayuwarsa, kanta ta kifa saman cinyarsa tareda fashewa da kuka "Su'ad na gamaki da girman Allah ki gayamin abinda ke sakaki kukan nan dukkin ruɗani da kukan nan banda Allah yakiyaye mu ma da tuni ina lahira! Princess idan mutum yana cikin damuwa kuka bashine magani ba addu'a itake maganin komai" "Nashuga uku Fu'ad kowa ya tsaneni a gidan nan gaba ɗaya sun juyamin baya Ankul sukeso baniba ashe haka rashin mahaifi yake na tabbata da Daddyna yana raye zai tausayamin yabani abinda zuciyata ke so, wai Ankul Fahad ne yake sona har'an tsaida ranar bikinmu maiyasa maiyasa ankul zaimin haka!" da sauri Fu'ad yasa hannu yadafe saitin zuciyarsa dayaji tai masa wani irin bugawa saboda yanda zancan yadaki zuciyar tasa, wani duhu yagani a idanunsa ganinsa yaɗauke na wucin gadi😥hakan yasa ya lumshe idanunsa yana karanto addu'a _Allahumma ajirni fi musibati wakalifni khairan minha, la'ilaha illah anta subahanaka inni kuntu minal zalimin_ ```Allahumma la sahala inlla....Su'ad ta amshe suka karasa tare, yai shuru kawai sabida yanda yakejin zuciyarsa ya tabbata inya buɗi baki kuka zaiyi shi kuma baison yayi kuka gaban Su'ad, jin shurun Fu'ad yasa taci gaba da basa labarin yanda sukai da baban karaye, gaba ɗaya ya shuga damuwa kansa ya kulle yama kasa cewa komai abu ɗaya daya sani shine ko sama da kasa zata haɗe bayajin zai iya hakura da Su'ad, "Fu'ad kayi shuru bakace komaiba dan Allah kanema mana mafuta ko kuma mu gudu mubar garin nan mutafi wata kasar musamu a ɗaura mana aure inyaso saimu dawo daga baya" buɗe idanunsa yayi akan fuskar Su'ad data gama ɓaci da hawaye shima idanunsa yayi jajir yace "Zaki bini da gaske zaki bini mu gudu sudan a ɗaura mana aure acan dangin babata inyaso saimu dawo" kanta tashuga gyaɗa masa mikewa yayi yana kallon agogo yace "kije kiyi sallar mangariba lokacin sallah yayi ki mana addu'a Allah yabamu nasara awannan yakin dake tunkaromu amma kisani tabbas ni nakine kema tawace ruwa da iska babu abinda zai rabamu nidake kamar hanta da jini ne rabamu zaiyi wuya, ki tattara komai naki da kikasan yanada mihimmanci inayin sallah zamubar gidan nan.....🙆‍♀️ Saura kiris a daina turasa ko ina zai ci gaba da zuwar maku ne a group ɗina na Kukan Zuciya real fans idan har kinsan da gaske kinason cigaba da bin book ɗin nan to maza yimin magana ta wannan lambar 07039793439 zanyi adding naki a group ɗin batare da kin biya ko sisinki ba🥰 [6/4, 7:48 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and weitting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 11&12 Su'ad ta ruko hannun Fu'ad daya juya zai tafi masallaci ya juyo yana mata murmushi kallon hannun nasa tayi tareda kafawa zoban hannunsa idanu, ahankali ta ciro zoban azurfar dake hannunta tasaka masa a hannunsa tana matukarji da zoban Ankul Fahad ya siyo mata shi awani zuwa saudiya dayayi, ta ciro na hannunsa tasaka a babban ɗan yatsanta tayi ko sa'a ya zauna ta kwantar da kanta saman kirjinsa "Wannan zoban yazama zoban alkawari a tsakaninmu, alkawari mukayi da zuciyoyinmu matukar muna numfashi babu rabuwa a tsakaninmu duk rintsin da zamu shuga mu tabbata a kaunar junanmu, musa aranmu babu mai rabamu inba mutuwa ba!" Rukota yayi sosai ajikinsa ahankali Yace "Na amince da duk abinda kikace insha Allah ni nakine ke tawace Ruwa da iska babu abinda zai rabamu ba rabuwa nidake" Ankul Fahad da tun futowar Su'ad yabiyo bayanta a ɓoye yanason yaga inda zata take wannan gudun kamar bata hayyacinta, ganin inda ta shuga yasa ya ɓuya jikin bishiya kasancewar garin yafara duhu yasa basu gansa ba amma shi yana ganinsu daga inda yake yanama jiyo duk maganganunsu, hawaye yake sosai dan bai taɓa zaton akwai soyayya tsakanin Su'ad da Fu'ad ba, a iya zaman fu'ad a gidan zai iya cewa bai taɓa ganin sunyi magana da ita ba saima harare harare, ashe soyayya suke suka mayar dashi wawa, ashe harare hararan dasukewa juna na soyayya ne yakasa ganewa, ahankali yafuto daga wajan ɓuyansa Yace "Baku kyautamin ba tayaya kuka ɓoyemin wannan babban abin farin cikin, Su'ad azatona nine mutum na farko dazaki fara faɗamin abokina yana sonki, kaima Aboki duk laifinka ne daka gayamin kanason Besty wallahi da bazan taɓa fallasa sirrin zuciyata ba, ashe daman Su'ad ce budurwar da kullum kake gayamin kanasonta kake cewa kayi budurwa yar garinmu, ina mai tabbatar maku da na janye batun aurena da Su'ad na bar maka danna gano itace farin cikinka ni kuma fatana ako da yaushe inganku cikin farin ciki ina maku fatan alheri a rayuwar auranku!" yana gama faɗar haka yai gaba Fu'ad yabisa yana kiransa amma baiko waiwayo ya kallesa ba ya wuce cikin gida abinsa, kai tsaye ɗakin Mami ya wuce yasameta zaune saman gado tana lissafin kuɗi, zaman da yayi yasa ta kallesa tareda ajje abinda take Tace "Fahad lafiya maiya sameka?" hawayan idanunsa suka zubo kan kyakkyawar fuskarsa "Mami ashe daman Su'ad da Fu'ad soyayya suke ban sani ba! Mami yaya zanyi da tarin soyayyar danakewa Aminatu yanzu haka zan hakura inaji ina gani in rasa farin cikina, mami bakiji yanda zuciyata take harbawa jinake kamar zan mutu" tausayin kaninta yakama ta ta sakko daga saman gadon ta zauna kusa dashi tareda dafa kafaɗarsa tana bugawa ahankali alamar rarrashi tama kasa cewa komai jitake kamar ta tayasa kukan amma ina bazatayi ba ta karyar masa da gwiwa matsayinta na babba ita zata karfaffa masa gwiwa wajan ganin ya jajirce yasawa zuciyarsa salama "Kayi hakuri sau tari abinda kakeso bashi ke zama alkhairi ba a rayuwarka kasawa ranka dama can Su'ad ba rabonka bace ka sadaukar da soyayyarka ga masoyanka guda biyu da kariga kasani farin cikinkinsu shine naka, inaso gobe kaje karaye ka gayawa baba sunusi ka janye batun auranka da Su'ad kafasa" haka tayita lallashinsa har zuciyarsa tayi sanyi yaji aransa yama hakura da auran ma gaba ɗaya zai zauna a haka ya karashe sauran rayuwar data rage masa. Su'ad idar da sallarta kenan tana zaune saman dadduma tana azkhar Ummi tashugo ɗakin ta zauna gefan gadon su'ad ɗin ahankali tafara magana da sigar lallashi "Su'ad kiyi hakuri ki ɗauki kaddara kisa aranki auranki da Fahad babu fashi naga wannan dogon yazo mana gida, bansan dame yazo ba amma inaji ajikina kamar da abinda kuke kullawa, yanzu dan Allah bakiji kunyar Mami ba agabanta kike nunawa ɗan uwanta baki sonsa ke bakisan kara ba, tunda aka haifeki take ɗawainiya dake koni dana haifeki bansan wahalarki ba, ita komai tasamu ke dukkan takardun kadarorinta sunanki ne komai ta samu Su'ad burinta akoda yaushe tasaki farinciki ashe kodan wannan bazaki so ɗan uwanta ba, inda watace bazata taɓa goya maki bayaba amma dayake kaunar datake maki daga zuciyarta ne haka ta zaɓi farin cikinki akan na ɗan uwanta, koma ba wannan ba ashe bazaki iya cikawa Daddynki wasiyarsa ba daya bari, dan Allah amatsayina na wacce na haifeki na rokeki daki hakura da Fu'ad ki rungumi kaddararki Fahad insha Allah bazakiyi nadamar auransa ba zakiyi farin ciki" tunda Ummi tafara magana Su'ad ke kuka gaba ɗaya Ummi tagama kashe mata jiki amma yaya zatayi da zuciyarta kan abinda takeso, ita bata taɓa son Ankul ba batajin kuma zata so shi, bare takaisu ga aure, to inta auri Fahad maita aura, kanin Mami zuciyarta tabata amsa tayaya zata iya zaman aure da wanda takewa kallon kanin mahaifiyarta, koda ta auri Fahad batajin zata iya basa kulawar da mace take bawa namiji ina zatakai kunyarsa, batasanma Ummi ta futa a ɗakinba sai data ɗago kanta da niyyar tayi magana kana taga ɗakin ba kowa sai ita, Fu'ad massages yayi mata ya koma asibiti wajan sarkin mota za'ayi masa karin jini. Washe gari Ankul sassafe yaɗauki hanyar karaye karfe goma acan tayi masa bai wani jima ba ya juyo kai tsaye asibitinsu ya wuce bai biyo gida ba, tinda yazauna a office ɗinsa yakasa aikata komai ko feshan ɗinsa Dr hafis yaturawa su, Dr hafis daya tashi ya shuga office ɗin Fahad harya zauna fahad baisan yashugo ba saida yasa hannu yataɓa sa kana ya kallesa da sauri yana ajjiyar zuciya kamar wanda yai kuka. "Amma bakada lafiya kwana biyun nan naganka sai'a slow" Fahad ya ɗora kansa jikin kujera ahankili kujeran ke juyawa dashi yace "Lafiya kalau nake kawai inada damuwa ne akan Su'ad" Dr Hafis dariya yayi "Su'ad Su'ad ko yaushe dai maganarka akanta nagaya maka kafaɗa mata awuce wajan katsaya kana kallon ruwa sai kwaɗo yayi maka kafa tukunna" sauke numfashi Fahad yayi tareda futar da iska mai zafi daga bakinsa Yace "Na nawa kuma asheni ina zaune yaron nan Fu'ad yagama siye zuciyarta" nan dai Fahad yasanarwa da Dr Hafis komai "Kabar damuwa kayi addu'ar neman zaɓin Allah hakan zaifi wannan damuwar da kake ciki wacce zata iya haifar maka da ciwo" godiya yayiwa Dr sannan suka mike suka futa tare dan tuni lokacin tashinsu yayi. Fahad koda ya koma gida wayar Fu'ad yakira yajima bai ɗaga kiranba sannan ya ɗaga. "Aboki kana inane ko ka koma" "A'a ina kano asibiti jiya wajan tahowarmu motarmu ta faɗi sarkin mota yabugu aka kaganshi a kwance tun jiya ba cigaba ɗazu naiwa mai martaba magana yasoma shirya masa tafiya cairo anjima jirginsu zai tashi" Fahad wanka kawai yayi ko abinci bai ciba ya wuce wajan Fu'ad wanda tun a wayar dayaji muryarsa yasan yana tare da damuwa, sanda yaje kallo ɗaya yamasa yaga yayi wani zuru zuru shidaman haka yake yanzu ne damuwa zata saka sa rama kilama nan gaba kaɗan saiya kwanta zazzaɓi bayan sun kai sarkin mota airport suka juyo Fahad dake tuki ya kalli Fu'ad daya ja uban tagumi kansa kurum ya girgiza yana faɗin "Duk kabi kasa damuwa aranka kalli yanda kayi wani ziru zuru kamar wanda yatashi daga jinya" murmishi Fu'ad yayi yana kallon Fahad dayaci gaba da faɗin "Ni naruga nabar maka Su'ad harma naje karaye munyi magana da Baban karaye kasan girman ka awajena ya wuce na auri abinda kake so tabbas dan son Su'ad ina sonta tun randa tazo duniya naji banida wata mata inba itaba!" Fu'ad yaɗago kansa yana kallon Fahad kana yace "Bazan iya auran abinda kakeso ba aboki kai kafi cancanta daka aureta saboda kafini sonta, kai karayu da kaunarta ni kuma yan watanni nayi a soyayyarta dan haka bazan iya auranta ba ni na bar maka bazan aureta! ajje ni gidan Anty Hadiyya" mirmushi Fahad yayi yanabin Fu'ad da kallon tausayi Yace "Bazan ajjeka ba da gidanta kake sauka naga inkazo kano ko kwana nawa zakai muna tare sai wannan karon ashe daman har mace takai girman da zata raba amintarmu" lumshe ido Fu'ad yayi yana murmushi Yace "Su'ad tayi kaɗan ta rabamu muje ni daman banson naje gidanne ta ganni ta shuga damuwa banson damuwarta ko kaɗan" Fahad baice komaiba yaci gaba da tukinsa "Inason nasai kayan sawa banzo da shirin kwanan garin nan ba sai gashi ina shirin yin na biyu" "Wanne kaya kuma zaka siya, ga nawa nan nasan zasuyi maka saidai tsayinko" kallon juna sukai sai kuma suka fashe da dariya atare suka furta "Maika tuna" nan ma dariyar sukayi kamar basune a damuwa ba Fahad yace "Natuna rayuwarmu ta scaundry inban wanke Uniform ɗina ba na saka naka su Moha suyita tsokanata saboda yanda rigan ke sakkomin har kusan kasa oh rayuwa kaga yanda muke da Moha kamar baza'a rabuba amma tunda muka kammala school bamu kara ganin juna ba ko yana raye" har sannan murmushi bayyane kan fuskar Fu'ad yace "Allah nima nakasa mantawa da Moha koya zama sojan ko yaya oho Allah dai yasake haɗamu wata rana" har suka karasa cikin gida suna hira, gidan shuru kamar babu kowa da'ace da ne da tuni koba yaran gidan zaka samu Mami da Ummi a falo suna hira amma damuwa yanzu tasa kowa zaman tunani a ɗaki shiyasa ba wanda yasan da zuwan Fu'ad gidan. Karfe huɗu baban karaye yaiwa gidan tsinke tunda ya zauna yakewa Mami faɗa wai ta zuga ɗan uwanta yaje ya gaya masa ya fasa auran Aminatu "To kisani wallahi koda zan ɗaura aure gobe da safe Fahad yasakomin ita da dare to saina ɗaura aidai na cika wasiyyar ɗan uwana kuma ku sani na maida ɗaurin auran nan da kwana shida ranar asabar mai zuwa aure babu fashi!" yagama faɗansa ya tafi ko gaisawa basuyi ba, Ummi daɗi taji sosai nan take tasoma kiran waya tana sanar da bikin Su'ad asabar, Fahad jiki a sanyaye yamike daga wajan yakoma ɗakinsa anan yasami Fu'ad kwance kan gado yana kuka kamar wani mace dan gaba ɗaya yana jiyo faɗan baban karaye daga inda yake saboda yanda yake maganar cikin faɗa da fusata "Fahad maiyasa banda sa'a a soyayya kowacce mace naso bana samu abaya naso Suwaiba kamar hauka amma ta yaudareni yanzu naso Su'ad wacce itama ke sona kamar ranta amma kaddara ta rabamu Fahad mai nayiwa soyayya take azabtar dani haka nagama soyayya bazan karaba!" mikewa yayi yana yiwa Fahad sallama ba yanda Fahad bai lallashi Fu'ad ba kan yazauna zuwa safiya sai yabi jirgi ya koma amma yakafe har yakai kofar futa daga falon farko na gidan yaja ya tsaya jin Su'ad na kiran sunansa kallo ɗaya yayiwa fuskarta bai sake kallonta ba saboda yanda zuciyarsa ta tsinke "Daman kana gidan nan ban sani ba yaushe kazo" "Ɗazu muka shugo da Fahad yanzunma tafiya zanyi" yafaɗi haka yana cigaba da tafiya da ɗan gudu take binsa saida yafuta compound sannan ya tsaya "Zantafi Su'ad kiyi biyayya ga iyayanki duk ɗa nagari yana son ganin farin cikin iyayansa kisa aranki daman can Allah bai kaddara zamuyi aure ba! iyakarmu soyayya kimanta dani ki rungumi mijinki Fahad zakiji daɗin zama dashi fiye dani insha Allah zan dawo ran asabar wajan ɗaurin auranku" kam ta kame waje ɗaya jin maganganun Fu'ad bata ankare ba taga Fu'ad yana shirin fita daga gidan wani ihu ta saki tareda faɗin Fu'ad Come back please!!! ta zabura zatabi bayansa taji an riketa duk da idanunta a rufe suke da ɓacin rai tasan wane saboda jin kamshin sa datayi "Kasakeni Ankul kasakeni nabisa kana kallo farin cikina zai tafi" gaba ɗaya Fahad jiyake kamar yayi kuka ganin yanda jikin Su'ad ke ɓari kamar mai shirin tada aljanu🤭"Saketa Fahad" Ummi dake kallonsu tun ɗazu ta faɗi shiko sake kankameta yayi danshi yafara tunanin ba lafiyarta kalau ba "Kasake ta nace! tabisa suje can ta nemi wasu iyayen su ɗaura mata aure da shi saboda ke bakisan tawalkali ba, shi yana namiji ya iya tafiya yabarki ya gaya maki gaskiyya amma kin kasa ɗauka saboda idaninki sun rufe da makauniyar soyayyarsa" Fahad baiyi aune ba sai kawai gani yayi Su'ad ta sulale ta faɗi kasa tana wani irin numfashi daba shi ba hatta Ummi dake faɗa saida hankalinta yatashi, Mami da sauri tayi kan Su'ad tana faɗin "Shikenan kun kashe min ita ku bakuda asara ni kuka cuta Su'ad dan Allah kitashi ke kaɗai nakeda ita ke nake kalla ako da yaushe naji sanyi a raina ke kika maye min gurbin da a kullum ke damuna a zuci Aminah...😥 [6/4, 7:48 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and weitting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA S ANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 12&14 Fahad ya kinkimi Su'ad yasata a mota gaba ɗaya hankalinsa yatashi asibitinsu ya wuce da'ita Dr Hafis ya karɓeta ruwa ya jona mata tareda mata alkurai harya samu tadawo normal tai barci, Hafis yadafa kafaɗar Fahad yace "Agaskiyya kubi yarinyar nan a yanda takeso abokina nasan duk akan maganan nan ce dan Allah abarta kasan yanda jininta yai mugun hawa kuwa, wallahi kuka cigaba da kuntata mata zaku iya rasata gaba ɗaya" Fahad yadafe kansa cikeda damuwa ya ce "Dr narasa yanda zanyi Baban karaye yadage kan maganar nan halin yanzuma fa harya tsayar da rana gaskiyya inaga barin garin nan zanyi inkomai ya dai daita na dawo" "Kaje ina?" yaji muryar Ummi tana faɗa tareda shugowa ɗakin "Wallahi kasani ko mutuwa Su'ad tayi sai an ɗaura auran nan an kaita gidanka inyaso daga gidanka a wuce da'ita kabari, Mami ko kallon inda Ummi da Fahad da suke magana batai ba gaba ɗaya hankalinta naga Su'ad ganin yanda take sauke nunfashi a hankali yasa hankalinta kwanciya. Da kuka sosai Nafarka lokacin ɗakin ba kowa sai Yaya Fatima Ummi da Mami sun futa, Yaya Fatima ta hararw ni kamar zata kaimin duka cikin masifa ta ke faɗin "Su'ad yanzu abinda kika zaɓarwa kanki kenan mai Fu'ad yakeda shi wanda Fahad bashi da? dan Allah ki kwantar da hankalinki ki rungumi kaddararki, a rayuwar nan fa kowa kika gani da kalar kaddarar sa" Kuka nake sosai nace "Na hakura da Fu'ad tunda harya iya karya alkawarinmu yatafi yabarni bayan munyi alkawarin duk runtsi duk wuya muna tare amma ya iya tsallake ni yatafi ya barni na hakura Yaya na karɓi zaɓin Daddy na zan cika masa burinsa bayan ransa zan tabbatar da wasiyyar sa daya barmin koda kuwa hakan na nufin tarwatsewar zuciyata da tabbatuwar kunci a rayuwata," "Insha Allah ma bazakiyi kunciba a gidan Fahad zaki samu farin ciki da walwala fiyeda kowacce mace dake gidan mijinta nasan irin son da Fahad yake maki kema kuma kinsan hakan kawai soyayya da kauna ce suka rufe maki idanu kika kasa tantance Aminci zaki zaɓa ko kauna" "Na zaɓi Aminci nabar Kauna da Soyayya bari nahar abada bazan sake soyayya ba nayi banji da daɗi ba nabarta har karshen numfashi na, ki gayawa Fahad a maidani gida ni naji sauki" *Ina bawan Allah Fu'ad* Yana futa a gidan yatare nape ko gaya masa inda zai kaisa baiyi ba ya kifa kansa saman kafafunsa shi kaɗai yasan maiyake ji a zuciyarsa, saida suka hau babban titi kana mai nape ɗin Yace "Ranka yadaɗe ina muka dosa" batareda Fu'ad yaɗago ba yabasa amsa da "Fara kaini Atm dake kusa na ciri kuɗi sannan ka karasa dani airport" basu jima suna tafiya ba mai nape ya faɗa masa gasu a Atm Fu'ad yafuta yacuro kuɗi sannan suka cigaba da tafiya, suna isa airport ya saka hannu a aljihu ya ciro dubu huɗu yabawa mai nape ɗin "Yallaɓai ɗari biyar ne kuɗinka" hannu kawai yaɗaga masa batareda yace komaiba yasoma tafiya har ya shuge cikin airport ɗin mai nape ɗin na kallonsa, haka kawai yaji tausayin bawan Allah daga gani yana cikin damuwa "Allah ya magance maka damuwarka yahaɗaka da farin cikin duniya dana lahira yabaka duk abinda kake nema" mai nape yafaɗi haka yana share hawayan fuskarsa rabonsa dan gidansa tun bayan sallar azahar ya futo nema ko abinda iyalansa zasuci da rana bai basu ba mashin ɗinma ba nasa bane na haya ne, gida ya koma yabawa matarsa dubu biyu yace suyi cefane sannan ya cigaba da aiki, Fu'ad yana shuga airport ɗin baisha wahalar samun jirgi ba saboda yasaba da ma'aikatan wajan a recepsion ya zauna kasancewar sai nan da minti goma sha biyar jirgin zai tashi, shirun dayayi tunanin Su'ad yake har sannan yana jin ihunta sanda take faɗin _"Fu'ad come back please"_ ya share hawayan idanunsa yazaro glass daga aljihunsa yasakaya a fuskarsa suka ɓoye jan da idanunsa sukayi. Anty Jameela wacce guguwa tai sama da ita bata ajjeta ko ina ba sai gaban wata yar karamar bukka wacce a ido idan ka ganta bazaka taɓa zaton ko kaza zata iya shiga ta zauna ba bare mutum, bukkar ko kofar shiga babu amma tana tsayawa a gaban bukkar ta buɗe ta shiga da sauri tana kwalawa bokan kira harta zauna gaban sa inda ya bayyana "Ranka ya daɗe gashi na aiwatar da duk abinda kace" karɓar abinda ta mika masa yayi tareda wurgasa ya shuge cikin wata kwarya wacce abin yana shuga kwaryan takama da wuta, wani ihu Boka yayi tareda kecewa da dariya Yace "Burinki ya cika Fu'ad zai zama yanda kike so kallesa nan" lekawa Anty Jameela tayi cikin yar tukunyar dake gaban bokan zaune taga Fu'ad a wani waje da'alama recapsion na filin jirgi ne fuskar nan tasa ba walwala, ɗagowa tayi tana kallon boka bakinta har rawa yake wajan faɗin. "To maiyakeyi anan ɗin? kuma ina zashi tsoro nakeji karya bar kasarnan ban gama aikinba" "Ba'inda zaije gidama zai dawo yana kano daga gidansu wata yarinya yake wacce yake masifar so, nasoma ace itace zata mana aikin nan so ba yanda zanyi yarinyar tanada addini sannan babarta a tsaye take akanta da addu'o'i sau uku ina tura aljanu na suna dawomin da konan nan jiki shiyasa na haɗa aikin da tsohuwar budurwarsa Suwaiba duk yanda zakiyi kiyi dan ganin yaje legos sun haɗu da'ita dan itace cika makon aikin mu, ya cilla mata kullin magani wannan ki tabbatar yasha a cikin lemu zamu saka masa a zuciyarsa ya zarto nan gidanki ke kuma kina zuwa kije sashinsa ki buɗe lemu ki zuba a ciki dazaran yasha zance yakare" "To boka ina godiya amma inna buɗe lemu na zuba wani abu ai zai nuna alamar an buɗe" "Baki yarda da aikinmu ba, kenan kina shakku akai" da sauri ta girgiza kanta alamar A'A kafin tayi wata magana taji an watso ta wajan bukkar ta zura takalmanta ta soma tafiya sai da tayi nisa kana ta juyo fili ta gani fetal ba alamar bukkar ta ɓace ɓat🙆‍♀️ Prince rai ɓace ya sauka a garinsu, kai tsaye G R A ya wuce gidan mahaifinsa bayason a masarauta asan yadawo yasan halin mai martaba da sakawa zuciyarsa damuwa akan lamuransa shiyasa bai doshi gidan ba so yake saiya dawo dai dai tukunna, can kasan ransa yana son zuwa masarauta yaga Umma amma ji yake kamar ana fisgarsa zuwa gidan Abie. Anty Jameela ta gama zuba maganin kenan a cikin lemu ta futa shi kuma ya shugo gidan, haka kawai yaji kamar wanda ake jansa zuwa sashinsa inda baima cika zama ba, yana shuga ya buɗe fridge ya ɓalle murfin lemu yakafa kai yasha bako bisimillah😰kuskuren dayayi kenan, wani irin juya yaji kansa yanayi hajijiya ta ɗebesa luuuu yafaɗa saman kujera ya soma barci, Alhamdulillah Su'ad ta sami lafiya harta koma gida mun bar hospital na daina kuka a fili na rashin Fu'ad sai KUKAN ZUCIYA danake na goge komai na Fu'ad daga wayata kama da lambar sa hotunan sa duk wani abu da nasan zai tuna min da Fu'ad, ganin hankalin Su'ad ya kwanta yasa Mami da Ummi suke ta shirya shiryan bikin Su'ad da Fahad, haka shima Fahad tuni yasai sabon gida anan sharaɗaG R A katon gidane daya cikasa da kayan alatun more rayuwa duk wani abu dayasan Su'ad tanaso saida ya zuba a gidan a ɓangare guda ba karamin lefe ya haɗaba kamar wanda baisan ciwon kuɗi ba haka yake kashe su har saida Ummi tai masa magana, Mami da yaya Fatima sukaje suka dawo da santin gidan Yaya tasami Su'ad wacce yanzu batada inda take zama samada ɗaki sabida karta ga Fahad, har sannan banajin sonsa kawai zanyi biyayya ne "Kinga gidanki kuwa kamar na wata yar shugaban kasa gaskiyya ba karamin so Uncle ke maki ba, da mukaje faɗi yake Fatima dan Allah kalli gidan nan kiga in akwai abinda kikasan Su'ad tanaso wanda bansa ba dan Allah ki faɗamin nasaka" taɓe baki nayi ina juyawa yaya baya na ce "Daman zai faɗi haka mana tunda yasan yariga yagama da rayuwata, yarabani da farin cikina"mirmushi Yaya tayi ta futa daga ɗakin, tana aikawa da Su'ad harara Wasa wasa sai gashi yau alhamis saura kwana biyu ɗaurin aurena da Fahad har sannan bansakejin ɗuriyar Fu'ad inata dai saka idanu zuwansa tunda yace zai zo ɗaurin auranmu nasan tabbas zaizo ɗin, ba wani taro za'ayi sosai ba kuma ma ɗaurin auran a karaye ne shiyasa tun ranar juma'a da yamma Mami dasu yaya fatima sai wasu matan yayun ummi suka wuce karaye. Da yamma ina zaune nida fadila yar wan ummice kawata ce sosai tun yarinta haka kawai nakejin faɗuwar gaba wacce narasa ta maice na ɗora kaina saman kujera ina jiyo Fadila tana waya dasu Mami kamar daga sama naji kamshin turaransa ban buɗe idona ba har sanda naji sallamar Ankul wanda ko tantama babu nasan tare suke da Fu'ad, ilaiko muryarshi najiyo yana gaisawa da Ummi data futo daga ɗakinta, muryarsa fes kamar bayada wata damuwa, banbuɗe idonaba har saida na tabbatar da sunbar falon zuwa sashin Ankul sannan na buɗe na ɗauki wayata na shuge ɗakina inajin yanda kirjina da kaina suke bugawa "Ameen maiyasa maiyasa zakazo ayanzu so kake ka hanani karasa biyayyar danake shirin yiwa mahaifina kanason tarwatsa zuciyata ne" kwanciya nayi lamo har sanda naji wayata tana kara koda bansan wake kiranba amma na tabbata Mami ce dan ring ɗinta daban yake a wayana "Dota kinci abinci kuwa" "E!" nabata amsa ina sauraron abinda zatace. "kaiwa Ankul wayanki zamuyi magana na kira tasa baya shuga ko baidawo ba?" Inama zan iya yiwa Mami karya danace mata bai dawo ba, amma bazan iya ba dole na mike nabi hanyar zuwa ɗakinsa, da sallama na shuga suna zaune su biyu da'alama magana suke mai mahimmanci ganin yanda hannunsu yake sakale cikin na juna, banko kalli inda Fu'ad yake ba namikawa Ankul waya nace "Mami ke kiranka, bansan maita gaya masa ba nidai ina tsaye naga ya fuce da sauri ko wayar tawa bai bani ba, na fara tafiya zanbar ɗakin naji Fu'ad ya ruko hannuna, na juya ina kallonsa hawaye na zarya a fuskata na tausayinsa ganin yanda ya zabge lokaci ɗaya kamar wanda yai jinya banyi aune ba kawai naji na fashe da kuka hannu yasa ya toshe bakina murya kasa kasa Yace "Princess rufa mana asiri so kike Ankul ɗinki ya jiyomu" da sauri yasa hannunsa a cikin jakarsa ya ciro karamin akwati mai ɗan karan kyau yasakamin a hannuna ya koma saman gado ya kwanta ni kuma na futa daga ɗakin da sauri, banga Ankul ba da'alama baya gidan. Ankul kai tsaye gidan Baban su Zainaba ya wuce, har ɗakin baban yashuga yazauna yana gaida Baban dake masa wani kallo kamar zai kai masa duka. Yace "Yanzu gobene ɗaurin auranka amma ka kasa zuwa ka gayamin sai yayarka ce take gayamin saboda bakuda zumunchi kun rainani ko saboda ni banida kuɗi, to bazan wakilceka ba kaje ka nemi wani bani ba" taɓe baki Fahad yayi tareda mikewa ya ajje masa ledar ɗinkin da Mami tace yakawowa Baban sannan yace "Badamuwa Baba inma bakaje ba bazan rasa wanda zai wakilceni ba barema da kaina zan iya karɓarwa kaina aure" yana gama faɗar haka yafuce daga ɗakin, dai dai sannan Zainaba tashugo ɗakin a ruɗe ita bata taɓa jin zancan auran ba sai yanzu innarta ke sanar mata, zubewa tayi gaban baban tana rusar kuka "Wallahi baba ka cuceni kaine kayi silar rabani da Fahad gashi yanzu inaji ina gani zaiyi wani auran ka kasa taɓuka komai😰kilama tazo ta haifi namiji shi kenan dukiyar da muka sakawa rai tabar tamu" Dariya Baba yayi kamar wani sabon kamu ya zira hannunsa a aljihu yafuto da wani kullin magani yana nuna mata yace "Kalli wanan ɗazu na samosa a wajan wani malami badai gobene ɗaurin auran ba to yanda aka kaimasa amarya haka za'a ɗakkota kedai ki zubamin idanu kawai inada abinda nake kullawa" Sosai Zainaba take murna dajin maganar da Baban yafaɗa hakan yasa ta koma ɗakinta zuciyarta fes da farin ciki. *RANA BATA KARYA* Tun sassafe samarin gidanmu suketa shirin tafiya karaye dan shaida ɗaurin auran Aminatu da Fahad, sosai Fahad yake cikin farin ciki marar musaltuwa kallo ɗaya zakayi masa ka gano farin cikin dayake ciki, yana sanye cikin Fara kal ɗin shadda yasha malum malum shugarsa shida Jabeer iri ɗaya ce, ko'ina ka hangosa baki buɗe sai zuba murmushi yake duk sun shirya Fu'ad kawai suke jira yagama shiryawa su wuce, Tsab yagama shirinsa yafuto yana gyara zaman rawaninsa suka jero shida Fahad zuwa wajan da motocin dazasu shuga suke. Ina tsaye baki window ina leka compound burina kawai na saka sa a idona nai masa kallo na karshe, irin kallon danasan har abada bazan sake masa irin kallon ba. Da sarsarfa yake tahowa kasancewar su Fahad sunyi masa nisa dan harsun shuga mota shi ya tsaya amsa waya, binsa nake da kallo yanda yayi kyau cikin bakar shadda ya ɗora malum malum ta farar shadda wacce akayiwa aiki a gaban rigar da bakin zare, rawaninsa da takalminsa harma da agogon fatar dake hannunsa duk bakake ne, kamar wanda akace ya juyo muka haɗa ido cak ya tsaya yanamin murmishi tareda ɗagomin hannu yaci gaba da tafiya, murmushin da nakejin har abada bazan taɓa mantawa dashi ba kasancewarsa na karshe da yayimin ina kallo ya shuga motarsa wani yaja wanda nake zaton tare sukazo saboda kayan gidan sarauta dana hango a jikinsa da'alama dogari ne,komawa nayi na zauna gefan gado tareda jan tagumi, ina nan zaune har barci ya ɗaukeni ban sani ba saidai farkawa nayi naji gidan yakaraɗe da hayaniya na buɗa ido da sauri na sakko daga gado dai dai da shugowar Fadila tana murna da faɗin yarinya bani tukwaici nagaya maki wata magana...✍️ 07039793439 [6/4, 7:48 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA *Na gaisheku ƴan group ɗin KUKAN ZUCIYA comment ɗinku na sani nishaɗi wannan page ɗin gaba ɗaya nakune kuji daɗinku* "Wanne abu zaki gaya min da har saina baki tukwici nasan dai cewa zaki an ɗaura min aure da Fahad koba haka zaki faɗa ba" ban jira Fadila ta ce komai ba na faɗa bathroom na kunna famfo ruwa na zuba na fashe da matsanancin kuka "Shikenan shikenan yanzu na zama mallakin Uncle haba kaddara mai yasa zaki mana haka maiyasa zaki rabani da farin cikina wayyo Allah wayyo zuciyata wayyo Ameen" ta karasa faɗa da karfi tareda nemar waje na zauna na fashe da matsanancin kukan takaicin rashin Prince Ameen, Mami gaba ɗaya hankalinta na gida hakan yasa ana gama ɗaurin aure itada Momy matar wan Ummi suka juyo gida, Ba wani shagalin biki akai ba sabida yanda bikin yazo ba shiri ga kuma rasuwar Daddy dako wata biyu bai yi ba, da mangariba Mami da sauran tsirarun ƴan uwa suka mika ni gidan Fahad, gidan da nasa a raina zan tabbata ina Kukan Zuciya a cikinsa, basu wani jima ba aka tafi aka barni daga ni sai halina tunda muka shiga gidan nake kuka ta cikin mayafin daya lulluɓe min duka jikina basu jima da tafiya ba uncle ya shigo, sallamar dayai tayi dai dai da bugawar zuciyata wanda yai sanadin dana kuma fashewa da kuka ya zauna kusa dani ya buɗe mayafin daya lulluɓe ni yana murmushi saidai annurin fuskarsa lokaci ɗaya ya kau, ya saki mayafin jiki sanyaye, bai cemin uffan ba haka nima bance masa, nadai lura jikin Uncle yai matukat sanyi ganin ya fita yasa na kwanta kan gadon ina kuka sosai, Fahad mai saukin hali kullum kalaman lallashi yake bina dashi musamman ganin naki sakin jiki da shi, kyautatawar Uncle a gareni yasa nabar kukan fili na rashin masoyi na koma kukan zuciya, Uncle na matukar kokari sosai ganin ya kwantar min da hankali komai na gida shi yake yi tun bana sakin jiki da shi harna ware na saki jiki muka koma kamar da sanda muna gida, har sannan mikin son Ameen Fu'ad na nan ɓoye cikin zuciyata nakan tina dashi a kullum nakan kuma so nasan a wanne hali yake yanzu ina yawan ɗaukar wayar Uncle a ɓoye nayita kallon hoton Fu'ad ina kukan zuciya wani bin sai nayi kamar zan kira lambar sa sai kuma na tina haramcin hakan na ajje wayar na ɓuya a ɗaki nai kuka sosai tareda addu'a Allah ya cire min sonsa a zuciyata, sanda hutun da aka bawa Uncle a wajan aiki ya kare ya koma aiki randa yatafi sai naji gidan shuru kewar gida ta kamani gashi muna hutun school, Zaune suke gaban malam na gangare wanda yasha uban rawani da malum malum kamar malamin gaske, Zainaba tana kuka take cewa "Dan Allah malam ka taimakamin inason mijina, gashi ya sakeni har saki uku, ya auri wata, sonake yasaketa yazo yamaidani acusa masa tsanarta sosai yaji nan duniya ba warda ya tsana sama da ita ya korata gidansu da takardar saki uku" malam ya zana wata kasa dake gabansa ya girgiza kai ya ce "Auran nan babu rabuwa aciki duk wanda yace zaija to komai zai iya faruwa dashi sannan kema babu sauran zama ke dashi sai dai kizaɓi abinda kike so bayan wannan" "Malam ka taimakeni!" Ungo wannan yamika mata wani kullin magani yace "Ki zuba sa a inda kika tabbatar zai taka koya tsallaka, inhar kikayi haka to ba abunda zai iya yiwa matar tasa zai zama fanko awajanta ita kuma zata kasa jurewa harta kai ga ta nemi saki, bayan yasaketan kizo ki gayamin zansan yanda za'ayi sai'a maida auran naku" cikeda murna tabasa kuɗin daya butaka ita kuma ta dawo gida ta tisa baba agaba akan ya kira Fahad yace yana son ganinsa yanzu, lokacin Uncle na shirin barin office dan haka ya shaida ma Baba da gashi nan zuwa yanzu insha Allah, Da gudu Zainaba tashugo cikin gidan tun ɗazu tana tsaye kofar gida tana jiran zuwan Fahad tun daga nesa data hango motarsa ta dawo gidan ta kunce kullin maganin daga gefan zaninta ta zuba sa a kofar ɗakin Baba, mahaifiyarta data futo daga ɗakinta tabita da kallon tuhuma "Zainaba mai kikeyi haka a kofar ɗaki ba sallamar Fahad nakeji ba, waima maine wannan a hannunku" Baba daya leko daga ɗakinsa yace. "Kefa mairo kin fiya saka ido ina ruwanki da maine a hannunta ke Zainabu cewa Fahad yashugo ina ciki" Fahad yashugo da sallama yana gaida Innah mairo fuskarta cikeda fara'a take amsa masa gaisuwar, yana shuga ɗakin Baba Zainaba tayi wani tsalle tana murna harda taka rawa, a kasa ya zauna yana gaida Baba, ta inda yake shuga bata nan yake futa ba faɗa yake sosai "Yanzu saboda rashin zumunchi irin naku ace kayan abinci ma bazaku iya saimin ba saina roka kuna kallon halin danake ciki aikima ya gagareni amma bazaku rinka tausayamin ba wannan ba halin ubanku bane, ubanku mutumin kirki amma kaida yar uwarka mahaifiyarku tashuga tsakani na da ku" Fahad dariya ma abin yabasa daya tuna ko karshan wata saida Mami tagaya masa ta turawa Baba kayan abinci, shine yanzu zai zo yana masa mita "Ayi hakuri baba ban zaci wanda Mami takawo harya kare ba yanzu bari naje zan aiko maka dasu" "Basai ka aiko ba kabani kuɗin kawai nasiya da kaina" mikewa Fahad yayi yana murmushi yafuta, mota yaje ya ɗebo kuɗi ya kawo wa Baban sannan yafuta, har sannan Zainaba tana zaune kofar ɗakin daɗi ya kume ta ganin har sau biyu yana taka maganin. Yau sosai nakejin nishaɗi hakan yasa da wuri na kammala abinda zanyi nai wanka ina zaune gaban madubi na gama tsantsara kwanliya wacce najima banyi irinta ba tun kafin rasuwar Daddyn mu, doguwar rigar material nasa wacce takama jikina tamin kyau sosai na feshe jikina da turere mai kamshi, na gyara gashina dayasha kalolin mayuka sai kamshi yake da kyalli, ban ɗaura ɗan kwalinba na ajjesa saman kujera ina kallon agogo karfe huɗu saura kwata, mamaki nake maiya hana Ankul dawowa bayan yacemin karfe biyu zai dawo zama nayi na ɗakko wayata na kunna data nahau online hira muke da Yaya Fatima kiran Fahad yashugo wayan nawa da sauri na ɗaga cikeda shagwaɓa Nace "Shine kayi zamanka har yanzu baka dawo ba bayan kace karfe biyu zaka dawo" ina jiyo sanda yai murmushi mai sauti "Kina son nadawo ne, inna dawo maizan samu mai kika tanadarmin?" "Na tanadar maka da komai,kuma ni tsoro nakeji nafison innayi motsi na ganka kusa dani hakan yana faranta min rai" "Da gaske to gani nan a hanya" kashe wayan yayi saida yayi sallar La'asar a masallaci dake ɗan nesa da gidansa kaɗan sanna ya karasa gida. Horn ɗin motarsa dana jiyo yasa na futa da sauri na buɗe masa get,yashugo da motar na maida gate ɗin na rufe na karaso wajan motar na buɗe masa murfin motar, yafuto yana dariya tareda sakani cikin jikinsa ya sumbatar bakina yace "Kinyi kyau sosai besty bakiga yanda doguwan rigan nan tai maki kyau ba" sosai naji daɗin yabon da yai min hakan yasa na kuma shugewa jikinsa ahaka muka jera zuwa ciki, saida nakaisa har ɗakinsa na haɗa masa ruwan wanka ya shuga yana tsokanata inzo na tayasa wanka, na futo daga ɗakin da gudu ina dariya, Allah yasani kunyarsa nakeji banajin akwai wata rana da zatazo wacce zan iya tayasa wanka, ina nan falo zaune ya futa sanye da wando 3 kwata da farar t shart mara nauyi, kusa dani ya zauna ya jawoni jikinsa yana shafa gashin kaina "Waini yaushe za'a daina jin kunyata saboda Allah ace wankama har yanzu da kaina nake baza'arinka yimin ba" rufe idona nayi alamar jin kunya ina dariya kasa kasa nace "Nifa bazan iya ganinka ba kaya ba ajikinka ai kunya zanji" dafe baki yayi yana dariya kasa kasa "Ok yanzu nagane laifin nawa ne, aiko yazama wajibi yau saina cire wannan kunyar dake tsakaninmu Allah yakaimu dare" murmushi kurum nayi tareda mikewa na kawo masa abinci na ajje bisa carfet dan nasan Ankul tun tuni bai fiyason cin abinci a dannig ba, sosai yaci abincin yana tsokanata inata dariya muna nan zaune muna hira har aka kira mangariba yafuta masallaci ni kuma na wuce ɗakina nai alwala. Ankul bai shugo gidan sai wajan karfe takwas da rabi lokacin har nayi shirin kwanciya bayan nayi wanka na saka night wear na zuba humra sai tashin kamshi nake banji shugowar sa ba kasancewar harna fara barci sai mutum naji cikin bargo ya haɗe jikina da nasa, na buɗe baki ina shirin yin ihu ya saurin haɗe bakina da nasa, yanda yake kissing ɗina yasa jikina yaɗauki rawa Sosai yake min wasu kalar abubuwa wanda sam bansan dasu ba, gaba ɗaya yafuta hayyacinsa niko har sannan jikina rawa yake musamma sanda naji yana kokarin shuga jikina sosai nake kuka da rokonsa amma baimasan inayi ba saidai cak ya tsaya yana maida numfashi lokacin dayai kokarin shuga jikina J ɗinsa yaga tai wani irin kankancewa da sauri ya janye jikinsa daga jikina ya kwanta gefena yana maida numfashi, ban fuskanci komai saima zato danai ko rokonsa danake ne yasa ya tausayamin yafasa abinda yai niyya amma yanda naga yana numfashi yasa na kunna light da sauri tausayinsa ya kamani ganin yanda ya haɗa gumi aruɗe nace "Ankul lafiya maiya sameka" janyoni yayi jikinsa tsawon lokaci yana cikin wani yanayi yanda idanunsa sukayi ja yasa na ruɗe na soma kuka, "Ankul na amince gani kayi abinda kai niyya dani inda zaka dawo dai dai amma ni tsoro...hannunsa yasa saman laɓɓana alamar nayi shuru, hawaye naga sun zuba daga idanunsa yace "Bazan iya maki komai ba Su'ad bansan iya tsawon lokacin dana ɗaukaba batare dana gano cewar bani da cikakkiyar lafiya ba nidai nasan har sanda muka rabu da Zainaba lafiya ta kalau" sam ban gane inda zancan nasa ya dosa ba hakan yasa gaba ɗaya hankalina ya kuma tashi aruɗe nace "Bakada lafiya Ankul tashi to muje hospital kona kira Dr Hafis yazo ya duba ka" "Ba rashin lafiyar jiki nake nufi ba kalli nan" yafaɗi haka yana nunamin J ɗinsa, kallon inda ya nunamin ɗin nayi da sauri na runtse idona saboda gamon danayi, Fahad yana murmushi yace "Buɗe idonki ki kalleni ki gane rashin lafiyar danake nufi ya zamuyi" yanzu kam nagano abinda yake nufi "mu gayawa Mami nasan zata samo maka magani" "A'a karmu gayawa kowa mubar wannan sirrinmu ne, zan nemi magani bansan da matsalar bama da tuni nasamo magani, wannan yazama sirri nidake karki gayawa kowa dan Allah" "Haba Ankul tayaya zan iya gayawa wani wannan matsalar ai tamuce dagani sai kai" rungumoni yayi jikinsa har barci ya ɗaukeni baiyi barci. Fahad dayaga Su'ad tayi barci tashi yayi yai wanka ya gyara jikinsa ya ɗakko system ɗinsa ya soma binciken magani daya dace ya sha. Tun sanyin safiyar lahdi yaketa shirya kayansa cikin trabiling bag fuskarshi fal da damuwa ga kansa dake masifar sara masa saboda damuwa idanunsa sunyi jawur sosai kamar wanda yai kuka,kofa yabi da kallo ganin tayi motsi cak ya tsaya yana bin Khadija data shigo ta zaune kan sofa ta fashe da kuka "Yaya Prince yanzuma tafiya zaka kuma yi ka barni ni ɗaya?" Khady ta faɗa cikin kuka sosai, rigar hannunsa ya jefa saman bed da sauri ya tsugunna gaban Khady yasaka hannunsa cikin nata yanaji inama shine yake wannan kukan inama shima zai iya kukan nan ko zuciyarsa zata masa daɗi "Khady yi shuru dan Allah ba laifina bane laifin Abie ne na gaya masa bana son tafiyar nan amma ya kafe dole wai saina fara aiki a asibitin legus nima zanso ace an barni nan na rinka ganinki ko yaushe amma insha Allah na maki alkawari zan rinka zuwa duk karshan mako please Khady ki daina kukan nan" cikin kuka Khady ta gyaɗa kanta tana bin ɗan uwan nata da kallon tausayin rasa masoyiya da yai, Khady da Juhaina daketa rawar kai tare suka raka Prince har filin jirgin sama saida yatafi sannnan suka dawo gida, a legos gida da motar hawa asibitin dazai fara aiki dasu suka basa kai tsaye yafara aikinsa ba ruwansa da sabgar kowa indai ba hospital zai je ba to bazaka taɓa ganinsa a waje ba kullum yana gida kamar mace, Sauri sauri yake shirin futa bayason makara saboda karfe tara yanada feshen ɗin dazaiwa c s, takwas saura ya shuga hospital ɗin tun daga resepsion yake amsa gaisuwar ma'aikata yanda suke basa girma kai kace shine mai asibitin a mutumche yake amsa gaisuwar saidai fuskar nan tasa tamke ba ko ɗigon fara'a haka yake haka suka saba ganinnsa shiyasa basu wani damu ba. Bai tsaya a ko'ina ba sai kofar katon office ɗinsa tamkar falon wani gidan saida ya zauna saman kujera ya sauke ajjiyar zuciya tareda cusa hannuwansa duka biyun cikin gashin kansa yana fuzzar da iska mai zafi daga bakinsa, shirye shiryan shuga tiyata yafara yi ta hanyar canza kayan jikinsa ya shuga ɗakin tiyatan. Anty Jameela na murmushi ta damkawa Suwaiba rafas ɗi nyan dubu dubu guda uku "Ga somin taɓin kuɗin aikinki nan bazan baki sauran ba sai aiki ya kammala" Murmushi Suwaiba tayi daɗi takeji sosai a ranta da ganin wannan uban kuɗin wai duk nata ne hakan yasa tace "Bakida damuwa Hajiya aiki kamar angama sane gobe insha Allah tun safe zanwa garin legas tsinke na ruga naga inda yake da gidan dayake zaune abu ɗaya zaki bani makullin gidan" "Au kinga na manta wallahi gashi" tamika mata makullin bayan ta ɗakkosa daga jakarta, mikewa Suwaiba tayi tana wani juyi kamar tana gaban mijinta🤭dariya Anty Jameela tayi bayan taga futar Suwaiba daga ɗakin, harda tsallanta na murna gobe iwar haka burinta ya cika an ɓatawa Fu'ad suna shida sarautar saidai yagani anayi💃 Fu'ad tunda yashuga asibiti bai futo ba sai tara na dare gaba ɗaya agajiye yake jin kansa, ta restaurent ya biya yayi take away sannan ya wuce gida wanka yafara yi saboda gajiyar daya kwaso, jiyake inama yanada mata tabbas yau da saidai su raba gajiyar nan, abincin yaci yaɗan hau online bai jima ba yafara jin barci haka yasa ya kashe datan ya wuce bedroom. Dare yayi sosai ahankali take juya kanta cikin barci kafin ta farka a firgice tana salati, salatin datayi shiya tashi mai martaba dake kusa da'ita yana barci, a kiɗime ya farka yana tambayar "Asiya lafiya naganki haka maiya sameki wani abune ya faru?" "Lafiya kalau ranka ya daɗe amma wani mafarki nayi, hankalina yatashi anya ko One boy yana lafiya" Mai martaba maida kansa yayi ya kwanta tareda lumshe ido kana yabuɗesu akan matar tasa "Lafiya kalau ɗanki yake ɗazuma saida mukayi waya dashi lokacin yana hospital yace bai koma gida ba" Umma sakkowa tayi daga kan gadon ta shuge toleit mai martaba yabita da kallo yana sakejin son matar tasa uwar gidansa yana sake shuga ransa musamman ganin yanda ta damu da lamarin Fu'ad ko yaushe batada magana saita Ameen yayi kaza ko yaranta data haifa bayajin tana yiwa so kamar yanda takewa Fu'ad, da Khadija duk da sauran matansa suna zargin son datakewa Fu'ad badan Allah bane dan tana ganin nan gaba shine sarki shiyasa take sonsa, shidai yasani ba haka bane son datakewa Fu'ad tun yana yarone sau tari Ummu kafin ta rasu tasha bata Fu'ad ya jima awajanta shiyasa suka shaku sosai, Umma tafuto ta shimfiɗa dadduma ta tayar da sallah tana rokon Allah yakare mata ɗanta ya nesantashi daga abinda tayi mafarkin yasamesa yanzu, sanda ta gama addu'o'inta ta shafa ta koma ta kwanta sannan ta lalubi wayarta taga karfe 03:44 am lambar Fu'ad ta buga tajima tana ring sannan yaɗaga aɗan tsorace yake tambayar Umman lafiya "Lafiya kalau One boy kawai cewa nayi bari na tashi ɗana ya ribaci daren nan da koda raka'a biyu ce ta nafila" dirowa yayi daga kan gadon yana murmushi yace "Na gode Ummana na mike kuwa alwala ma zanyi nayita sallah daga nan har safiya ina rokon Allah yakarawa Ummana lafiya da nisan kwana tayita bani kulawa har zuwa taga jikokina" dariya Umma tayi ta kashe wayar ta shige jikin mijinta tana murmushi, Fu'ad bai koma barci ba sai bayan sallar asuba daya dawo daga masallaci ya koma barci bayan yayi karatun kur'ani izifi uku yai azkhar sannan yakoma ya kwanta,dan yau bazai shuga hospital ba sai huɗu na yamma. Karfe shida dai dai jirginsu Suwaiba ya sauka a garin legos ikko ikon Allah cunkus ɗakin tsumma😹itada kawarta ne hotal suka kama suka ɗan huta bayan sallar mangariba Suwaiba ta wuce gidan Fu'ad, ta tarar baya nan hakan yasa tasa makulli ta buɗe karamar kofar shuga gidan ta shuge ciki ba kunya, ɗakuna biyu ta gani cikin falon ta murɗa handling na kofa ɗayar tajita a rufe hakan yasa ta nufi ɗayar tana murɗawa ta buɗe ta shuga, wanka tayi ta shirya cikin wasu shegun kaya kanana masu masifar kyau da fusgar hankali, ta feshe jikinta da kalolin turarukanta da wanda Anty Jameela tabata wanda ta karɓo daga wajan boka🤭 Takwas dai dai Fu'ad yashugo gidan bakinsa ɗaukeda addu'ar shuga gida harda sallamarsa kamar wanda yabar mutum a gidan, ajje ledan abincinsa yayi saman kujera yana shirin shuga ɗakinsa yaji an rungumosa ta baya ba karamin tsorata yayi ba saboda shidai yasan shi kaɗaine agidan, bai ankare ba yaji an soma shafa jikinsa ana kokarin ɗora hannu kan J ɗinsa, afusace ya jiyo yana karanta ayatul kursiyyu domin azatonsa gamo yayi saidai wazai gani inba gizo idanunsa sukai masa ba Suwaibace wannan a fusacen dayake ya danki wuyanta yana faɗin "Malama maiya kawoki gidana maiya sake dawo dake rayuwata bayan yaudarar da kikamin saboda kin maidani sha sha sha shine yanzuma kika dawo ki yaudare ni?", Suwaiba da idanunta suka furfuto tafara hango mutuwa saboda yanda ya rike mata makogwaro tace "Ka sakeni zangaya maka wanda ya turoni" bai saketanba saima kara rike mata makogwaro dayai idanunta dayaga ya firfito tana kakarin mutuwa yasa ya wurgata ta bugu da kujera tasaki ihu bai tausaya mata ba yasa kafa yatake hannunta "Zaki gayamin ko saina haɗaki da hukuma" kanta take girgizawa tama kasa magana sabida azabar da hannunta da kanta keyi,wayansa ya ɗakko ganin yana shirin kiran yan sanda yasa ta magantu "Anty Jameela ce ta turoni na shugo rayuwarka muyi rayuwa na zama karuwarka saboda batason kazama sarkin bare" dafe kansa yayi ya koma saman kujera ya zauna kamar kuma wanda aka kunna yamike ya fara jan kafafun Suwaiba bai tsaya da'ita saida yakaita kofar gate can waje ya wurgata ya koma ciki ya ɗebo sauran kayanta ya watsa mata "Wannan yazama na farko kuma na karshe dazaki kuma shugomin gida, ki gayawa wacce ta turoki insha Allah nafi karfinta itada duk wani sharrinta, kar nake kallonta a tafin hannuna,harya juya zai koma ciki yadawo yamika mata hannu "Ina kika sami makullin da kika buɗemin gida" "Anty Jameela ta bani a sashin Abie ɗinku ta ɗakko" murmushi mai ciwo Fu'ad yayi yamika mata hannu "Bani makullin" tamika masa yakoma ciki yana sauke ajjiyar zuciya.....✍️ Saura kiris pages su daina fitowa na daina posting ɗin book ɗin nan a kowanne group sai group ɗin Kukan zuciya real fans indai har kinsan kinason cigaba da bin labarin nan to masa yimin magana ta wannan lambat nai adding ɗinki a group 07039793439 [6/4, 7:48 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 17&18 Dakyar Suwaiba ta koma hotal ɗin data sauka saboda wani azababban ciwo da wuyanta yake mata lalle ta tsallake rijiya da baya a irin rikon dayai mata tabbas zai iya kasheta tasan inya kasheta yakashe banza saboda ba wani gata ne da ita ba, iyayanta bawasu masu hali bane tasan kasar nan tamu anaji ana gani sai a rufe maganar tunda shi ɗan manya ne bakaramar nadama tayi ba data bari kawarta ta ruɗe ta harta karɓi wannan aikin na Anty Jameela datake ganin bashida wani wuya. Yau da nishaɗi muka tashi kasancewar sunday ne Uncle yana gida bai fita hospital ba kamar yanda muka saba tare muke komai na gidan yanda Uncle yake kula dani yasa gaba ɗaya nama manta da Fu'ad gaba ɗaya na mallakawa Uncle zuciya na, bayan munyi sallar azahar wanka mukayi tare muka fito danning zamuci abinci, ina sanye cikin doguwar rigar atamfa A shape wacce ta matukar zaunawa a jikina ni kaina nasan nayi kyau saboda yanda nayi kiba na kara haske, ga wani ɗauri danayi sosai Uncle ya yaba da kwalliyar tawa sai bina yake da kallo, jerowa mukai zuwa wajan danning ɗin ina tsokanarsa ina dariya tare mukaci abincin kamar yanda muka saba ciyar da juna, falo muka koma ya kunna kallo ni kuma na kwantar da kaina saman cinyarsa ina shirin barci, buga kofar da'akai yasani mikewa zanje na buɗe kofar "Besty keda kika soma barci ki zauna ni na buɗe" harara nai masa irinta masoya nace "Saidai ayi riga rigayan zuwa"kafin na rube baki yatafi da sarsarfa nima na take masa baya ya rigani zuwa saidai ganin waɗanda suke bakin kofar yasa shi yin turus kunya duk ta kama sa ganin kayan dake jikinsa Mami suka shigo falon da sallama itada Ummi a kunyace yadawo falon yana wani sinkuyar dakai kamar wanda yaiwa sarki karya🤭 Ina jikin Mamina na makalkaleta Ummi sai bina take da kallo nasan itama cewa zatayi nayi kiba, danko ni nasan ba karamar canzawa nayi ba, Mami data kasa daurewa tace "kai masha Allah Dota ɗita nayi murna sosai Allah ubangiji ya inganta nasan wannan kiba bata haka nan bace mai dalili ce da'alama nakusa samun jika" da gudu na mike na shuge kichin na kawo masu lemu da cake Allah yasa inada abinci hakan yasa na haɗo masu dashi, Ankul yana gama gaisawa dasu ya koma ciki danba karamar kunya yajiba yanda suka gansa. Su Mami sunjima sosai sai bayan sallar mangariba suka tafi. Anty Jameela na tsaye gaban dinning tana shiryawa Abie abinci da lamun dayasha magungunan data amso a wajan boka, wayarta dake ajje kan dinning tashuga ruri ganin Suwaiba ce mai kiran yasa ta saurin ɗagawa tareda jan kujera ta zauna, jin abinda Suwaiban ke faɗa mata yasa ranta yaɓaci bata jira futawar Abie ɗinba ta wuce ɗakinta ta kule can ciki bayan ta dannawa ɗakin key Wayan boka ta kira tana sanar masa abinda Fu'ad yamata "Kinga ki futa hanyar yaron nan ba abinda zamu iya akansa tsaye yake kan addu'a da azkhair gashi yana yawan karatun kur'ani gefe kuma ga watanan datake kara masa addu'ar kariya, kinsan aljanu nawa natura suna dawomin nikam na futa hanyar yaron nan bazai kassarani ba" Anty Jameela ranta ɓace ta futo daga ɗakin nata saurin saita kanta tayi ganin Abiee zaune bisa dinning yana aikawa cikinsa lemu, zama tayi kusada shi tana kara masa sannu da hanya, saida yagama cin abinci yabita da kallo "Narasa maiya zaunar dake agarin nan kinki komawa kaduna" taɓe fuska tayi "Ni kawai garin yafuta araina nafison zaman nan kaima kabar aikin nan ka dawo nan ka amshi sarautarka" murmushi yayi kawai yana danna wayarsa. "Niko Alhaji nace maizai hana yaron nan Ameen asama masa wata a aura masa shekarunsa kullum daɗa ja suke yakasa ajje iyali" "Kamar kin shuga raina abinda yake cimin rai kenan ko jiya nai masa magana amma sai cewa yayi shi bayanzu zaiyi aure ba shekarunsa fa yanzu Talatin da shida, inaga zanyiwa mai martaba magana a haɗasa da Juhaina ta wajan mai martaba" da sauri Anty Jameela tace "Ai kuwa karkayi haka yarinyar nan rannan naji suna hira da Khady tana faɗa mata ɗan wazirin gombe ke sonta" shuru yayi baice komaiba, jin alamun bazai sake cewa komaiba yasa Anty Jameela tace "Ni badan kar'ace naso kaina ba sai nace inba damuwa a haɗasa da Baraka kanwata kaga itama taki futar da wani tsayayye suje can su sasanta kansu" nan ma shuru Abiee yayi baice komaiba sai can yace "Tabbas kinyi hange mai kyau gobe zan tura makama su tambaya mana inta amince ni banida damuwa da Ameen lamarinsa yafara bani tsoro aure zan masa saidai kawai atura masa matar legos" yana gama faɗar haka yamike yafuta. Washe gari tana ganin Abiee yafuta itama ta fuce zuwa gidansu gargaɗin Baraka tayi akan indai aka tambayeta tanason Fu'ad ta amsa da E kuma karta sake tasa soyayyarsa aranta dan bazama ne zai kaita ba aiki zatai mata karta sawa kanta wata soyayya. Wasa wasa saiga batun auran yakankama tuni har an tsaida rana abinka da manya duka sati biyu aka sanya bikin, ango yanacan baisan abinda ake ba, dan tunda yasa kafa yabar garin bai kuma zuwa ba mai martaba yana kai masa ziyara akai akai haka Abiee ɗinsa Umma ko suna waya kullum, yau tun safe yana kwance bashida lafiya wani azabanban ciwon ciki yake kamar zai mutu, wayar abokinsa Usman yakira yana sanar masa bayada lafiya, Usman ya shaida masa baya gida ya shuga makaranta yanada class, Dr Haris yakira yace gashi nan zuwa yadubasa. Saida yagama aunasa yakoma ya zauna cikeda damuwa "Gayses kana cutar da kanka dayawa, kanada bukata amma kaki ajje mace saboda wani banzan dalilinka, inma bazakai aure ba maizai hana kasami wacce zatana sauke maka bukatunka ga matanan dayawa a gari sai wacce ka zaɓa, kanada kuɗi kanada kyau babu macan dabazaka iya mu'amala da'ita ba, amma ka tsaya kana neman kashe kanka" murmushi kawai Fu'ad yayi "In ka gama sharhin bani maganin dazan sha ka fucemin daga gida dankai kana abu dolene saina bi ra'ayinka kai barima na maka ta mahaukaci duk matan nan kallon maza nake masu, tunda na rasa Princess banajin akwai sauran wacce zata sake burgeni" "Faɗa kake amma ka bani dama wallahi yau saina kawo maka wacce zata ɗebe maka kewar Princess ɗin" ɗagowa Fu'ad yayi yana kallon Haris batareda yace komaiba, magani Haris yaje yasiyo masa ya kawo masa sannan yayi masa sallama. Washe gari yana office saiga Haris dawata kyakkyawar yarinya kallo ɗaya Fu'ad yayi mata ya kauda kansa yana ta'awizi, zare glass ɗin idanunsa yayi wanda yazame masa jiki ko yaushe ka gansa yana manne da idanunsa wanda ba karamin kyau yake kara masa ba, kallon Haris yayi tareda haɗe gira ya ɓata rai afusace yadakawa yarinyar tsawa wacce tasata fucewa da sauri jikinta yana rawa. "Haris na rokeka da girman zatin Allah kataimakeni karka sakani cikin wannan harkar taku, kaima da kake ciki kullum addu'a nake maka Allah yaganar dakai gaskiyya, maye amfanin zina, maiye daɗinta maye daɗi acikin saɓon ubangiji..."Ya'isheka Fu'ad" Haris yafuce daga Office ɗin afusace yanacin alwashi. Ranar asabar da dare yagama shirinsa na kwanciya wayarsa tayi kara da sauri ya ɗaga cikeda girmamawa yake gaida Abiee ɗin nasa, anan yake shaida masa an ɗaura masa aure harma an kawo amarya nan ɓangaransa na cikin gida, gobe in Allah ya yarda za'a rakota nan" ba karamin tashin hankali yashuga ba yana gama wayada Abiee yakira Umma kamar zaiyi kuka yake tambayarta "Umma da gaske abie yake anyimin auran dole" dariya maganar taba Umma saida taɗan dara sannan tace "Auran dole kuma One boy kamar wata mace, da gaskene an ɗaura maka aure da Baraka kanwar Antynku Jameela" tsaye yamike da sauri zaiyi magana Umma ta katsasa da "Kar kace komai kayi addu'a Allah yasa hakan shiyafi alkhairi, yarinyar batada matsala nayi bincike akanta karka damu Allah yabaku zaman lafiya yakawo zuri'a ɗayyiba" batare dayace komai ba yakashe wayar ya maida kansa ya kwanta yanajin wani ɗaci a zuciyarsa, rasama mai zaiyi yayi hakan yasa ya ɗauki wayarsa ya turawa Anty Jameela tex _"Sakonki yasame ni na yaba kware da makircinki duk abinda kike nufi dani Allah yamayar maki kanki, banga abinda nai makiba amma kin tusoni agaba, kisani Allah yana tare dani insha Allah bazaki taɓa cimma burinki ba akaina mu zuba mu gani"_ tajima tana karanta sakon kafin tayi delate ɗinsa. Washe gari aka raka amarya Baraka legos yan rakiyan basu wani jima ba suka juyo kasancewar a jirgi sukaje ashi ɗin kuma zasu dawo. Fu'ad yasan ankawo amarya amma bai dawo gidanba sai sha ɗayan dare, daman tunda zai futa ya rufe ɗakin dayake amfani dashi yatafi da makullin, ko a falo bai zaunaba ya wuce bedroom ɗinsa wanka kawai yayi ya kwanta bai farkaba sai asuba agurguje yai alwala ya wuce masallaci, bai dawo gidanba sai bakwai na safe nanma a gurguje yai shirin office danshi ko'amafarki baya fatan ganin fuskar yarinyar da'aka kawo masa da sunan amarya, wasa wasa saida Baraka ta shafe sati guda bata saka angon a idanunta ba, itama bata wani damu dashi ba tunda ita ba yarinya bace ko daga yanda ya nuna mata tasan cewa baya ra'ayinta shiyasa ta janye jikinta daga zaman falo ko yaushe tana zaune cikin ɗakinta, bata futowa sai taji futar motarsa daga sannan zata futo tafara sabgoginta tanada matukar tsabta shiyasa ta gyara ko'ina na falon harma da kichin ɗin abubuwan da sukai kura ta wanke su, sosai takejin daɗin zamanta a gidan batada wata damuwa tadafa abinda ranta keso, komai gashinan jibge a gidan sai abinda kai niyyar ci, zaman kaɗaici ne kawai ke damunta Allah yasama tanada waya ita kan ɗebe mata kewa. Gaba ɗaya yinin yau ina cikin damuwa saboda Ankul kwanansa biyu kenan yana famada zazzafan zazzaɓi duk yabi ya rame gashi bayason magani saidai yayita yiwa kansa allura, yanzuma haka yana kwance cikin bargo tun safe nake masa nacin yazo yayi break amma yaki, dana kammala abinda zanyi na koma ɗakin nasa na kwanta kusa dashi cikeda damuwa na zuba masa idanu, jawoni yayi ya kwantar dani ajikinsa, sam yau jikin nasa ba zafi, lamo nayi ajikinsa ina wasa da hannuna a kirjinsa har zuwa sanda naji yakirani da sunana sak waton AMINA abinda yasani saurin ɗagowa ina kallonsa, abinda bantaɓa jiba kenan daga bakinsa,kauda kansa yayi gefe a idanunsa na hango zallar damuwa hakan yasa na soma kokarin tashi daga jikinsa amma sai ya sake haɗani da jikinsa yana magana a hankali kamar bayaso "Amina lalurar nan tawa bata samun sauki bace inaga bazan sami lafiya ba, ke yarinya ce kinada kuruciyarki bazan cigaba da shuga hakkinki ba shiyasa na yanke hukuncin rabuwa dake, duk da tsananin son danake maki amma ba yanda zanyi dole na maidake gida...😰 07039793439 [6/4, 7:48 PM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 19&20 Da sauri na tashi daga jikinsa na kwalla kara tareda fashewa da kuka "Ni nace maka bazan iya jurewa ba, ko ka taɓa ganin cutar dabata da magani ina sonka! kuma zanci gaba da sonka har karshan numfashina zan rayu dakai rayuwa ta mutu ka raba koda ace baka warkeba bazan taɓa iya barinka ba" Ganin yanda nake kuka yasa ya janyoni jikinsa ya rungumeni idanunsa na zubarda hawaye, shuru nayi ina tunani Allah yasani ina son Ankul bazan kuma iya rayuwa babu shiba yayama za'ayi na amince ya sakeni koda bana sonsa ai bazanso zama karamar bazawara ba, ba kowa bane zai fahimci abinda yasa muka rabuba kuma ma inya sakeni nacewa su Mami me? babu mai yarda dani kowa cewa zaiyi ni nazaɓi saki saboda daman ba sonsa nake ba, ganin nayi nisa a tunani har banji bugo kofar da'ake ba yasa ya girgiza ni Yace"Kinga tunanin ya'isa haka naji na fasa zanci gaba da neman magani amma kisani a addinance inna shekara guda bansami lafiya ba dole zamu rabu" Ban tsaya sauraronsa ba danna fara tunanin zafin zazzaɓe ne ya taɓasa yakemin wannan surutan😹banzan, futa nayi jin ana sake bugun kofar da karfi, ina buɗewa ta shugo gabana yai wata irin faɗuwa ganin Zainaba ce da yarta Ameera wacce bazata wuce shekaru sha uku ba, gaba nayi suka biyoni zainaba tanata kallon gidan harma da motocin dake parke a compound na gidan, wajan zama na nuna masu na wuce ciki na sanar da Ankul yayi baki, nadawo na kawo masu ruwa da lemu da cake, da gudu Ameera ta tafi ta makalkale Ankul tana murnar ganin Daddy ɗinta, shima yayi murna sosai da ganinta rungumeta yayi a jikinsa yana tambayarta yaya school, surutu sosai takewa Ankul shima yana biye mata har Zainaba ta tashi tafiya fir Ameera takibin Zainaba tace tazo kenan ba karamin daɗi Ankul yaji ba hakan yasa yace Zainaban taje kawai, amma taki tafiya saima Cewa datai"Intafi inbarta makaranta fa gashi bata tawo da wasu kayan ba,sannan ma ai bancewa Baba anan zan barta ba" "Nidai nace ki tafi Ameera tazo kenan zanci gaba da rukon yata makaranta zan canza mata wata, kayama abarsu kawai zan siya mata wasu" Badan ranta yaso ba ta tafi bayan Fahad yabata ten k yace tahau mota,sai bayan ta futa yakalleni yana murmushi yace "Na ɗora maki nauyi ko" Murmushi nayi ina kallon yanda Ameera ta kwanta ajikinsa nace "Nauyi kuma rukon Meeran shine nauyi ai yata ce ko bakai nake aure ba inada damar riketa bare kuma ina tare dakai" Rausayar da kansa yayi kafin yace "Shikenan to na yarda ga amanarta nan na baki ita kijata ajikinki kiriketa kamar yanda zaki rike yarki koda bayan raina ban yarda ki mayar da'ita ga mahaifiyarta ba, inason kibata tarbiya irin wacce uwa tagari take bawa yaranta kibata tarbiyya islamiyya wacce musulmai da musulumchi zasuyi alfari da'ita, dan Allah karikemin Amana" Kallonsa kawai nake nikan cutar nan ta Ankul tafa fara bani tsoro musamman yau dayake zubamin sambatu tagumi nayi har sannan ina kallonsa shima kallon nawa yake munjima muna kallon juna nace "Ankul anya wannan zazzaɓin bai taɓamin kaiba?" yau gaba ɗaya na kasa gane kanka daga zancan rabuwa kuma an dawo na mutuwa da barin wasiyya" Dariya yayi tareda mikewa"Au yau kuma kallon taɓi taɓi akemin saboda na faɗi gaskiyya tona gode shirya mu futa ayiwa Meeran taki siyayya ki samo school ɗin dakike so tafara sai ayi mata regestresion zuwa monday tafara" ɗaki ya shuge ni kuma na kama hannun Meera muka shuga ɗakina nace mata ga ɗakinta nan ta zauna, ai kuwa tayita murna harda ɗan tsallenta ni kuma na futa, tunawa danayi ban kulle kofa ba bayan futar Zainaba yasa na futa ina saka kafata a kofa na hangi wani bakin abu kamar garin magani da sauri na tsugunna ina bin gun da kallo ganin yanda aka barbazashi a bakin kofar, gefe na hangi wata laya, gabana ne yafaɗi jikina ya ɗauki rawa Ayatul kursiyyu nayi sannan nasa kafata na taka maganin bakina ɗaukeda addu'o'i na ɗauki layar na damke a hannuna na share wajan na zuba magani a kwatar waje nadawo ciki tuni Ankul yayi wanka harya futo ni daman banjima dayin wanka ba hakan yasa na shafa hoda kawai na zura doguwar riga yar baharein nai rolling mayafinta saman kaina sannan nafuto, key ɗin motar Ankul na karɓa nace bazaiyi tuki ba tinda bayajin daɗin jikinsa, ni najamu har zuwa babban shagon Ankul ɗin dake zoo road sosai na jidarwa Meera kaya har saida Ankul yai magana yana dariya Yace "Yau na banu besty karki nakasamin store mana" Dariya nayi nace"Inma mun nakasa saika kara wasu mudai in za'ayi order nan gaba asa damu" murmushi yayi ya jingina da bango yana kallona, bayan munfuto aka loda kayan a boot na motan muka wuce gidanmu can tarauni acan Ankul yabarni nida Meera Yace zai laika asibiti da yamma zai biyo mu koma gida, munjima da Mami muna hira Ummi bata nan tana gidansu can Aisami Mami ke tambayata "Niko Su'ad cikinki watansa nawa?" Murmushi nayi tareda yin kasa da kaina ina wasa da hannuna nace "Mami nifa banida komai" Shuru tayi tana kallona har sannan ina wasada hannuna kasan zuciyata ina tunanin kodai futowa zanyi nagaya mata gaskiyya danni Allah yasani yau ɗinnan nasawa kaina zargin Zainaba akan rashin lafiyar Ankul musamman kan abinda nagani hakan yasa na katse shurun ɗakin da cewa "Mami Ankul bayada lafiya fa, kuma kinga ɗazu na gani a compound" namiƙa mata layar dana gani ɗazu,hannunta na rawa ta karɓi layar tana bissimillah" tajima tana juya layar kafin Tace "Kina nufin Fahad bayada lafiya matsayinsa na namiji yaushe haka tafaru" nan nagaya mata tunda akai auranmu ne "Waye yazo gidanku yau?" "Zainaba ce kawai shiyasa nafara tunanin rashin lafiyarsa kamar dasa hannunta aciki ko kwanaki da mukaje Misra akan lalurar ne har islamic chemist yaje amma ba canji shiyasa na yanke kawai na faɗa maki" Shuru tayi tareda tagumi tana kallona tama kasa cewa komai, jikinta yayi sanyi har mukazo tafiya sanda Ankul yazo bayan sallar mangariba, batayi masa zancanba muka koma gida. Ranar monday Ameera tafara zuwa school tun bakwai da rabi Ankul yake kaita bata dawowa sai shida na yamma nake zuwa ɗakkota, gefe nima naci gaba da karatuna. Mami bayan tafiyarsu Su'ad ganyan magarya tasamu guda bakwai ta dakasa ta zuba a ruwa ta karanta suratul bakara daga aya ta farko zuwa ta biyar, sai ayatul kursiyyu da wattaba'u da amanar rasulu da kuliya aiyuhalkafirun kulhuwallahu falaki da nasi...ayoyi da dama tayi amfani dasu ta tofa, ta ajje ruwan washe gari da dare da kanta taje har gida ta kaiwa Su'ad tace ta tabbatar Uncle yayi wanka dashi a tsabtataccan waje lokacin Uncle yana nan kallonsu kawai yake baice komaiba, sai bayan tafiyar Mami Yace "Waton duk rokonki danai karki faɗawa kowa lalurata saida kika faɗawa maminki ko?"yayi kyau nasan zaman da zanyi dake" Uncle yafaɗi haka cikin fushi Dariyama yaban hakan yasa nayi dariya kafin nace "Ba dole na faɗa mata ba kafara batun rabuwa yaya kake so nayi da rayuwata in bana tare dakai koba haka bama Meera tana bukatar kani kaga dole mu nemi mafita" Rike baki Uncle yayi cikeda mamakin maganarta yace "A'a kidaice Antyn Meera tana bukatar mijinta, mai wannan yake nufi" yafaɗi haka yana buɗe jarkar da Mami ta kawo ruwan, taɓe baki yayi kana "Ya ce yanzufa sai tace sammu akaimin shine taje ta haɗo wannan" dariya nayi tareda ɗaukar jarkar nace "Nidai taho nayi maka wankan nan a alamu muka gani wanda ya tabbatar mana da zarginmu" baice komai ba yabiyoni ɗin, cikin ikon Allah kwana uku yana wanka yadawo normal ranar yini yayi yana murna sai faman kirana yake daga office naga shirya shi wallahi yau ya warke dayasan hakane aida tuni yagayawa mami da kansa amma kyautata dabance bari yadawo, bai shugo gida ba sai Takwas na dare yasame mu zaune a falo Meera tana kwance kaina sai faman juyi take tunda ta dawo daga school takemin korafin cikinta yana ciwo faɗa nai mata akan rashin cin abinci nabata abincin taci danna zaci yunwa takeji amma maimakon ciwon yayi baya saima gaba yake, ko zama baiyi ba ya koma ya haɗo mata magani harda allura yai mata muna nan zaune a falo har ɗayan dare tana fama, sai wajan biyu saura tacemin yadaina zataje ta kwanta, wayata na bata na kaita ɗakina nace ta kwanta intaji ciwon takira lambar Ankul sai nazo, na wuce ɗakin nasa harya kashe light ya kwanta na kwanta kusa dashi yajani jikinsa yana faɗin zoki kwanta sarkin tsoro ba abinda zan maki nima na gaji yarki ta rusa mana wannan daran namu, har barci yafara fuzgata naji karar faɗuwar abu a falo hakan yasa muka mike tare nida Uncle da sauri nai hanyar futa falon Uncle yaruko hannuna yanamin wani kallo wanda bantaɓa ganin irinsa daga garesa ba, ya mike ya haɗani daa jikinsa yana sauke numfashi "Ina sonki Besty" yafaɗa da murya a shaƙe, karajin motsi danai yasa na fusge hannuna tareda faɗin "Uncle sakeni kilafa Meera ce jikin ya motsa ta futo kar zafin ciwo yasa ta futa waje a daran nan" sake haɗani yayi da jikinsa yana sakin ajjiyar zuciya kallon idanunsa nayi yanda suka canza launi yasa nai murmushi Na ce "To tawo muje mu dubata saimu dawo tare" tare muka futa dai dai an kunna hasken falon abinda na gani yasani kwala ihu haɗeda salati na kankame Uncle jikina yana rawa manyan kartini majiya karfi kallo ɗaya zakayi masu ka gane su waye, Uncle sakina yayi yana tunkararsu bako alamar tsoro a garesa "Lafiya zaku shugo mana gida da daran nan" wata dariya wani acikinsu ya bushe da'ita yana girgiza yabawa Uncle amsa da "Wajanka aka turomu mu ɗauki ranka" Murmushi mai ciwo Uncle yayi ya ce "Raina kuma kamar kaine mala'ikan mutuwa" da sauri na kankame Uncle ina kuka nake faɗin "Dan Allah karku kashe sa zamu baku duk abinda kuke bukata amma karku taɓamin mijina" zama wanda na lura shine ogan nasu yayi kan kujera yana kureni da kallo yace "Gaki kuwa kyakkyawa zaki iya fansar mijinki da wannan kyan naki ki bani minti goma kacal mu shuga daga cikin na kawar da kishina shi kenan na barki da mijinki" Uncle wani irin ihu yayi tareda kallon wanda yai maganar ya janyeni daga jikinsa ya doshi wanda ke maganar yana tattare hannun jallabiyar dake jikinsa a yafara kokarin kai masa naushi, ɗaya daga cikinsu ganin ya doshi ogonsu yasa ya shammacesa ta gefansa ya caka masa wuka a gefan cikinsa "Ya Allah" Uncle yafaɗa tareda dafe wajan daya yankesa da gudu nai kan Ankul ina kwala masa kira ganin yanda jini yafara zuba, kafin nakai ga Ankul ya zube a kasa saboda jinin dake zuba daga jikinsa, ɗora kaina nayi saman cikin Uncle nasoma kuka yanda yake futarda numfashi yasa nakai hannuna zan cire masa wukar da har sannan take jikinsa aka banko kofar shugowa ana faɗin karki taɓa Su'ad da sauri na ɗago ina kallon mai magana...✍️ 07039793439 [6/8, 11:44 AM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 21&22 Da sauri na ɗago kaina na kalli wanda yashugo Cp Mukhtar ne bayansa ummi da mami ne sai Yaya Jabeer da tawagar yan sanda kamar masu shirin yaki, da sauri Jabeer ya'isa inda Uncle ke kwance ya tallafo kansa, Cp ya saka wani kyalle ya zare wukar jikin Uncle sannan C P yabada umarnin a tafi dashi asibiti bisa jagorancin yaransa, ina kallo su Yaya Jabeer suka tafida Uncle hospital Mami kuwa ta zauna dafa'an tana kuka ganin halin da ɗan uwanta ke ciki da wuyama ya tashi😰 Kwamishina ya tusa keyar yan fashin dasuka shugo mana gida, amaimakon nagansu su biyar kamar yanda suka shugo saina lura babu ogansu wanda yazauna kan kujera, C p yace mu rofe gidan su ajjemu a asibiti sai sannan nayi magana Nace "Yaya Mukhtar akwai fa sauran ɗaya su biyar suka shugo,nan da nan yabaza yaransa suka cigaba da bincike gidan sai sannan na tuna da Ameera na shuga ɗakinta amma naga wayam bako alamarta hannu na ɗora aka🙆‍♀️ na fashe da kuka ina faɗin "Wayyo Allah na shiga uku banga Ameera ba," nafaɗa ina rushewa da matsanancin kuka, duk yanda aka bincika gidan ba Ameera ba ogan yan fashin, C p yabar sauran yaransa suna tsoron gidan yayinda mu kuma muka wuce Hospital inda aka kai Uncle muna shuga dai dai an futo dashi daga ɗakin tiyata dan yankan yataɓa masa hanjinsa, bin gadon da'aka turoshi nayi da kallo ganin yanda fuskarshi tai haske yasa na fashe da kuka tareda rungume Mami, Ummi tace "Ba kuka zakuyi ba mugodewa Allah dayasa aka kawosa asibiti da wuri da tuni mun rasashi amma yanzu da izinin ubangiji zai tashi nan da yan awanni" shuɗewar awanni Uncle bai farkaba nayi kuka na harna gaji Mami ta koma gidanmu, gefe guda kuma yan sanda na gudanar da bincike kan wanda yaturosu da kuma ɓacewar Ameera. Wajan sha biyun ranar juma'a Uncle ya farka yana wata irin karkarwa da sauri na futa na kira Ummi kasancewar asibitun datake aiki ne,tare suka shugo da wani likitan, Uncle ya ruko hannuna cikin ciwo yake faɗin "Su'ad kiyafemin mutuwa zanyi ina Ameera ina Mami, Ummi ga amanar Ameera nan na damka a hannunku kuriketa kar'a bawa dangin mamanta nabar maku ita duniya da lahira,Su'ad kiyi hakuri yau mutuwa zata rabamu fatana ko bayan raina karki manta dani kirinkami addu'a,Allah yabaki wani mijin wanda zai soki fiyeda son danake maki,naso ace nayi tsawon rai ta yanda zankula dake nabaki farin cikin rayuwa amma mutuwa zata rabamu kigayawa Mami tayi hakuri daman mu kaɗai muka rage yau gani nima zan tafi na barta😰" Wata shakuwa da yayi can kuma sai aman jini, gaba ɗaya likitocin sukai kansa kowa da abinda yake masa har sannan hannunsa yana cikin nawa ni kuma na kifa kaina kan gadon dayake kai inata kuka duk da maganganunsa basuyi tasiri a zuciyata ba danni gani nake kawai zafin ciwo yasa yake waɗan nan surutun, salatin dayayi haɗe da kalmar shahada yasa na ɗago ina kallonsa idanunsa na kallon sama naji hannunsa dake cikin nawa yasaki, Ummi naga taja baya tana salati ɗayan likitan yaja farin kyallan dake lulluɓe jikin Uncle ya rufe masa fuska, ban fuskanci mai suke nufi ba saida naji ɗayan likitan ya kalli Ummi Yace "Sai hakuri Dr kullu nafsin za'ikatul mot" Ai bansan sanda na mike ba na rungumo Ankul da karfi nace "No!!! wallahi karyane! nace karyane ba Ankul ɗina bane yamutu kaine dai bakasan aikinka ba, na buɗe Ankul ina kallon fuskarsa "Kanaji ana maka sharrin ka rasu Fahad katashi ka shaida masu baka mutuba katashi nace Uncle Dan Allah besty ka tashi ka gaya masu kana raye" rukoni da'akayi yasa najuya ina kallon wanda ya rikeni Yaya Jabeer ne idanunsa sun kaɗa sunyi jawur ba kuka yake ba amma tabbas halin dayake ciki kwara ace kukan yake zuciyarsa zatafi samun sauki😰rungumesa nayi tareda fashewa da kuka Nace "Dagaske wai da gaskene Uncle ɗina ya rasu, Yaya Jabeer ka karyata dan Allah ka karyata min Innalillahi wa'inna ilaiheer raji'un" Ummi ta ruko hannuna muka futa zuwa gida, su Yaya Jabeer suka tsaya zasu tawo da gawar Ankul. Har muka shuga mota ina kallon ɗakinda gawar Uncle ke kwance inajin wani irin kewarsa datake shugata, shikenan kuma na rabu da Uncle bazan sake ganinsa ba? na rasa Ankul kamar yanda na rasa Daddy na gaba ɗayama kukan yaɗauke na koma kamar wata mutum mutumi har sanda aka gama haɗa gawar Uncle aka kirani wai muyi sallama sosai nasawa zuciyata juriya nai masa addu'a da fatan Allah yasa aljannace makomarsa. Kwanaki uku mukayi muna zaman makokin Uncle, har sannan ba labarin Ameera,abinda ya kuma ɗagan hankali kenan nakan shuga damuwa musamman idan natuna amanar da Ankul yabani hankalina yakan tashi, sosai yaya mukhatar yake tsaye kan case ɗin, kwanan Uncle goma da safe ina zaune a main falo aka kwankwaso kofa naje na buɗe yan sanda ne guda biyu mace da namiji iso nayi masu zuwa ciki na kira Ummi da Mami ɗan sandan ke magana "Munzo daga stesion ne munason zamu tafida Amina matar Fahad zata amsa mana tambayoyi saboda zarginta da'ake dasa hannunta a kisan Fahad ɗin" Zumbur Mami tamike tareda dafe kirji tana salati tace "Daman ance ku yansanda kun fiye sharri yau kuma sharrin naku kan ɗiyata ya sauka ni na raini abata nasan halinta bazata taɓa goyan bayan zalinci bama bare takai ga kisan kai, kutashi ku futar mana daga gida tunban farfasa maku kafafuwa ba" Ummi ta dafa kafaɗar Mami tace "Kibari su tafi da'ita tambaya kawai zata amsa masu ta dawo", hannuna Ummi ta kamo tace "Gatanan kuje ni nasan ba hannun ta acikin kisan nan" Mami ciki ta shuge ta ɗakko wayarta ta kira kwamishina ko gaisuwar dayake mata bata amsaba tace "Tayaya zaka turo yaranka suzo su tafi da yata" "Kiyi hakuri Mami bincike ne yabiyo ta kanta, yaran da muka kama sunce matarsa ce ta aikosu su kashe sa saboda bashi take soba aka aura mata shi, bincikenmu yatabbatar da Su'ad batason Fahad dole akai mata Mami ajje wayarta tayi ta saka hijab tacewa yan sandan "Naji kuje zankawota da kaina amma bazata shuga motarku ba" ba yanda suka iya haka suka tafi nidai har sannan ina tsaye ina binsu da kallo zuciyata wani irin zafi takemin wanne irin sharri ne wannan maye alakata da yan fashin nan wanne laifi namasu da zasumin wannan babban kazafin, hannuna Mami taja tana Faɗin "Karki damu Su'ad wallahi nasan sharri ne tayaya zakisa a kashe Fahad tabbas akwai wata a kasa kodai akwai wanda suka sami matsala da Fahad yaturo aka kashe sa yakeson ya ɗora maki laifin ba komai kiyi addu'a insha Allah komai zaizo da sauki". Bayan munje duk yanda Mami taso subata ni mutawo tare ki sukayi saima sakayani dasukai, ina kallon Mami tabar stesion ɗin ranta aɓace, duk yanda muke zaton case ɗin yawuce haka dan gaba ɗaya laifin kisan ni aka ɗorawa tuni yan sanda sun turamu kotu, yan uwana sai shuge da fuce suke ganin anbada belina amma sam D P O yaki, ranar Monday muka fara halartar kotu, nanma ba nasara saima tarin tambayoyi dasuka rinkamin danma lauyana yana bani kariya sosai saboda kwararran lauya Mami ta ɗaukarmin, Alkali ya ɗaga shari'a nan da sati biyu ya kuma umarci yan sanda da lalle su nemu damo wanda ake zargin shiyasan wacce ta turosu dan yazo yafaɗi gaskiyya. ___________******____________ Fu'ad yadafe kansa dayaji yana sara masa saboda damuwa gaba ɗaya yana cikin damuwa, shirye shiryan tafiyar sa England dayake yasa bayama da nutsuwa, sam baida labarin rasuwar Fahad duk da yakan tunasa lokaci zuwa lokaci, yakanyi mamakin wai duk yanda suke da Fahad amma saisu share fin wata guda ba wanda ya kira kowa gaba suke ba kawai kowa yanjin nauyine duba da abinda yafaru, badan ransa yasoba Abiee yatakura masa lalle saiya tafi da Baraka yarinyar da yau watanta guda kenan amma bai taɓa sakata a idonsaba, yau da wuri ya shugo gidan saboda yanason yakaita amata shirye shiryan tafiya, wani cost zaije wanda zai shafe watanni takwas a london, wanka yayi yaci abincin daya shugo dashi sannan ya koma falo ya kwankwasa kofanta ya koma saman kujera ya zauna. Baraka dake zaune gefan gado tayi tagumi, zumbur ta mike jin bakon lamari yau wacce bakuwa suka samu a gidan har take bugo mata kofa, plate shoe ɗinta ta zura tareda yafa ɗan kwalin doguwar rigar dake jikinta ta futo, ba karamin faɗuwa gabanta yayi ba ganin Fu'ad a hakimce saman kujera da wannan ranar, kallo ɗaya yai mata ya ɗauke kai yana taɓe baki, shi baiga amfanin wannan auran da'akai masa ba, waya gaya masu yana son farar mace shi sam arayuwa baya bukatar mace fara, kuma taɓe baki yayi ganin yanda ta zauna kasan carfet saida yamike sannan Yace "Ki shirya akwai wanda zai kaiki kiyi pascort" ɗakinsa ya shuge ya kira direbansu na office yace yazo zai aikesa, yana zuwa ya haɗata suje ayi mata abinda yakamata, ba karamin haushi Baraka tajiba, ta kudurci aniyar saita cusawa Fu'ad soyayyarta kota halin kaka bata taɓa ganinsa ba sai yau akallo ɗaya kuma datai masa ta kamu da mugun sonsa ayan kwanakin dasuka rage masu ta fara futowa ta sabarwa kanta zaman falo wani bin tana nan yake shugowa tai masa sannu da zuwa amma ko kallon inda take bazaiyi ba zai shuge ɗakinsa, sosai take shuge masa har ɗakinsa takan shuga in yana ciki musamman da safe ta gaidashi, yau tana shuga tasame sa kwance ya kifa cikinsa yana sauke numfashi ya haɗa ubangumi duk da fankar dake yi a ɗakin, karfin fankar ta kara tareda kunna A c cikeda karfin hali ta hau saman gadon tana masa sannu, janyota kawai yayi jikinsa atake yafara aika mata da sakonni, bata wani tsaya jan aji ba tabada kai bori yahau😹 dan itakam daman ta jima tana son zuwan wannan ranar duba da shekarunta ayanzu zasu kai ashirin da tara zuwa talatin amma ta kame kanta zata iya rantsuwa da Allah babu wani namijin daya taɓa koda rike mata hannu, ba karamar azaba tasha ba a hannun Fu'ad dan da zafi zafi yake gabatar da komai bako alamar tausayawa, saima daya sami nutsuwa ne yaɗan tausaya mata ganin yanda lokaci ɗaya jikinta yai sanyi sosai bathroom ya shuga ya tsabtace jikinsa sannan ya haɗa mata ruwa zafi yace taje ta gyara jikinta kafin ta futoma har yayi barci, murmushi tayi ganin yanda yake sauke nimfashi ahankali ta sumbaci laɓɓansa ta fuce daga ɗakin tana murmushi, tun daga wannan ranar Baraka ta koma ɗakin Fu'ad da kwana bai hanata ba saima farin ciki dayai da hakan,ahankali suka saba saidai har sannan baya sakar mata fuska zata iya rantsewa bata taɓa ganin dariyarsa ba, dama shi can bayada fara'a tun bayan rabuwarsa da Su'ad sai abin yai gaba ga kuma damuwar wannan aure da'aka kakaba masa, ranar alhamis jirginsu ya ɗaga zuwa birnin londan, ko cikin jirgi tana lafe ajikinsa tayi barci ta tashi har jirginsu ya sauka, Usman abokinsa yazo tararsa saida yakaisa har gidan dazai zauna kana ya koma gidansa yakawo masu abinci shida tasa matar. __________Ranar da muka koma kotu ta cika fiyeda zama na farko yan sanda kuma sunzo da damo wanda ya gudu a daran, sosai yakafe kan lalle nina sakasu kashe Ankul abinda yaja hankalin mutane sosai, Alkali na shirin yanke hukunci lauyana da baisami zuwa ba sai sannan ya turo kofar kotun yashugo yana neman afuwar alkali. Yace "Ya mai girma mai shari'a inason na gabatar da shaidata wacce zata tabbatar da ba Amina Usman Karaye bace tai wannan kisan kan" Alkali yace "Kotu tabaka dama" Ganin Amira danayi yan sanda sun shugo da'ita ta tsaya tana kuka kamar bazata ce komai ba, gaba ɗaya bata cikin nutsuwarta har saida alkali yai mata magana ta nutsu tayi magana sannan tafara magana "Sunana Mariya Fahad Aliyu, ranar alhamis tara gawata da misalin karfe biyu na dare ina kwance a ɗakina naji tsayuwar mota a bayan gidanmu labulan ɗakina na ɗaga na lega windo dai dai sannan wannan ta nuna ɗaya daga cikin yan fashin ya hauro gidan namu yabuɗewa sauran gate suka shugo, yanda naga bindugu da wukake a hannunsu saiya tsorata ni hakan yasa nai amfani da wayar Anty na dake hannuna na kira Mami yayar mahaifina ina kuka na sanar mata yan gashi sun hauro gidanmu, Mami saboda tsabar kiɗimewa bata kashe wayar ba ta futa tana sanarwa da Ummi halin da'ake ciki, Ummi ita ta kira C p Mukhter tagaya masa, anan na kashe wayar ganin Mami bata kashe ba, sanda yan fashin suka shugo gidan ɓuya nayi can gaban gado ina jiyo abinda ke faruwa a falo amma tsoro ya hanani fitowa, sanda yan sanda suka shugo gidan wannan ta nunana damo ya shugo ɗakina ganin zanyi ihu ya toshe min baki, ya yage net ɗin dake jikin windon ɗakina wanda ya futo ta waje ya jefani sannan shima ya diro ya jani muka faɗa wani babban rami dake bayan gidanmu, wani yakira a waya bayan yaga wucewar motar yan sandan yazo ya ɗaukemu suka kaini wani gida suka kulleni a ɗaki sau ɗaya wani bawan Allah yake kawomin abinci da rana mai gadin gidanne yace yanajin tausayi na zai taimakamin na futa. Ranar danayi sati a gidan mamata taje ta gayamin ita ta tura su damo su kashe Abbana dan tagaje dukiyarsa dan Allah na rufa mata asiri nace bazan iya rufe wannan asirin ba anan ta umarci damo da lalle in dare yayi nima ya aikani inda babana yatafi...🙆‍ Comment and share Eid Mubaraka my lovely fans🥰😍❤️🌹 [6/9, 7:02 AM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 23&24 Ranar nayi kuka sosai sai dare wanda ke gadin gidan yazomin a tsorace yace na biyosa, tare muka gudo daga zariya da mukazo kano ya dankani a hannun yan sanda anan CP yaganni ya ɗaukeni zuwa gida na gaya masa komai yanda yafaru sai yau nazo nan domin na shaidawa duniya cewa ba Anty bace ta kashe Daddyna ba Ummana ce" tana zuwa dai dai nan ta fashe da kuka tareda zubewa a kasa Ummi ta ɗauketa suka tafi da'ita asibiti nan take Alkali yawanke ni sannan ya yankewa Zainaba da su Damo hukuncin kisa ta hanyar rataya mahaifiyar Zainaba dake cikin kotun itada Zainaba ganin yanda yan sanda suka kama Zainaban yasa ta yanke jiki ta faɗi nan take rai yayi halinsa. Mami kuka take sosai jikinta sai karkarwa yake yaya Jabeer ya riketa zuwa motarsa muka shuga zuwa gida, sosai masoyana suke ta zuwa tayani murna,wasa_wasa saiga Mami ta kwanta ciwo kamar bazata tashi ba kwananta biyar a asibiti sannan taji sauki aka sallamota. Rayuwa nake wata irin rayuwa mara jin daɗi kullum cikin kuka muke nida Ameera musamman in mukaga hoton Ankul dole tasa Mami ta ɗeɓe duk hotunansa dake cikin gidan, karatuna naci gaba namaida hankali sosai wajan zuwa makaranta cikin shekaru biyu na kammala natafi low school. __________Ahankali yafuto daga cikin tsadaddiyar motarsa fuskarsa ba ɗigo annuri, yajima tsaye nan jikin motar yana kallon cikin gidansa, kafin ya saka hannu yaɗau jakar Laptop ɗinsa ya saɓa a kafaɗarsa yafara takawa a cikin compound ɗin, har zuwa tsakiyar falo, da gudu wata kyakkyawar yarinya da bazata wuce shekaru biyu ba ta futo daga ɗaki ta ɗanesa cikin muryarsu irinta yara tace "Papi welcome back" lumshe idanu yayi tareda sumbatar kumatun yarinyar Yace "My Princess yaya gida" futowa tayi daga ɗakinta tayi kwalliya sosai cikin kananun kaya riga da wando wanda suka matukar amsar jikinta, kokarin shugewa jikinsa take yaɗaga mata hannu, ya ɗauki yarsa suka wuce ɗakinsa, dage kai Baraka tayi tanabin mijin nata da kallo tarasa gane kan wannan bahagon mijin nata shekaru uku kenan da auransu amma babu wata shakuwa a tsakaninsu bata taɓa ganin dariyarsa ba sai ranar data haifa masa Baby taga yana murmushi sanda yagaya mata yasawa yarinyar Aminatu Su'ad kowa da Su'ad yake kiran yarinyar amma shi yabi ya kakaba mata Princess tarasa wanne irin so Fu'ad yakewa Princess indai yana gida to yana tare da'ita harta kwana tare suke da'ita ko ita sai yayi sati bai haɗa makwanci da'ita ba indai ba bukatarsa ce takawosa ba, Wanka yayi yafuto yana goge ruwan jikinsa da karamin tuwel Princess ya kalla wacce ke zaune saman gado tana game a wayarsa murmushi yayi yanajin kaunar yarinyar tana kara shugarsa, lumshe idanu yayi yana tuna farkon haɗuwarsa da Su'ad irin soyayyar dasukayi har zuwa kallon karshe dayayi mata ranar ɗaurin auranta da Fahad, da sauri ya zauna gefan gado yadafe kansa yana sake tuna rayuwarsa tunta yarinta shida Fahad yatuna yau shekaru uku kenan ba wanda ya nemi a wani acikinsu, da sauri ya ɗakko tsohon sim ɗinsa na nageria ya saka cikin wayansa yai copy ɗin lambar best freind kamar yanda yai save ɗin numbar, yakira yafi sau goma amma maganar ɗayace lambar bama ta aiki, sake dafa kansa yayi ya kira Abokinsa Usman bayan sun gaisa yace "Usee asamarmin jirgi inda dama zuwa gobe nakeson sauka a nageria" Dariya Usee yayi yace "Turaki ikon Allah yau kuma nageria tai kira kenan kaida madam ko kai ɗaya?" "Nida Princess banda Mamanta" "Angama mai girma turaki" Ko Baraka bai gayawa tafiyar ba sai sanda zasu tafi airport yace "Zamu tafi gida da Princess ba daɗewa zamuyi ba bana tunanin zamu wuce one week" Rau rau tayi da idanu kamar zatayi kuka tace "Ni wanne laifi nayi dabaza'a tafi dani ba, shekara uku fa rabonda naga mamata" Batare daya kalleta ba yace "Ni tawa mamarma mutuwa tayi samada shekaru rabona da'ita yaya nayi saike da kullum sai kinji muryanta kuna vidio call kina ganinta" Tana kallo jirginsu yatashi tana hawaye ta tare texzii tahau zuwa gida zuciyarta kamar zata fashe saboda bakin cikin Fu'ad ita kam sam bazata taɓa ɗorar da farin cikin aure ba babu wata soyayya a rayuwar auran nasu share hawayanta tayi tana faɗin "Anty Jamila duk ke kika jamin dan haka nima bazan taɓa baki haɗin kai wajan cikar burinki" __________Jin ana kwankwaso kofa yasa na mike da sauri na buɗe dan daman zaman jiransa nake, tsayawa yayi a bakin kofar ya harɗe hannuwansa a kirji ganin an buɗe kofar yasa ya shugo da sallama saida ya zauna na kawo masa lemu da ruwa, bai sha ba saima wani kallo dana lura yana bina dashi, ganin na kamasa yana kallona yasa ya ɗauki wayarsa ya waske yana dannawa. Binsa nayi da kallo dan ganinsa saiya tunamin da Ankul ɗina ba kaɗan ba suke yanayi da Uncle ɗin dande wannan yafi Uncle tsayi, sanye yake cikin kananun kaya blue jeans da black shart katse shurun namu nayi ta hanyar faɗin "Nura ko" Kallona yayi yana wani taɓe baki kana yace "No Am Nurein" "Ok Mamin bata nan taje nan zoo road amma ina zaton tana hanya ni sakon data bani tace nura zan bawa kai kuma kace Nurein so inaga ba naka bane" ɗagowa yayi yana kallona karaf idanunmu suka sarke cikin na juna kallon ido da ido mukai wanda hakan ya haifar min da wani bakon yanayi Kyauda idanuna nayi daga cikin nasa ina danna wayata Mami nakira na shaida mata tayi bako "Su'ad bako kuma ba Nura bane" "E Mami wannan ya ce sunansa Nurein dariya Mami tayi kana ta ce yajirani gani nan a hanya" Ajje wayata nayi saman kujera na kunna Aljazira ina kallon labarai, shuru nayi ina kallon labaran Kallona yake yana ɗan murmushi ganin yanda nabada hankalina kacokan wajan kallon "Malama kinzo kin kunnawa mutane kallon saiki fassaramin abinda suke cewa danni dai ba fahimta nake ba" Taɓe baki nayi ina cigaba da kallona bance komaiba "Toki canza mana tasha inbazaki fassaramin ba" Dafe kaina nayi nace "Nifa na gaya maka ban san mai suke cewa ba" "Ai yanda kika zurawa tibi kyakyawar fuskar nan taki kawai yatabbatar min da kinsan mai suke faɗa" bai jira cewata ba ya ɗauki remote ya canza tasha, zanyi magana kenan Mami da Ameera suka shugo da ɗan tsallanta Ameera ta karaso wajena ta mikomin ice cream tace "Anty na ga tsaraba na maki" "Kai nakuwa gode my Deauther kamar kinsan anjima nakeson zuwa havila nasha ice cream" Idanun Nurein akaina yake gaida Mami cikin girmamawa yace "Ma'ma tace nazo na karɓar mata sako wajanki" "E munyi waya da'ita tace zakazo shiyasa da zan futa nabawa Su'ad ta ajjiye maka" ina kallon ya lumshe idanunsa yabuɗe su akaina, Mami tabasa sakonsa tai hanyar shuga ɗakinta "Mami wannan Nuran fa bai sha ko ruwa ba balle lemun dana ajje masa" Juyowa tayi tana kallonsa "Nura nanfa gida ne amma ko ruwa baka sha ba" shafa kansa yayi yana murmushi ya ce "Mami nagode na koshi ne banjima da shan ruwa ba a mota na" "Ummm to inma dai ta fulani kayi kai ka juyo" murmushi yayi yamike ya ɗauki ledan kayan da Mami tabasa ya tako zuwa kujerar danake kai yasa hannu ya ɗauki wayata yajima yana dannawa kana ya ce "Maine pin ɗin faɗamin" yafaɗa da murya kasa kasa "Nima ban sani ba" nafaɗa ina maida hankalina kan kallon danake, Amira yakira da hannusa suka futa tare da wayata a hannunsa, jimawa kaɗan Ameeran ta kawomin wayata tana dariya "Anty waifa tambayata yayi kinada saurayi,ni kuwa nace masa mijinki ya rasu" ta karasa faɗa jikinta a sanyaye "Sai yace maki mai kuma" dariya yayi wai damancan da shi kika dace nama basa number ɗinki" wayana kawai na ɗauka na shuge ɗakina. __________Hannu yabawa Chiroma suka cabke tareda rungume juna, Chiroma ya ɗauki Amina yana shafa kanta ya ce "Baby Su'ad ce yau a kasarmu kinzo kiga takwararki" harara Fu'ad ya zabgawa Chiroma tareda yin gaba ya shuge ɗaya daga cikin tawagar motocin da Mai martaba ya turo su ɗauki Fu'ad ɗin, ko cikin mota hira suke sosai shida Chiroma har suka karasa gida, a compound yasami Umma cike take da ɗokin ganin One boy ɗinta musamman daya sanar mata tare yake da Baby Su'ad, rungumesa tayi tana dariya ta shafa kansa tareda jan kumatunsa kamar wani karamin yaro ta ce "Ah lalle nayi farin ciki da ganinka gaduk kanin alamu maman baby tana kulawa dakai sosai irin wannan kumatu haka" dariya yayi tareda bin bayanta zuwa ciki tana ɗauke da Baby Su'ad, kai tsaye sashinsa ya wuce yai wanka yaɗan huta har zuwa dare sanda Umma takirasa yazo suci abinci da mai martaba. "Masha Allah my Son ka girma amma wannan baturiyar tazo kenan bazata koma ba" mai martaba yafaɗi haka yana nuna Baby Su'ad dake kwance saman cinyarsa tana wasa da rawaninsa Fu'ad zama yayi kasan carfet yana murmushi yake gaida mai martaba dake amsawa fuskarsa sake, tare suka ci abincin suka gama sannan suka gangara hira anan Mai martaba ke cewa Fu'ad "Al'ameen banason zamanka acan wata kasa nafison zamanka nan kusa dani kullum shekaruna daɗa ja suke girma yana daɗa kamani, ko yaushe mutuwa zata iya ɗaukata in baka kusa akwai matsala, kasani akwai masu harin kujerar nan ni kuma nafi aminta dakai, shiyasa nayi magana da Ummanka akwai babban fili dana sai maka tun kwanaki kadawo ka gina asibiti ka zauna kusa dani hankalina zaifi kwanciya" Fu'ad shafa sumar kansa yayi wacce ke kwance luf tasha gyara ya ce "Allah yaja da ranka ina godiya amma ni nafison zaman wata kasa can hankalina yafi kwanciya idan ina nan yakan tunamin da abubuwa da yawa waɗanda sun kasa goguwa a zuciyata" yafaɗi haka da raunanniyar murya. Umma murmushi tayi cikeda tausayi dan tun sanda taji sunan yarinyar Ameen ta tabbatar da har sannan da sauran soyayyar Su'ad a zuciyar Fu'ad "AMEEN Kayi hakuri kamanta komai kadawo kasarka da zama hakan zaifi maka" "Insha Allah zan dawo Umma" yafaɗi haka yana mikewa dan zuwa cikin gida yagaida sauran matan mai martaba. Girgiza kai Umma tayi tareda faɗin "Narasa wanne irin so Ameen kewa yarinyar nan ba yakasa mantawa da ita kullum addu'a nake masa amma kamar tiri kalli yanda ya koma da Fu'ad mutum ne mai faran faran ko yaushe fuska a sake amma ni rabon danaga dariyarsa harna manta" Murmushi kawai Mai martaba yayi ya mike zuwa sashinsa, duk yanda Fu'ad yaso ya zo kano wajan Fahad abin ya gagara ko yaushe suna tare da mai martaba in anka gayyaci mai martaba zuwa wani taro saiya turasa shida Chiroma gaba ɗaya ya gaji shifa saboda haka bayason zaman bare yafi kaunarsa zaman nesa fiyeda gida. Babban wajene mai kunshe da sashi sashi daban daban wanda ya danganci mata kama da wajan gyaran jiki shagon ɗinki daya tara manyan teloli da sukasan ɗinki yasansu, kayan costumeties, komai da mace ke bukata zaka same sa awajan gefe kuma ga babba wajan cin abinci da babban event, wajan na mami ne bata jima da buɗesa ba nike kula da ɓangaran gyaran jiki na mata wanda aka zuba ma'aikata sosai waɗanda sukasan aikinsu, sosai wajan ya karɓu a wajan mata musamman na yankin mu dama kewaye, sauri nake zan koma gida saboda yamma tayi lokacin tashina yayi, banzo da mota ta ba driver ne yakawoni dan haka na futo bakin titi ina jeran nape, wata mota harta giftani tayo baya ahankali glass ɗin motar yake sauka mamallakin motar ya leko kansa yana murmush ya ce "Hajiya Su'ad yammata kwana dayawa ko nemana bakya yi" Ni dariyama yabani ko akanme zan nemesa daga gani ɗaya danai masa to in nemesa ince masa me, buɗemin kofa yayi yana faɗin "Zomu tafi gidan dama na nufa Ma'ma ta aikeni wajan Maminki" haka kawai naji bazan iya yimasa musu ba na shuga, tare muka shuga gida da Nurein hakan na lura ba karamin daɗi yayiwa Mami ba, wasa wasa saiga shakuwa ta shuga tsakanina da Nurein harya fara bayyana min asirin zuciyarsa tun ina sharesa amma yawan nacinsa yasa na amshi soyayyar sa, kamar da wasa muka fara soyayay mai zafi harta kai ga muna batun aure. __________Ashirye ya futo cikin da kakkiyar shaddarsa ruwan zuma kallo ɗaya zakayiwa shaddar kasan bata kananun kuɗi bace wani kyalli take da walkiyya mai ɗaukar idanu hannunsa ɗaure yakeda agogo na zallar fata baki, yakafa hular tangaran ta zauna das akan nasa kafafunsa na saye cikin tsadaddan takalmi Haf shoe baki mai matukar kyau, tunda yafuto Jakadiya take binsa tana masa kirari dariya ta bashi sosai yanda take zuzuta sa saida yadara wanda hakan yasa Umma dake zaune a falon ta ce "Lah yau wacce rana Turaki yana dariya gaskiyya jakadiya nabaki dubu hamsin" guɗa jakadiya tayi wacce tasa Turaki ya toshe kunnansa yana murmushi ya kalli Juhaina dake zaune gefan Umma tayi tagumi tareda zubawa Turakin idanu ba karamin kyau yayi mata ba yau nan take wani abu ya tokare kirjinta, Turaki zama yayi a kusa da'ita ganin yanda ta kafesa da idanu ya ce "Autar Umma lafiya kike kuwa irin wannan kallon kamar baki sanni ba" taɓe baki tayi tareda mikewa ta shuge ɗakinta faɗawa saman gado tayi ta fashe da kuka, tarasa yaya zatayi da soyayyar Fu'ad ta kasa son ko wanne namiji shi kaɗai takewa wani irin so, wayarta ta ɗauka ta kira lambar Khady tana kuka take cewa "Deeja na kasa jurewa soyayyar Yah Yarima zata kashe ni yaya zanyi ina zansa kaina naji daɗi, inata kokarin ganin na manta da soyayyarsa amma yau ganinsa ya tada min tsohon mikin son sa daya jima yana addabar zuciyata, nayita nuna masa ta hanyoyi daban daban acan baya amma yakasa ganewa" "Juhaina ya kikeso ki maida mana hannun agogo baya, ya zakiyi da Abdallah kuma wanda kika amshi soyayyarsa dan Allah ki manta da wani Ameen sauran wata" Khady ta faɗa ranta ɓace bayanta Turaki yabi ya tsaya bakin kofa yana jiyo maganganunta da khady shuga yayi ciki ya zauna gefan gado saida ya zauna ɗin sannan ta gansa da sauri ta kashe wayan tana maida kanta saman fulo "Tashi ki gayamin da gaske sona kike mai yasa kike sona?" Sake ɓoye fuskarta tayi cikin fulo, ganin baza tayi magana ba yasa yamike tareda faɗin "Shi kenan ni zanje kano na dawo anjima zanzo saiki faɗamin da gaske kike sona zaki aure ni?" Fucewa yayi daga gidan har zuwa inda tawagar fadawa suke waɗanda zasuyi masa rakiya zuwa kano, zai biya ta masarauta yakai sakon mai martaba. Sai bayan sallar La'asar Turaki ya shuga gidanmu dake tarauni mai gadi bai tsaya tambaya ba yabuɗe masu get tawagar motocin guda biyar suka shuga ciki, Turaki ya shuga main falo da sallama, gidan shuru kamar ba kowa saida yasake sallama sannan hanne mai aiki ta futo, murmushi tayi dan ta ganesa saidai jikinta yai sanyi sosai dan ganinsa saiya tuna mata da Uncle Fahad mutumin kirki,gaishesa tayi sannan ta wuce ciki ta sanar da su Ummi zuwansa tare suka futo da Mami ya zube kasan carfet yana gaidasu, tuni hawaye yafara wanke fuskar Mami Ummi dake ciccin magani ta ce "Fu'ad sai yau Allah yakawo ka kai mana gaisuwar Fahad samada shekaru uku da rasuwarsa" Arazane yaɗago yana kallon Ummi muryarsa tana rawa ya ce "Ummi ban gane ba mai kike faɗa haka ina Fahad" Mami da har tafara kuka ta ce "Fahad Allah yai masa rasuwa wata biyar da bikinsa yan fashi suka shugar masa gida suka kashe sa" "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, la'ilaha illallah muhammadan rasulilla"abinda Turaki yake iya faɗa kenan kafin yafashe da matsanancin kuka.. 07039793439 [6/10, 7:37 AM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 25&26 Kuka yake sosai yajima yana kukan wanda kukan nasa ya kuma karyarwa da Mami zuciya ta wuce ɗakinta itama tana kuka,ya jima yana kuka har sanda Yaya Jabeer yadawo yai masa rakiya makabartar da'aka binne Ankul, sosai yai masa addu'a kafin zuciyarsa ta karye yashuga basa hakuri kan rashin zuwansa, kamar wani mahaukaci haka yake zaro zance naban hakuri kamar wanda yake magana da yarayyan mutum, har saida Yaya Jabeer ya rukosa suka futo zuwa wajan mota har sannan kuka yake, bayan sun dawo gida Abinci Ummi ta kawowa Fu'ad ba yanda zaiyi haka yafara tsakurar abincin dan yafaɗawa Ummi shifa a koshe yake amma ta kafe saiya ci, zuba idanu yake yaga gilmawar Su'ad amma shuru ba alamarta, kunya tasa yakasa tambayar ina take, gabansa yabuga da karfi har saida yasa hannu ya dafe kirjinsa ya lumshe idanu yana addu'ar Allah yasa ba wani auran tayi ba, tabbas idan akace Su'ad ta auri wani bayan Uncle to kuwa ya cika mara sa'a a rayuwa, lumshe ido yayi tareda kwantar da kansa saman seater yanajin zuciyarsa naci gaba da bugawa kamar zata fasa kirjinsa ta fito saboda fargaba. Tun daga bakin gate na gidanmu nasan yau munada babban bako ganin manya manya motoci acikin gidan, can gefe na faka motata Ameera ta kalleni da alamar tambaya ta ce "Anty yau wa muka samu a gidan nan yacika da fadawa haka?" Ban bata amsa ba sakamakon gabana da yai wata irin faɗuwa, na futo daga motar na ruko laidar hannuna dana siyo mana yoghurt Ameera tuni ta shuge ciki ni kuma saida na tsaya na kulle motar sannan na shuga zuwa ciki, lumshe idanuna nayi saboda wani daddaɗan kamshin turare dana shaka tabbas nasan kamshi nan amma na rasa a inda nasansa, cigaba nayi da tafiya har zuwa falo na uku inda komai nawa ya tsaya cak na wucin gadi sakamakon idonsa daya shuga cikin nawa ledar hannuna na saki sannan na wuce ɗakina da gudu ina sakin wani marayan kuka😥ganinsa danayi yatuna min da masoyina Fahad, sosai nake kuka har zuwa sanda Ummi ta shugo ɗakina "Wai wannan kukan na menene najin daɗin ganin Fu'ad ne kona me?" "Ummi Uncle! dana gansa sai naga kamar zan gansa tareda Uncle ɗina,ban saba ganinsa shi kaɗai ba ko yaushe zan gansa yana tare da Uncle ɗina, Ummi da gaske Uncle yatafi kenan bazai kuma dawowa ba?"bazai sake rayuwa tare damu ba?"shi kenan mun rabu, bazan sake ganin saba bare naji ko muryarsa!" "Su'ad zaki fara ko, to kije sitting room Fu'ad ɗin yana can zai maki gaisuwa" "Gaisuwa kuma Ummi shekara nawa da mutuwar Uncle maiya hana sa zuwa sai yau yaga damar zuwa" "Idan kikaje sai kiji dalilinsa na kin zuwan" tana gama faɗar haka ta fuce daga cikin ɗakin, ban futa ba har saida Amira tazo tace "Ummi tace lalle ki futo wajan Uncle Fu'ad karta shugo ta sameki" Da sauri na ɗago na kalli Ameera sai kuma na duro daga gadon na yafa mayafina na fuce daga ɗakin. Zaune na same sa ya saka kansa cikin kafafuwansa sallamar danai tasa ya ɗago yana kallona da jajayan idanunsa dasuka sha kuka, kujeran dake kallon wacce yake kai na zauna batare da na gaidashi ba dan Allah yagani batun yau ba nakejin haushin Fu'ad saboda nasan yanda suke da Fahad bai kamata ace har zuwa shekarun nan baizo gaisuwa ba. "Ashe Fahad mutuwa yayi?"mai yasa ba'a gayamin ba?"ina can ina rayuwa ashe nayi rashin aboki amini ɗan uwa" "Ashe dama ka damu dashi ainazaci daka damu dashi daka nemesa a tsawon wannan lokacin" "Bana kasar nan Princess ina london shekaru uku kenan, yanzu hakama saboda shi nabaro tarin ayyukan dake gabana nazo kawai danna gansa saboda ina kiran lambobinsa basa shugowa, gaya min ina yan fashin da suka kashemin aboki an yanke masu hukunci" "E! an yanke masu, amma Zainaba har yanzu tana raye a gidan yari" "Maiya kawo Zainaba cikin wannan zancan" komai daya faru na kwashe na gaya masa, idanunsa yai ja sosai alamar ɓacin rai ya ce "Matsalar kasan nan kenan shi kenan ita baza'a kasheta ba yanzu ba time damunje gidan yarin amma zan dawo nan da friday yazama dole akashe ta kamar yanda takashe min aboki" mikewa yayi yana kallona ya ce "Zan koma sai...shuru yayi bai karasa ba sakamakon shugowar Ameera ta miko min wayata tace "Anty gashi Yaya Nurein ke kiranki" amsar wayar nayi ita kuma ta futa, kara wayan nayi a kunnena ina murmushi "Ina kika shuga kika bar wayarki inata kira?" "Nayi bako ne ina sitting room nabar wayan a ɗakina" "Bako Su'ad maiyazo yi wajanki" murmushi nayi ina kallon Fu'ad ta gefan ido ganin yanda ya kafeni da idanunsa yana aunamin wani kallo dana kasa gane na mene, hakan yasa na kara narkar da murya cikeda shakawaɓa na ce "Kai Hubby maine na damuwa abokin Uncle ne fa yazomin gaisuwa kaima kasan babu wani a zuciyata inba kai...ban karasa ba naga Fu'ad a kaina yana huci ya fisge wayar yasa ta a aljihunsa yafuce daga ɗakin a fusace, murmushi nayi inabin bayansa "Kabani wayata nidai" bai juyo ba yaci gaba da tafiyarsa ina biye dashi har mukaje falon karshe, saida yakama handling na kofa ba tare daya juyo ba ya ce "Karki sake naga kafarki a compound wallahi sai ranki ya ɓaci harni zaki rainawa hankali a gabana kina kiran wani da Hubby" Dariya yabani sosai amma na maze nace "To naga mijina ne sainaki kiransa da Hubby dan kana wajan nidai ka bani wayata in kuma baka da wayane tona bar maka" juyowa yayi ya kalleni yai kwafa tareda girgiza kai yafuce da sauri, dariya nayi nima na juya zuwa ciki ina murmushi... Tunda yashuga mota ransa ke ɓace ko kallon Chiroma dake masa hira baiyi ba yana kallo kiran Baraka yana shugowa harya katse bai ɗagaba sai dare sosai suka shuga garin nasu dan suna tsaya yin sallar mangariba da insha data riskesu a hanya,yana shiga gida wanka yayi yai shirin barci sai sannan yakira Baraka bugun farko kuwa ta ɗaga kamar daman jiran kiran nasa take, gaishesa tayi kana ta ce "Dan Allah Abban Su'ad zan biyi su Usman zasu taho nageria duk zaman nan bayamin daɗi gashi kai har yanzu baka dawo ba kusan satinka biyu kenan" "Bance ki tawo ba ki zauna nima na kusa dawowa" rokonsa tashugayi hardai ya sakko ya barta ta biyo Usman ɗin su tawo tare, yana ajje wayar ya ɗauki wayar Su'ad duk yanda yaso ya gano pin ɗin scirity dake jiki kasawa yayi sai ajje wayar yayi da niyyar gobe zai bawa Chiroma asan yanda za'ayi a cire masa scurity ɗin jiki. Nikam tunda na koma ɗaki nake cikin nishaɗi wanda na rasa na menene fushin da Fu'ad yayi yatabbatarmin da har yanzu yana sona saidai niɗin ina sonsa har yanzu tambayar danaiwa zuciyata kenan inma ina sonsa ina zankai soyayyar Nurein anya inna juya masa baya banci amanarsa ba, amma to Fu'ad har yanzu bayada aure ko yanada shi kilama bayan mata harda yara, shuru nayi tareda jan uban tagumi anan har Ameera ta shugo ta sameni,wayar Mami ce a hanunta ta ce "Anty Game fa nake amma Nurein sai kira yake Mami tace nakawo maki ina kika saka wayarki?" amsar wayar nayi na kirasa tambayar daya faramin "Ina wayarki?"maine tsakaninki da Turaki Fu'ad an tabbatarmin shine yazo gunki yau" Murmushi nayi inabin wayar da kallo nace "Wayata ta faɗa ruwa, Fu'ad kuma banida wata alaka da shi a yanzu kawai yazo gaisuwar abokinsa ne" "Abaya akwai wata alakar kenan?" ya tambayeni ransa ɓace bai jira amsata ba yaci gaba da magana "Su'ad gaskiyya bazan laminci ganinki da wani ba kibani dama kawai na turo manya na indai da gaske kike sona kuma zaki aure ni" "Amma kasan tsakanina dakai ba yaudara ko?" "Ki tabbatarmin da hakan ta hanyar bani izinin turowa gidanku a saka mana rana" "Naji to na amince ka turo ɗin" kashe wayar yayi tareda mikewa zuwa ciki sashin Abbansa yasan yanzu acan zai tadda Mamansa, ilai kuwa kamar yanda yazata ɗin tana sashin suna tareda Abba sunacin abinci saida yajira suka gama kafin yafara magana "Abba daman akwai wacce nake zuwa wajanta to sai akace na turo manya shine nace bari na gaya maka" Mama ta kama baki alamar mamaki tace "Ikon Allah daman wai kanada budurwa Nurein amma baka taɓa zancanta ba dani harna fara magana da innarku saude a haɗaka da Halima ɗiyarta wace wannan kuwa" "Ma'ma Su'ad sunanta yar kawarki Mami" mug ɗin hannunta datake shan yoghourt ne ya suɓuce ya faɗi tana kallonsa da mamaki "Yanzu Nurein duk yammatan dake garin nan karasa wazaka aura sai bazawara kana saurayinka" mur yasha kamar bai taɓa dariya ba yana kalon Abbansa dayai shuru yana kallonsu "Abba ai auran bazawara ba haramun bane ko?" yatambayi Abban nasa "Hakane Nurein ba haramun bane sunna ce ma, nayi farin ciki da faruwar hakan gobe zan yiwa Alhaji islama'il magana sai suje" "Yauwa Abba na gode Allah ya kara girma" "Kai saurareni kajini da kyau, na rantse da Allah ko bayan raina ka auri yarinyar nan ban yafe ba! bandama rigima irintaka ina kai ina ita shekara nawa ka bata yarinyar ma da'ake zargin ita ta kashe mijinta..."kinga ya isheki haka kai Nurein jeka ciki" Abba ta inda yake shuga bata nan yake futa ba tas ya wanke maman ya tashi ya shuge ɗakinsa, itako kwafa tayi ta koma nata ɗakin tana zagayan neman mafuta. Chiroma da computer ɗinsa yai amfani ya cire tsaron dake cikin wayar Su'ad yabawa Turaki, ahankali yake duba wayar harya shugo wajan sakonni sosai yasha mamakin irin zafafan sakonni da Nurein ke aikowa da Su'ad itama bata sanya wajan maida masa da martani, kansa yaji ya sara masa tareda wani irin bugawa da kirjinsa yayi har saida ya dafe wajan, duk Chiroma yana kallonsa baice komaiba dan yanada labarin soyayyar sa da Fu'ad, wanka Fu'ad yashuga ya futo ya shirya cikin bakar jallabiya mai gajeran hannu ya nufi sashin Umma, yanda yake tafiya cikin sanyin jiki yasa Umma take kallonsa da tausayawa harya zauna kujerar kusada ita yana gaidata "Al'ameen ashe abokinka Allah yai masa rasuwa ɗazu Chiroma ke gayamin daya shugo nan Allah yai masa rahma" "Ameen Umma yanzuma zuwa nayi nace a shirya Baby Su'ad zamuje kano dana ce sai friday zan shuga saboda case ɗin waɗanda suka kashe sa, amma bazan iya bari har sai zuwa juma'a ba" "Ok tana ciki tareda Juhaina inagama tai mata wanka tun ɗazu" mikewa yayi ya shuga ɗakin Juhaina, tana zaune gefan gado kusada ita Baby Su'ad ce tana wasa da teddy da sallama ya shuga ɗakin ya zauna saman kujera yana kallon Juhaina datai kasa da kanta, da gudu Baby Su'ad tazo ta faɗa jikinsa ya rungumeta yana kallon Juhaina yace "ɗago ki kalleni magana zamuyi ta fahimta, batun yau ba nasan kina sona ajiya naso na faranta maki ta hanyar auranki amma wani dalili mai karfi ya gifta wanda yasa na fasa, nasan kinsan labarin Su'ad da irin son danake mata jiya naje garinsu na samu mijinta ya rasu, zan maye gurbinsa zan auri Su'ad a wannan karan insha Allah ina sonta! wani irin so nake mata wanda bantaɓa yiwa wata ɗiya mace ba a duniya son danake mata yasa bazan iya haɗata dake ba, Baraka ma bansan yanda zanyi da'ita ba! idan kinada wani dayake sonki ki basa dama yafuto idan kuma babu ina neman alfarmar ki karɓi tayin soyayyar da Chiroma yai maki" Da sauri ta ɗago tana kallon Fu'ad har sannan idanunta na zubda hawaye tace "Shi kenan na hakura dakai amma kasani zuciyata tana sonka! nabaka zaɓi ka zaɓarmin Chiroma ko Abdallah ɗan sarkin gombe" Shuru yayi yana nazari kana ya ce "Ke wanne yafi kyanta maki arai ke zaki zauna da abinki bani zan zauna maki ba tayaya zan maki zaɓi" "Nazaɓi Abdallah inaso nai naisa dakai bazan iya auran Chiroma ba saboda nasan ko yaushe kuna tare zan rinka ganinka akai akai wanda hakan zai iya haifar min da matsala" "Shi kenan zanyiwa mai martaba magana ki faɗawa Abdallah ɗin yaturo a tsaida rana kawai" mikewa yayi ya futa, Juhaina tabi bayansa da kallo yana futa ta kifa kan gadon ta fashe da kuka, shi kenan Su'ad ta rusa mata burinta, batajin zata taɓa son yarinyar nan da yaya Turaki ke matuwar so sai tayi duk wani abu datasan zai bakanta mata rai a duk ranar data shigo gidan... 07039793439 [6/11, 9:46 AM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 27&28 Ashe batada rabon auran Turaki ta leko ta koma yayi mata😰kuka take sosai har Umma ta shugo ta sameta, faɗa tai mata sosai tariga tasan son datakewa Turaki. Shi kuwa a nasa ɓangaran shirinsa yake hankali kwance yau jinsa yake cikin wani irin nishaɗi wanda yajima baijisa a cikiba gefe kuma ga kewar Fahad datake damunsa, a haka yagama shirinsa cikin bakin materi'al mai ɗigon fari, ya kafa hula zanna bukar wacce aka ɗinkata da bakin zare sosai shugar tai masa kyau yasha naɗin rawani baki, cikin kwanciyar hankali da nutsuwa yake tuka motarsa Baby Su'ad na zaune gefansa tana shan ice cream ɗin daya sai mata a hanya, surutu take masa shi sam hankalinsa ba'a kanta yake ba yanaga Su'ad hangota yake da tunanin yanda zasu kaya a karo na biyu shin zata amshi soyayyarsa ko zata ki, a yanda ya fahimceta jiya kamar ta manta da shi Nurein yake ko wa shine a gabanta, tabbas a wannan karon jiyake komai zai faru saidai yafuru amma bazai taɓa bari ta kuɓuce masa a wannan karon ba. Yau tun safe banida aikinyi sai barci tun goma na safe danai break nasake kwanciya saboda gidan ba kowa saini kaɗai sai hanne mai aikin gidanmu, ina sanye cikin kayan barci dogon wando da riga iya cinya sai hula dana saka akaina barci make sosai sonake na huta kafin huɗu na yamma na shiga shagonmu yau Mami ce acan nasan kuma zuwa yamma zata dawo ni na karɓeta wajan ba laifi sosai muke samun costomer masu zuwa gyaran gashi wasu kuma kunshi ko kitso dan wajan ba abinda bamayi harda kwalliyar amare. Cikin barci naji ana dukan kofata a hankali, buɗe idona na kalli agogo 11:45 am dirowa nayi daga kan gadon ina turo baki da jin haushin wacce ke bugomin kofa ta katsemin barcina mai daɗi nasanma hanne ce, hakan yasa na buɗe kofar idanuna rufe nake magana ina mika da'alamar barcin bai isheni ba "Dan Allah hanne maine haka ina barci na mai daɗi harda mafarki kikazo kika tasheni" nakarasa faɗe ina mika tareda buɗe ido zaro idanu nayi😳 ina komawa da baya ganin wanda ke tsaye a bakin kofar cikeda mamaki na ce "Fu'ad lafiya da safiyar nan?" da gudu wata kyakkyawar baby tazo tarikeni cikin muryarsu ta yara tace "momma kicewa Papi ya maidani wajan Nani na nidai banason nan" rungume yarinyar nayi koba tambaya kamanninta kaɗai sun tabbatar minda yar Fu'ad ce ɗagowa nayi ina kallonsa naga yanda ya kafeni da idanunsa kallona yake bako kiftawa, da sauri na kalli jikina kama hannun yarinyar nayi muka koma cikin ɗakina, nauyayyar ajjiyar zuciya ya sauke ya juya ya koma main falo ya zauna. Ina shuga ɗaki wanka na faɗa agurguje na futo na bar Baby ita kaɗai cream kawai na murza na zura doguwar riga na tareda hijab na ɗauki Baby muka futo, sosai ta lafe ajikina na ɗago fuskarta ina mata murmushi na ce "Ya sunanki?" "Aminatu Su'ad Ameen" lumshe idanuna nayi sakamakon wani daɗi daya ziyarce ni ko tantama babu Fu'ad sunana ya sakawa yarsa. Wani abu naji yatokaremin a kirji wanda babu ko tantama nasan kishine kenan wata ya aura bayan mun rabo, ashe daman zai iya auren wata inba niba, hamdala nayi a zuciyata tunawa da nayi yanda narinka masa addu'ar Allah yabasa wacce tafini kila Allah ne ya amsa addu'ata yabasa wata, saida na zauna kujerar nesa dashi kaɗan na ɗora Baby a kan cinyata sannan na kwalawa Hanne kira takozo da saurinta "Hanne kawomin abinci na bawa Baby na tasha hanya ki haɗomin da yoghourt bamai sanyi sosai ba"Baby na ai zakisha yoghourt ko?" na faɗa ina kallon fuskar Baby Su'ad "Kin manta dani ne?" "Maizan maka to kaje matarka ta baka" nafaɗi haka ina shafa kan Baby da naji ta shuga raina sosai jinta nake kamar nina haifeta, wasu hawaye suka zubomin dana tuna da tunifa nizan haifi yarinyar nan, da'ace Uncle yanada lafiya da tuni nima kila na haifi kamar wannan, "Subhanalla wannan hawayan fa, nifa ba kuka nazo kiminba zuwa nayi mu dai daita kanmu sonake na aureki nan bada jimawa ba, Su'ad kamar yanda kika sani abaya haka yake har yanzu soyayyarki tana nan cikin zuciyata" "Dakata Fu'ad kamanta duk wata soyayya da mukai dakai abaya yanzu babu ita a zuciyata bana sonka bazan iya auranka ba alhalin kanada wata matar wacce nasan ita kafara so kafinni" "Kema kinsan ba wacce nakeso nan duniya inba keba, kalli Baby Su'ad dake hannunki kawai zai tabbatar maki da kaunar danake maki, dan Allah ki ajje batun wata matata kizo mu sasanta kanmu muyi aure shine burinmu" Wallahi kaji na rantse bazan aureka ba, tuni na samu wanda nakeso kuma zan aura bazan taɓa yaudararsa ba" ina gama faɗin haka na saɓa Baby a kafaɗa na wuce danning da'ita nabarsa nan zaune, na kula ba karamin haushi yaji ba nan yabarmin Su'ad yai tafiyarsa nayi zaton zai dawo ya ɗakketa amma har yamma shuru harsu Mami suka dawo suna tambayata ina na sami yarinya nagaya masu yar Fu'ad ce. Fu'ad afusace yabar garin yanajin wani bakin ciki dayazo ya tokare masa a kirji harshi Su'ad zata kalla ta ce bazata aure shi ba, bayan ɗimbin soyayyar dasukayi abaya tun a hanya yafara jin zazzaɓi zazzaɓi da wani ciwon kai da kyar ya karasa gida, wasa wasa saiga ciwo ya kwantar dashi wani irin Zazzaɓi yake mai zafi da ciwon kai mai tsanani, shi kaɗai yake jinyarsa a ɗaki ko mutanan gida basu san bayada lafiya ba sai ranar da Baraka suka sauka a kasar itada Usman da matarsa, gidan mai martaba suka sauka Umma tai mata izinin shuga sashin Fu'ad ɗin bayan taci abinci ta ɗan huta. Yana kwance lamo kan gado ta shugo ɗakin da sallama, ɗago kai kurum yayi yana kallonta baice mata komaiba yamaida kansa ya kwantar saman fulo, da sauri ta zauna kusa dashi ta taɓa jikinsa taji zafi zau gaba ɗaya ruɗewa tayi "Abban Su'ad bakada lafiya daman kake zaune kai ɗaya a ɗaki" batajira cewarsa ba ta futa da sauri zuwa sashin Umma ta sanar mata, tare suka dawo ciki hankali tashe Umma ta kira sarkin mota Usman shiya ruko Fu'ad saboda gaba ɗaya jikinsa ya saki bayada wani kuzari, yanda kirjinsa ke bugawa yafi komai ɗaga masu hankali. Baby Su'ad tana wajena yau kwannanta huɗu kenan mun shaku sosai kasancewar batada wuyar sabo, kullum tanamin zancan Papi zai zo yaɗauketa, dariya nake mata nace kin gaji da zama dani saita girgiza kai alamar a'a, tun ina zuba idanun ganin Fu'ad har nasoma fargabar maiya hanasa dawowa duk da daman na lura ba karamin kular dashi nayi ba, har sannan ba waya a hannuna sau tari data Mami nake amfani data tambayeni ina tawa ce mata nayi a makaranta ta faɗi ban ganta ba, yau satin Su'ad ɗaya a gidanmu tunda ta tashi take kuka ita wajan Papi zata ita nakaita wajan Papinta, jin kukan yayi yawa yasa Mami tace na shirya na maidata garinsu da mamaki nake kallonta na ce "Mami ni ina nasan wani garin su inma nasa garin nasan gidanne?" "Ga Shareef nan yana gari ki shirya ya kaiku" ba yanda nayi haka na shiryawa Baby kayanta dana sai mata da tarkacan kayan wasanta, muka doshi garin su Fu'ad tunda muka ɗauki hanya gabana yake faɗuwa haka kurum nakeji ajikina kamar akwai abinda yasami Fu'ad shiya hanasa zuwa ko kuma fushi yayi dani, Allah yasani har yanzu ina son Fu'ad amma banajin zan iya auransa saboda yanada mata son danake masa yasa bazan iya zama dashi yanada wata matar ba, inata wannan tunanin barci ya ɗaukeni har muka isa gidan sarki, bamu sha wahalar shuga gidan ba saboda ganinmu da sukayi da Baby Su'ad, sarkin mota yafara ganinmu ya washe baki yana dariya ya ce "Hajiya barka da zuwa, kunzo kuma gidan basa nan yanzu Umma ta futa asibitin da Turakin yake" da sauri na ɗago na kalleshi muryata tana rawa na ce "Baba maiya sami Fu'ad ɗin?" "E to nadaiji ance ciwon damuwa ne" sarkin mota shiya mana jagora zuwa hospital ɗin Fu'ad na zaune jingine da fulo Usman yana gefansa ransa a ɓace sai masifa yake "Akan wata banza can kake neman kashe kanka dan tace bazata aureka ba saime, ni ban taɓa ganin irin wannan mahaukacin son ba, basu baka ita ba tana budurwa yanzuma data zama bazawara sai sun tsaya suna ja maka rai kamar itace..."Ya isheka Uthman kasan abinda zaka rinka faɗawa Su'ad itace rayuwa ta ruhina, wallahi a wannan karan na rasata mutuwa zanyi na gaya maka damuwata ne danka taimaka min baka zauna kana gayamin maganganun dazasu karamin ciwo ba, so ba karya bane na tabbata kasan mainene so tunda auran soyayya kayi! Su'ad koda ace ta tsufa mijinta ya rasu wallahi zan iya auranta a ko wanne yanayi take ita nakeso ba wani abu na jikinta ba *itace burina* idan nasameta banida sauran wata damuwa, dan Allah na rokeka kaje ka lallaɓamin ita ta daure ta aureni dan Allah" Fu'ad yafaɗi haka yana saka hannunsa cikin na Usman🤝 Jikin Uthman yai sanyi yana bin ɗan uwan nasa kuma aboki da kallo yama kasa magana sai kafesa dayai da idanu yana kallon yanda hawaye ke zubowa daga idanun Fu'ad hannunsa yaruko zaiyi magana sallamar mu tasa yai shuru da sauri na isa gaban gadon cikeda damuwa ganin yanda Fu'ad yai wata iriyar rama ya kara fari kamar wanda ba jini a jikinsa, ganina dayayi tsaye a kansa yasa ya ce "Kagani ko Uthman kana kallo tafara min gizo ko Aboki gayamin kodai na haukace ne ita nake gani a gabana dan Allah Uthaman karka tashe ni daga wannam barcin danake ka barni na dawwama tare da ita a cikin mafarki na, hannu ya miko min alamar na matso kusa da shi, ban matsan ba saima komawa gefe danai nasoma kuka "Kaima mutuwa zakayi kabarni kamar yanda Uncle yatafi ya barni, nifa wasa nake maka ko yanzu ka shirya na amince zan aureka indai hakan zaisa ka farin ciki, kasani ina sonka! inason ganinka cikin farin ciki da walwala kwanciyar hankalinka shine nawa", lumshe idanu yayi tareda maida kansa saman fulo ya kwanta yana mikomin hannu, hannuna nasa cikin nasa ya janyoni na faɗa jikinsa yasa hannayansa ya rungumeni yana sauke numfashi, muna a wannan yanayin har bamusan sanda Uthman ya futa ba, da sauri na janye jikina daga nasa tuna cewa hakan haramunne, Allah yayi hani da haka da sauri na fara furta Astagafirillah na koma can gefansa na zauna ina kallon sa, ya rame sosai sai uban haske daya kara. "Zubamin abinci yunwa nakeji" Basket ɗin dake ajje saman fridge na ɗakko na buɗe warmars na zuba masa fatan dankali dayasha hanta da alayyahu sai tashin kamshi yake, na mika masa plate ɗin amma sai yaki karɓa sai hannu yasa ya ɗauki spoon ɗin yafara ɗiban abincin ahankali yana ci ni kuma ina rike da plate ɗin abincin, muna a haka ta shugo da sallama, kyakkyawar maca ce fara kakkaura, tana rikeda da Baby Su'ad sai dariya take mata, take gabana ya faɗi daga gani ba tambayya na tabbata wannan ce matar Fu'ad mahaifiyar Baby Su'ad, zama tayi kusa dashi tareda taɓa jikinsa ta ce "Dear yaya jikin naka?" "Da sauki" yabata amsa a takaice yaci gaba da cin abincin nasa, ɗagowa nayi na sake kallonta itama ni take kallo tana aunamin harara. "Princess bani ruwa" Fu'ad da muryar maras lafiya, atare muka mike da ita na rigata isa gaban fridge saboda yafi kusa dani, ruwan gora na ɗakko masa na ɓalle masa murfin na basa a hannu ya kafa kai ya shanye ruwan tas, plate ɗin abincin na ɗauke wanda shima yaci dayawa na ajje sa saman fridge bayan nasa wani plate ɗin na rufe. Yanda ta shugo ɗakin cikin nutsuwa da kamala haɗe da cikakkiyar sallama yasa na maida hankali ga dattijuwan matar wacce nake zaton bazata wuce shekaru hamsin da biyar ba zuwa sittin, yanda naga fadawa na take mata baya ga yammata biyu atare da'ita ɗaya na rikeda hand bag ɗayan kuma na rikeda wayoyinta, hakan yasa na gane itace Umma matar mai martaba, hannuna ta ruko tana murmushi ta ce "Sannu da zuwa Su'ad ɗin Fu'ad yanzu sarkin mota yake gayamin kunzo kun kawo baby Su'ad" Kasa na zame ina gaidata cikeda girmamawa, hannu tasa ta ɗagoni ta maidani gefan gado na zauna. "One Boy yaya jikin, sai kuma ga Sweet heart tazo cuta ta warke" Murmushi kurum yayi sai sannan Umma taga Baraka dake zaune can gaban gadon kan kujera, "Ran uwargida ya daɗe yaushe kika zo, na baroki a gida kin rigani zuwa,kodan na tsaya duba marassa lafiya a genarel hospital" Baraka murmushi kurum tayi taci gaba da danna wayarta, Umma katuwar dadduma ta shimfiɗa ta zauna nima ta umarceni dana zauna ta zubomin abinci, kasa cin abincin nayi sai danna wayata da nake, shugowar Dr yasa na mike zan futa, dan tun ɗazu nake zuba idanu naga ta inda Yaya Shareef zai ɓullo amma shuru gashi har anfara kiran sallar la'asar, futa nayi ina lalubansa amma babu shi babu alamunsa ko matarsa ma bata inda ya ajjeta, cikeda damuwa nake danna lambarsa harta shuga bugun farko yaɗaga yanamin dariya. "Yah Shareef ina kaje ne?naga baka compound na hospital ɗin" "Waini kike tambayya toni kin ganni nan a abuja nafi minti talatin ma da sauka" Shar shar idanuna suka zubo da kwalla "Yaya zakamin haka ka barni a garin mutane katafi ka barni yanzu yaya zanyi na koma gida?" "Kinga kwantar da hankalinki motata ma tana nan garin jirgi nabi saboda kiran gaggawa na samu daga office, Umman mai martaba ita tace na barki gobe su Mami zasuzo duba Fu'ad saiku wuce tare" "Kwana kuma yaya anan garin kai haba bazan iya ba" "Bazaki iya kwanan gidan surukai ba" naji an faɗa daga bayana katse wayar nayi na juyo ina kallon Umma dake magana "Kiyi hakuri ni nayiwa Maminki waya ta turo mana ke Fu'ad yana cikin kunci da damuwa kamar yanda abokinsa Uthman yagayan kece damuwar Fu'ad, kiyi hakuri inma wani laifi yayi maki ku sasanta, yana sonki sosai Su'ad inya rasaki a wannan karon bazai iya jurewa ba, zuciyarsa tayi rauni sosai a kaunarki ki tausaya masa" Sunne kaina nayi kasa ina wasada zoben hannuna ganin bance komai ba yasa taja hannuna muka koma ɗakin, bakin mata da miji muka tarar jin danai Umma ta ce "Lale da Abiee munyi fushi sai yau kazo duba one boy ɗin nawa" hakan data faɗa yasa na gane mahaifin Fu'ad ne wannan "Ayi hakuri abubuwane sukayi yawa musamman wannan guguwar zaɓan data tunkaro mu bamuda lokacin kanmu kullum muna yawon kamfen, kuma nasan zuwan nawa ma baida amfani tunda gaku keda mai martaba,sannan ga Antynsa itama tana kusa tunda taki zaman abuja" Dariya Umma tayi batace komai ba, kallo ɗaya Anty Jameela tamin ta ɗauke kanta taci gaba da danna wayarta, nima shareta nayi nagaida Abiee kawai wanda ya amsa fuska sake yana tambayar Umma "Asiyya ina kika samu ya" "Au ashefa baka santa ba ita ta zaunar da Fu'ad anan" Umma tana faɗar haka yadafe baki🤭cikeda mamaki ya ce "Au anyi abun kunya nakasa gane Su'ad ɗin Fu'ad, haba shiyasa naga bakin ɗan naki yaki rufuwa" wani kallo da Anty Jameela tayi masa yasa yai shuru badan yagama magana ba, ɗakin yai shuru har sukai shirin tafiya, Baraka tabi bayan su tanawa Anty Jameela magana "Anty wai wannan yarinyar wacece ɗin su Abban Su'ad naga sai wani shisshige mata yake gani a waje amma bazai ce inmasa wani abu ba saidai ita" Anty Jameela saida tayi dariya kana tace "Hmmm wannan itace Su'ad budurwar Fu'ad wacce yaiwa mahaukacin so mijinta ya rasu shine yanzu yake so ta auresa, sorrynki yarinya idan har kikayi saken da wannan yarinyar ta shugo maki gida, kiga abata nan ma daya haifi ya sunanta yasa saboda ya raina maki hankali, lokaci yayi da zakizo mu haɗe kai muyaki yarinyar nan dan inkika sake ta shugo kin kaɗe ke matar shige (Anty mai zafafa) ita kuma matar so kinga babu haɗi, dole kiyita ganin takaici" Hannu Baraka ta ɗora aka🙆‍♀️"Wayyo na shuga uku daman Su'ad sunan budurwarsa yasa nifa na zaci na mahaifiyar sa ne, wayyo Allah na Fu'ad yakashe ni"😰gaba Anty Jameela tayi tabar Baraka anan tsaye tana goge hawaye. Nifa duk zaman garin ya'ishe ni, musamman yanda Fu'ad yake wani kallona duk na kasa sakewa hakan da Umma ta lura yasa gabda mangariba tace natashi mutafi gida, Fu'ad ya marairaice fuska "Umma tun yanzu zaku tafi yau bazaki bari ayi sallar insha ba" "E tafiya zanyi bakaga bakuwa ba, gida zamuje tai wanka ta kwanta ta huta gajiyar hanya" bayan Umma nabi data futa naji ya ce "Su'ad jimana" najiyo na kallesa "Wayan waye a hannunki" "Ta Mami ce" nabasa amsa ina kokarin futa,baicemin komai ba harna fuce, a wani babban super market muka tsaya Umma ta zaɓamin dogayan riguna masu kyau nayi amfani dasu tunda banzo da shirin kwana ba sai kayan ciki data sakani na zaɓi size ɗina, koda mukaje gida ɗakinta ta kaini ta haɗamin ruwan wanka nayi na shirya cikin daya daga cikin rigunan data saimin, nai sallar mangariba ina nan zaune ina cin abinci, aka shugo da sallama. ɗago kaina nai na kalli wacce tai sallamar itama kallona tayi ta ɗauke kai batare da tacemin komai ba, Umma ce ta shugo hannunta rikeda plate da aka shakosa da kayan fruit ta ajje agabana tana kallon yarinyar dake zaune gefan gado, "Juhaina bakiga bakuwa ba?Su'ad ce fa budurwa Turaki" Dan taɓe baki tayi tana kauda kai gefe ta ce "Naganta sannu fa" tana gama faɗar haka tai fucewarta daga ɗakin, murmushi Umma tayi tana rakata da kallo harta fuce. Sosai Umma take bani kulawa kamar yarta haka ta maidani, yanda kowa yasanni agidan abin har mamaki yake bani, kwana na biyu a garin aka sallami Turaki daga asibiti saboda yaji sauki sosai, wata irin kula yake bani duk da ni zaman gidan dik ya isheni hakan yasa na kira Mami ina mata korafi "Nifa Mami wallahi tahowa zanyi gida, kawai daga zuwana sun wani rikeni ba dangin iya bana baba inata zama masu a gida" "A'a karki taho ki bari jibi zanzo duba Fu'ad ɗin saimu taho tare" nidai badan son raina nake zaman gidan nan ba wallahi. Da yamma ina zaune nayi wanka nasha kwalliya cikin doguwar rigar Atamfa Umma ta bani washe garin randa naje kusan kala shida da'alama bayarwa tayi aka ɗinkomin su, wayar Mami ce a hannuna ina chat, kiran Nurein daya shugo yasani kwantawa saman doguwar kujera tareda kara wayar a kunnena, ko sallamar danayi bai amsaba ya ce "Wai zaman me kike a garin mutane yau kusan kwananki huɗu kullum nazo bakya nan an shaida min kina bare, garinsu Fu'ad ne fa mai kikeyi?" "Nima zaman yana damuna Hubby nafison nadawo gida amma sunki bani dama jinake kamar na gudu" "Kinga karki rainamin hankali nafasan maike tsakaninki da gayan nan inma ba iskanci ba maiya kaiki zama a garinsu" "Nurein mai kake nufi?" "Kinga dan Allah kitaimakeni ki dawo nifa tsoron gayan nan nake karya kwacemin ke, Su'ad ina matuwar sonki banson abinda zai rabani dake, kinga Abbana harya fara maganar turowa gidanku wata yar matsala aka samu da tuni sunzo ma please dan Allah kidawo" Ajjiyar zuciya nasauke kana nace "Ok naji Hubby zan dawo jibi" Wayar naji an zare daga kunnena a tsorace na mike dan nidai nasan ni kaɗaice a falon, Fu'ad na gani tsaye akaina yana kallona yana juya wayar a hannunsa, kallo ɗaya nayi masa na kauda kaina daga kallon nasa saboda masifar dana hango cikin kwayar idanunsa, cije leɓe yayi ya zauna kan kuja ya ɗora kafa ɗaya kan ɗaya yana girgiza kafar saman, na lura yana son yin magana amma tsabar fushi yasa yakasa cewa komai, nima zama nayi a kujerar dana tashi kaina a kasa ina jiran inji abinda zaice, karar wayar tasa na ɗago ina kallonsa, yanda yake huci yaso tsorata ni kallona yayi ido cikin ido. "Narasa maine maki kika daina sona Princess,na lura so kike ki kasheni da raina, kinsan irin son danake maki kuwa? Kinsan tsawon shekarun nan dai dai da dakika ɗaya sonki bai taɓa raguwa a zuciyata ba, kinssan mainene so kuwa Su'ad kinaso ki kaina lahira kwana na bai kare ba? sa'arki ɗaya wayar nan vataki bace wallahi da yau saina kwankwatsata naga ta inda wannan mayan zai sake kiranki, akaro na biyu karki yadda ayi na uku dan wallahi rai zaiyi matukar ɓaci, akanki zan iya yin komai, wallahi kinji na rantse idan na kara jin kina wayada gayan nan ko kika sake tsautsayi yasa na ganshi to wallahi saina ɗaure sa ko ɗan gidan waye a kasar nan saidai nima a ɗaurenin" yana gama faɗar haka yasa wayar a aljihu yasoma tafiya. "Kabani wayata to, waccan ma ka kwacemin wannan ai ta Mami ce kuma ni gidanmu zan tafi" ganin bai kulani yasa na mike nabi bayansa. "Nifa kabani wayata haka kurum zaka rabani da shi naga tare ka ganmu ko aurata kayi dazaka rinka kafamin sharuɗa" afusace ya juyo kamar zai dake ni yake faɗin "Haka kikace ko? wayar yamiko saida yabuɗe kofa zai futa ya juyo yanamin wani kallo dana kasa fassara sa ya ce "Ki shirya zansa a maidaki gida, kuci gaba da soyayya da Nurein Allah yabarku tare...✍🏻 07039793439 🌹 *KUKAN ZUCIYA* 🌹 Story and Writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 29&30 Gaba ɗaya kuma sai jikina yayi sanyi na koma na zauna, ashe Umma tana kallonmu ta saman mai martaba. "Kibi Turaki a hankali kwanan nan nakasa gane kansa gaba ɗaya ya canza nema yake ya birkice mana, ki shirya nasan yanzu zakiga ya turo ki futo amma banso tafiyarki yau ba, ba komai ai kin kusa zama tamu gaba ɗaya" Nidai bance komai ba na shuga ɗaki na haɗa kayana, ina futowa ko saiga dogari yace nazo, Umma ta kaini wajan mai martaba nai masa sallama, kyautar kuɗi yabani wanda naso kin karɓa Umma tace na karɓa in yayi kyauta ba'a kin amsa haka na karɓa ina godiya, Umma turaruka tabani masu kamshi da materi'al guda huɗu, ita ta rakoni a wajan motar dake parke a compound na gidan, glass ɗin motar mai duhu ne hakan yasa banga wanda ke ciki ba, nadai gane motar ta Fu'ad ce ganin danai ansa Turaki 3 baya Umma ta buɗemin na shuga kamshin turarensa danaji yasa na kalli gefena bayan Umma ta rufe murfin motar,yana zaune cikin motar ya haɗe cikin bakaken suit idanunsa na saye cikin bakin glass mai duhu ya maida hankalinsa kam laptop ɗinsa dake ajje saman kafafunsa ko kallon inda nake baiyi ba yaci gaba da abinda yake, jefi jefi nake ɗan satar kallonsa, ganin ba abinda ya shafesa da irin gudun da sarkin mota keyi. "Nifa kallon nan ya isheni haka" Turaki yafaɗi haka batare daya ɗago ya kalleni ba. Taɓe baki nayi bance komai ba inajinsa yana yan wakokinsa, bance mass kala ba har mukayi nisa, ɗan matsowa da yayi kusa dani yasa nai saurin kallonsa, hannuna ya ɗago yana kallon zoban hannuna, murmushi kwance saman fuskarsa ya ce "Haryanzu dai ina nan da matsayi na tunda ba'a cire zobena ba" zobena dana saka masa a ranar da mukayi ban kwana kafin bikina da Uncle, ya ciro yasaka min a kusa da wancan "Ga wannan nasan zai rinka tuna maki da Uncle duk da nasan shi ba sai lalle da zobe zakina tunasa ba akwai abubuwa da dama" yai kasa da murya cikin sigar lallashi idanunsa cikin nawa ya ce "Kice kikafi kowace mace mahimmanci acikin rayuwata, na rayu tsawon shekaru da soyayyarki, zan iya bada duk kan abinda na mallaka inhar zan same ki, yake masoyiyata ki sani kece mace ɗaya tak danakewa wani irin so da bazan iya misalta sa ba, dan Allah ki daure ki bani dama na futo nan da sati biyu ayi bikinmu nai maki alkawarin baki farin ciki aduk cikin rayuwarki, kibar batun matata ita ɗin kaddarata ce rabon Su'ad yasa aka auramin ita, Su'ad wallahi zuciyata babu soyayyar ko wacce mace inba taki ba" hannuna ya haɗe da nasa ya sumbata sannan ya saki hannun ya matsa can gefe ya ɗora kansa saman kujerar motar yai shuru "Zuciyata kaine kaɗai wanda takeson na riga na faɗa maka tun tuni na amince dakai ko yanzu ka shirya nima na shirya a ɗaura kawai, Nurein yanada zafin zuciya sonake mu rabu lafiya dashi shiyasa kaga ina biye masa amma tuni babu sauran soyayyar sa acikin zuciyata, mai waje yazo kaga mai tabarma dole yatashi, kaddarar auran Uncle tarabamu a baya amma a yanzu ba mai rabamu nidakai mutu ka raba" Wani kallo yake aunamin wanda na kasa tantance na maine shinna farin cikin maganata ne kona sone baice komai ba motar tayi shuru kowa yatafi tunani, karar wayarsa ta dawo damu daga duniyar tunanin da muka lula lokacin har mun shugo kano, kallona yayi kafin ya ɗaga kiran tana kuka take faɗin "Yanzu Abban Su'ad abinda kayimin ka kyautamin kenan, gaba ɗaya ka banzatar dani ka manta dani ka ɗauki wata can banza kun futa yawo wannan adalci ne maine maka haka daka tsaneni" lumshe ido yayi yanajin wani tausayinta na taso masa daga kasan zuciyarsa a hankali ya ce "Kinga ba yawo na futa ba kano naje zan maida Su'ad" yana gama faɗar haka ya kashe wayar sa gaba ɗaya bayason abinda zai katse masa wannan mode ɗin na farin ciki dayake ciki, satar kallon Su'ad yayi wacce ta wani haɗe rai, murmushi yayi a zuciyarsa yana faɗin mata sha'aninsu sai su, sam baitaɓa zaton zaiyi mata biyu ba amma ga yanda kaddara tayi dashi tabbas zaisha fama Baraka kishi Su'ad zuciya. Gabanane yafaɗi sanda muka shuga compound na gidanmu Nurein na hanga tsaye jikin motarsa yanda ya harde hannu a kirjinsa kawai ya nunamin a fusace yake Wani kallo Fu'ad ya watsamin tareda nuna wajan da Nurein yake "Wancan shine Hubbin naki ko hmm" yayi kwafa tareda futa bayan sarkin mota ya buɗe masa murfin motar, ɓangaran danake ya buɗe gabana yana faɗuwa na futo saboda bansan yanda za'a kwashe ba tsakanin Fu'ad da Nurein nikam banso wannan haduwar ba, ina futowa gaba ɗaya Fu'ad ya janyoni jikinsa ya rungumeni ta gefansa na soma kokarin kwacewa saboda ganin mutane awajan amma shi ko'a jikinsa a haka muka fara tafiya inata son cire jikina daga nasa. "Ai basai kayi haka ba, kowa daman yasan abinda kuke aikatawa kenan gashi nan yanzu ka futo ka shaidawa duniya" Nurein ke faɗar haka ransa a matukar ɓace, yacigaba da faɗin "Mai zanyi da ragowar wani kaje na bar maka ita" yana gama faɗar haka ya shuge motarsa yajata a fusace yafuce daga gidan, sakina Fu'ad yayi yana dariya harda rike ciki, ni kuwa gaba ɗaya haushinsa ya kamani da irin abunda yayimin ya wani rirrikeni gaban mutane yabani kunya "Daman saboda shi nayi haka Alhamdulillah kwalliya ta biya kuɗin sabulu ni daman haka nakeso"yana gama faɗar haka ya wuce ciki ya barni raina ɓace. Fu'ad bai wani jima a gidanmu ba ya wuce ashe karaye yatafi sukayi magana da Baban karaye a washe gari kuwa tawagar mai martaba sukaje nemarwa Fu'ad aure atake anan Baban karaye ya tsaida ranar ɗaurin aure sukuma suka bada komai ciki harda sadaki lefene sukace nan da sati ɗaya za'a kawo, ni duk abinda ake ban sani ba saboda rabona da Fu'ad tun da yakawoni ban sake jin ɗuriyar saba, ina zaune a ɗakina Mami ta shugo tanata faman murmushi kusada ni ta zauna ta kamo hannuna tana faɗin "Kinga ikon Allah ko ashe kunada rabon aure da Fu'ad yanzu baban karaye yazo wai an tsaida biki nan da sati biyu har sun biya sadaki" Kafafu na fara bugawa kamar wata karamar yarinya na soma kuka "Ni wallahi ban amince ba shine kawai zaije ya sami baba batareda ya nemi amincewata ba, ni bama yanzu zanyi aure ba sonake naci gaba da karatu na"murmushi Mami tayi tamike ta futa. Nurein tunda yabar gidanmu yake a fusace zuciyarsa yakejin ba daɗi, daman zargin dayake kenan gashi kuma idanunsa ya gane masa wayasan ma irin abinda sukai a can garin shi kuwa Su'ad ko daga ita sai shi suka rage a duniya yabarta bari nahar abada, zaije yaiwa mahaifiyarsa biyayya ta zaɓa masa koma wace ashirye yake daya aure ta. Yana tsaye gaban madubi yana ɗaura agogon rulex a hannunsa na dama, shugowarta ɗakin kenan ta tsaya daga bakin kofa tana kare masa kallo yayi mata kyau sosai ba karamin kyau kayan sarauta ke masa ba amma shi sam bai sani ba shiyasa bai fiya shugar ba, ahankali take takowa har zuwa inda yake tsaye yana kallonta ta madubi amma sai yayi kamar bai ganta ba ya kauda kai yana murmushi, tana zuwa kusa dashi ta rungumesa tareda ɗora kanta saman kafaɗarsa tana kallonsa ta cikin madubin ta ce "Abban Baby kayi kyau sosai sai ina kuma?ko unguwa zaku futa da takawa?" Murmushi yayi "Da gaske nayi kyau?" Kai ta ɗaga masa alamar e kan tace "Kyau sosai ma bakaga yanda kayan nan ke maka kyau ba, amma kai bakason sawa kafi kaunar kayita shugar kananun kaya kamar wani bature" "Naji to sakeni karki ɓatan lokaci kano zani" Wani kunci taji a ranta ashe daman duk wankan nan dayayi kano zashi wajan wannan shegiyar yarinyar tabbas duk yanda zatayi saita ɓata masa wannan kwalliyar sai taja abinda zai saka dole ya canza kaya dan bazata taɓa bari yaje kano da wannan shugar ba hannunta tai saurin ɗorawa kan j ɗinsa da sauri ya juyo zaiyi magana kafin yace komai tai saurin haɗe bakinta da nasa nan take ta fara aika masa da sakonni wanda yakasa jurewa dole ya maida martani, janyo shi tayi suka faɗa saman gado tana wasa da wasu sassa na jikinsa, ganin gaba ɗaya ya gama bada kai yasa tafara cire masa kayan tana jifa dasu kasa bayan ta gama yamutsa su ta yanda tasan dole dai ya canza wasu, sosai ta rikesa da salonta har sukaja lokaci kafin suka sami nutsuwa, shiya fara mikewa ya shuga bathroom bayansa tabi bayan ta kalli agogo tasan yana shiryawa ba'abinda zai hanasa tafiyar nan itaa kuma taci alwashin a yaudai bazaije kanon ba, a cikima bata kyalesa ba shima ya biye mata karar wayansa daya jiyo daga ɗaki yasa yai saurin yin wanka ya futo, itama wanka tayi tabiyo bayansa tana gunguni, kallonta yayi ya ce "Mai kike cewa?" "Nifa bai isheni ba kai kuma naga sai wani sauri kake?" "Hmm sodai kike ki hanani futa yau ki haɗani da kanwarki tayi fushi na shuga uku" Daure fuska tayi kamar bata taɓa dariya ba ta zauna gefan gado taja tagumi tana kallo yana sake wani shirin wanda yafi nada amsar sa. Ina zaune cikin shagonmu ina kallon yanda Mami kewa wata amarya kwalliya tai matukar kyau hotuna nake mata a wayar Mami danni har yau banda waya gobe dai nake saran zanje na siya nabawa Mami wayanta data dawo kamar tawa kiran Fu'ad ya shugo ina kallo ya katse ban ɗaga ba harsaida yasake kira nan ma saida ta kusa tsinkewa na ɗauka sallama yai na amsa masa ina wani cin magani "Amarya fatan kina gida gani na shugo kano nida Abokina Uthman" "Ok saikun karaso bana gida amma yanzu zan koma" Mami na gayawa Fu'ad ne zaizo na tafi gida, rasama mai zan masu nayi tunawa nayi yana matukar son gurasa na taɓa jin hakan a wajan Uncle hakan yasa na shirya masa gurasa wacce tajiku tai laushi tasha kayan haɗi irinsu cocumber kabeji tumatir green peper harda carrot dana gogasa sai lemun aya danai masa nasa a freezer, jin ana kiran sallar la'asar yasa na futo daga kicin ɗin na shuga ɗakina wanka nayi nai sallah kana na zauna gaban madubi na soma tsara kwalliya karo na farko kenan da zanyi kwalliya tun bayan rasuwar Uncle "Allah sarki Mijina I miss you wallahi" na faɗa a fili hawaye na kwaranyowa daga cikin idaniyata, gogewa nayi naci gaba da kwalliyata na kammala na ɗakko doguwar rigar Shadda na saka ina kokarin ɗaura ɗan kwali Ameera ta shugo "Wow Anty na ina zaki haka irin wannan kyau haka Allah bakiga yanda kikai kyau ba" sai kuma tayi shuru jikinta yai wani irin sanyi ta zauna gefan gado taja tagumi tana kallona "Anty kwalliyar nan taki saita tunamin da Abbana Allah sarki ubangiji yajikanka Abba" sai kawai ta kwanta saman gado tana kuka "Anty shikenan ni marainiya ce banida uba uwa tana can gidan yari, Anty dan Allah ki kaini gidan naga Ummana kafin a zartar mata da hukuncinta" zama nayi kusada Amira zuciyata babu daɗi jinake kamar na tayata kukan "Kiyi shuru Meera insha Allah gobe zamuje kiga Zainaba daina kukan dan Allah nima karki sakani kuka, ko yaushe ina gaya maki kirinka min kallon uwa mahaifiya ga Yaya Jabeer nan shizai zame maki tamkar Uncle dan Allah kidaina kuka inmun tuna Uncle addu'a zamuyi masa ba kuka kinsan haka Mami ke gaya mana ako yaushe" "Nayi shuru Anty"tafaɗi haka tana mikewa tsaye tareda share hawayanta ta shuga bathroom 07039793439 🌹 *KUKAN ZUCIYA* 🌹 Story and Writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Assosciasion* ☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation MARUBUCIYAR HALIN RAYUWA SOYAYYA DA ZUMUNTA SANYIN IDANIYYA AIMANAH YANAYIN RAYUWA AND NOW KUKAN ZUCIYA 31&32 Wanko idanunta Amira tayi ta fito, ni kuma na mike na daga labule ina kallon compaund dai dai sanda naga shigowar motar Fu'ad gidanmu, murmushi nayi tareda gyara fuskata nacewa Ameera ga Uncle dinta can yazo taje ta shigo da shi sitting room, jiki a sanyaye ta fita ina nan zaune har zuwa sanda tadawo tacemin Fu'ad ya ce naje "Kije kicewa Hanne takaiwa baki abincin dana hada sitting room ta hada da lemu da ruwa suna cikin freezer" batacemin komai ba ta fice bayan yan mintina nabi bayanta dai dai zan shiga Hanne ta fito hannunta rikeda kudi yan dubu dubu sai murmushi take tana dariya tacemin "Kinga yallabai Fu'ad ne yabani" Dariya nayi tareda cewa "an gode" nashiga da sallama yanda Fu'ad yakafeni da idanuwa har abin yaban kunya zama nayi kasan carfet ina gaida abokinsa Usman dasuka zo tare, fuskarsa sake yake amsamin gaisuwar banko kalli inda Fu'ad yake ba kaina a kasa bansan sanda yabaro inda yake zaune ba yadawo gafda ni ya zauna saida naji maganarsa tamkar maiyin rada a cikin kunne na sannan na dago muka hada ido, kashemin ido yayi salon dayayi yasani dariya tareda saurin rufe idanuna da hannuwana ina dariya "Kinyi kyau sarauniyata, ina godewa Allah dayasa inada rabon auranki ashe inada sauran farin ciki a rayuwata, dan Allah budemin fuskarki nayita kallah inajin dadi" kaina nai saurin sawa cikin kafafuna ina dariya sosai dan bakaramin dariya Fu'ad yaban ba daman can shi mutum ne mai barkwanci bare yanda yake magana da wata murya mai dadi da fisgar hankalin mai sauraro "Uhmm bazaki dago na kallekin ba?" ko rowar fuskar akemin?" tona kuwa gode bari na koma inda na fito" yafada yana mikewa tsaye, da sauri na dago ina kallonsa da murmushi a fuskata, komawa yayi ya zauna, shaf yama manta ba su kadai bane a dakin saida ya zauna sannan ya ga Uthman dake ta zafga loma, hararar sa Fu'ad yayi yana fadin "Malam maine haka kuma ya za'a kawo abu danni kai kuma ka zage kana cinyemin" "Ai naga ba shine a gabanka ba love kake yi niko bazan iya barin wannan delicious din ya wuce ni ba,kasan wannan best food ɗina ne bana filakonta ko a gidan sirikai nai, ni zanso ma a gaggauta ayi bikin nan kullum ina gidanka amarya tana hadamin wannan hadin dan tunda nakecin gurasa a rayuwata bantaba cin mai daɗi kamar haka ba"Usman yana gama fadar haka ya dauki flask ya fita dashi yana fadin "Bari a kaiwa su sarkin mota suma su fara taba abincin amarya kafin tazo"dariya Fu ad yayi tareda jin jina kai Zama ya gyara tareda cewa "Amarya wanne event kike shirya mana lokaci yana tahowa fa" "Bazanyi komai ba walima kawai zanyi shima a cikin gidan nan ba'a wani waja ba"sun jima suna tattauna yanda bikin nasu zai kasance sai gafda mangariba sanna suka tafi. Cikin satin shirye shiryan biki Mami ketayi ta gefe guda kuma ta zage tanamin gyaran jiki na musamman irin nasu na yan maiduguri cikin kwana uku kamshi yakama jikina ko giftawa nayi a waje sai anji kamshe barema ace na zauna a waje, saida biki yarage saura sati guda sannan Mami ta fara ɗirkamin magani wanda acewarta na sanyi ne Anty Fatima gaba daya tadawo gida saboda shirye shirye daman gidanta ita kaɗaice Yaya Mukhtar yana legos wani aiki, itama sosai ta tisoni a gaba da nata magungunan wani bin inna sha kaina har ciwo yake amma kona faɗa basa tsayawa fasawa Mami kam na gefe sai dai tayita mana dariya in taga yanda ake dirama dani wajan shan maganin Ayau gidansu Fu'ad suka kawo kayan lefe gidanmu Anty Jamila sai harare harare take tana sakin magana ba wanda ya kulata sai Mami dan tunda suka shigo gidan take wani cika tana batsewa tareda harare harare kaya suka jibgo sosai kamar ba gobe Momy matar wan Ummi itace ta soma yaba kayan tana faɗin "Kai kaya sunyi masha Allah Ubangiji yabada zaman lafiya" Anty Jamila dake wani shu'umin mirmishi ta ce "Kaya kam gasu nan sunyi kyau kamar bana bazawara ba"wani banzan kallo mami tayi mata tana faɗin "Aifa kam da babbar budurwa ai kwara karamar bazawara da Minal har nawa take banda ma kaddarar mutuwa da mai zai hada Minal da zawarci ga...."Hajiya dan Allah ayi hakuri mu rufe taro da salatin annabi" Umman mai martaba ta fadi haka dan tsaida maganar, saida suka tafi a mota Umma taiwa Anty Jamila tas takuma ce ko a biki bata bukatar ganinta a gidanta tunda ita ba'a zaman lafiya da ita, bakaramin shaka Anty jamila tayi ba ganin yanda Umma ke yarfa ta a gaban matan waziri, hakan yasa ranta yaɓaci ta sake cin alwashin ganin bayan auran nan na Fu'ad. Bangaran Fu'ad shiri yake sosai makeken gida mai kyau da tsari part biyu mai martaba ne ya mallaka masa gidan bakaramin dadi yaji ba Baraka ya dauka sukaje gidan ta gani yace tazaɓi sashin dayai mata iri dayane sai dai ɗaya yafi ɗaya girma hakan yasa taɗau babban acewarta saboda baki tunda itace uwar gida ko yan uwansa na Sudan ne sukazo a wajanta zasuna sauka, Mami da Momy da Anty Fatima suka zo sukaga sashin Minal ɗin sun yaba sosai, saura kwana huɗu biki Baraka ta tare a gidan dayai mata mugun kyau manyan kudi Fu'ad yakashewa sashin dan kawai ya farantawa Baraka dayake matukar ganin girmanta dan sanda yagaya mata zai kara aure yayi zaton zata tada hanakalinta tayi masa hauka irin wanda wasu matan keyi in mazansu zasu kara aure amma Allah sanya alkahiri kaɗai tace masa, yaso yayiwa Su'ad komai kamar yanda yayiwa Baraka amma Mami tace sun gode basai yayi komaiba ko cokalinsa basa bukata zasu saka komai. Saura kwana uku ɗaurin aure Mami dasu Mommy sukaje bare suka shiryawa su'ad ɓangaranta komai yayi dai dai inji Anty Fateema ba karamin kudi suka kashe ba kowa so yake ya faranta mata kasancewarta karama a cikinsu. Ranar alhamis akayi walima gida ya cika sosai dangi ta ko'ina sunxo yan karaye ma tun jiya da yamma suka zo kowa sai farin ciki yake da nishaɗi, Mami da kanta tai deccoresion ɗin wajan da zamuyi walima wanda yai matukar kyau mai ban sha'awa kowa ya kalla sai ya yaba, karfe biyar saura Amarya tafuto sanye cikin shiga ta mutumci less ne marun ajikinta sai plate shoe ta sanya dogon hijab ɗinta har kasa, fuskarta bawata make'up hoda kurum ta shafa sai kwalli da man leɓe sai fuskar tata tai kyau sosai ta zauna a inda aka tanada dan ita, malama Rabi'atu Yusuf ta gabatar da lacca ɗinta mai taken gidan Aurena, sai gaf da mangariba aka tashi bayan an kama amarya aka raba manyan bag wanda aka saka turaran wuta da humra da lallenmu na gargajiya,akaci akasha aka rufe taro da addu'a da kuma fatan zaman lafiya ga amarya da ango. .......Hajiya Jameela tunda suka koma gida take cika tana batsewa saboda abinda Umma tai mata ba kramin kona mata rai yayi ba, Abbie baya gari yana Abuja gaba ɗaya watan nan bai zauna a bare ba yana can ayyuka sun masa yawa har ana ya gobe ɗaurin auren Fu'ad baizo bare ba. Da sallama ya shugo falon saida yaiwa kansa mazauni a ɗaya daga cikin manyan kujerun dasuka kawata falon sannan ya ɗago ya kalli wacce ke zaune a falon kana yace "Anty Jameelah ina wuni" wani kallon banza ta wurga masa tareda girgiza kai ta lura tunda Fu'ad yadawo kasar nan ya raina ta banda ya rainata har ita zai kalli idanunta ya rinka kiranta da Anty Jameela koda yake ba laifinsa bane laifin Baraka ne saboda ita ke kiranta haka tasan a bakinta yaji, Fu'ad na murmishi ya ce "Nace ba dan Allah idan Abbie na ciki ki sanar mas nazo" Wani dogon tsaki Anty Jameelah taja kana ta ce "Lalle Aminu wuyanka ya isa yanka ina matsayin matar babanka kake kiran sunana gatsal haka, saboda baka da kunya ni zan maka magana da mahaifin naka?"to nima ban gansa ba." tana gama faɗar haka ta wucerta ɗaki, Mirmushi yayi tareda danna wayarsa ya karata da kun nan sa yayi sallama bayan sun gaisa da mahaifin nasa yake tambayarsa "Abie har yanzu baka zoba gashi gobe ɗaurin aure fa" Abie na dariya ya ce "Dole sai nazo nayi zaton tunda ga maimartaba ni basai nazo ba tunda ko nazo ɗan gayya nima zanzama" "Abba kazo, aurena fa yanzu saika ki zuwa bikina?" "Ameen baka da kunya ni kake gayawa bikinka" Fu'ad yana dariya ya ce "Abba kaifa abokina ne da mai Martaba ne shine bazan iya faɗa masa haka ba" "Shikenan zanzo goben mu haɗu a kano can naga za'a ɗaura auran nima zaman nan ya isheni ga tarin ayyuka ga Jameela taki zaman Abuja narasa zaman me take anan?" Fu'ad a ransa yace zaman samin ido mana amma a fili saiya waske da cewa "Abie aure kawai zaka kara anan kai zamanka da amaryarka anan ita kuma taci gaba da zaman nan ɗin" "Ba ruwana idan taji wannan maganar taka zaku kwashi yan kallo" Abie ya katse wayar yana dariya. BARAKA Duk yanda takeso ta jure takasa yau tunda gari ya waye takejin xuciyarta ba daɗi daurewa kawai take ganin gidan nata yasoma tara baki, zuciyarta ce ta wani irin bugawa ganin fitowar Fu'ad cikin shiga ta alfarma, yana sanye cikin dakakkiyar shadda mai sheki da walwali kallo ɗaya zakayiwa shaddar kasan bata kananun kudi bace saboda yanda take maiko da ɗaukar idanu ga wani kamshi datake fiddawa na musamman, hula takalmi agogo duk kansu jajaye ne, bakaramin kyau yayi ba kai bazaka ce yanada aure ba har yana da y'a, yanda yake washe hakora yana dariya shi kaɗai ma ya isa ya bayyanar maka da tsantsar farin cikin dayake ciki, gaisawa yake da yan uwan Baraka harya karasa bedroom ɗinta inda take zaune ta zabga uban tagumi saida ya zauna kusa da ita yana mirmishi ya ce "Yadai wife naganki wani iri?" bakaramin jarumta tayi ba waja maida hawayan dake kokari xubo mata tace "Banjin daɗi kaina na ciwo kaɗan kaɗan" "Oh sorry wife kisha magani ki kwanta ki huta and karki sawa kanki damuwa please" batare daya sake duban inda take ba yamike ya fice daga room ɗin,yana fita ta kife a kan gadon ta fashe da kuka mai tsima zuciya...✍🏻 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels